← Book details Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 241 OF 269

Sashe 241

Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ji tayi laifukan sa na gogewa suna shafewa , ƙaunar sa , son sa , tare da tarin tausayin sa masu nawin da bata taɓa jin makamancin su ba saboda ji da tayi kamar zuciyar ta ba zata iya ɗauka ba , kamar sararin dake ran ta yayi kaɗan.

da wani irin tasiri mai girma suke maye gurbin duk wani ɗan taƙi da ta bar wa soyayya mallaki a cikin ran ta .

Tasirin so da take ji a lokacin ya fi ƙarfin rarraunar zuciyar ta da take sabon shiga a fagen soyayya .

Ɗago da kan sa yayi yana kallon ta bayan ya gama tofa mata addu'o'i a ƙafar ta .

Ya ɗan dau lokaci yana kallon ƙaramar fuskar ta da take sake zama 'yar firat yana jin tausayi tare da wannan son nata mai yawa yana masa yawo a zuci .

Jin sa shiru ya sa ta buÉ—e idanun ta a hankali suka haÉ—a ido .

"Sannu Fatima insha Allah za ki samu sauƙi kin ji kou ?

GyaÉ—a kan ta tayi

A hankali ya miƙe ya ƙarasa ya ɗauki bowl ɗin da Siyama ta ajiye ya dawo ya zauna , ya fara bata ferfesun tana ci a hankali , har sai da ta ɗan ci dayawa kafin tace masa "ta ƙoshi .

Bayan ya ajiye kwanon ya dawo ya zauna tare da riƙo hannun ta ya sarƙe 'yan yatsun su waje ɗaya "Fatima kiyi haƙuri da abunda ya same ki Allah zai miki sakayya cikin gaugawa kuma insha Allah zan zamar miki garkuwar da babu wanda shi issa ya taɓa ki a rayuwa na ƙyale shi , kiyi haƙuri Fatima .

Matsa hannun sa da yake cikin nata tayi kafin ta É—ago kan ta tana saka idanun ta cikin nashi tace " Meyasa bata son ka haka ?

"Nima ban sani ba Fatima cikin rayuwata ban taɓa yi mata laifi ba amma ta zuba min ƙiyayya mai zafi da har da taimakon ta anka nemi raba ni da raina bayan ita ta gurgunta rayuwata ta rarraba ƙiyayyar da take min tsakanina da ɗiyan ta da suke 'yan ouwana .

Kan ta ta mayar ta kwantar a ƙafaɗar sa tana kaucewa kallon cikin idanun sa da suka fara sauya launi tace

"Kayi haƙuri ƙiyayyar ta ba za ta sa ko ta hana kome ba sai fa abunda Allah ya rataya alhakin faruwar sa akan ta .

"Idan ita bata son ka Allah da Manzon Allah su na son ka , Maimartaba yana son ka , Umma tana son ka sauran 'yan uwanka suna son ka , Siyama tana son ka , yaran ka ma zasu so ka .

ÆŠan jim tayi kafin ta É—ago kan ta tana kallon cikin idanun sa tace " kuma ni ma ina son ka , Ina son ka , ina son ka dayawa .

A bazata ya tsinkayi kalmomin da bata taɓa furta masa ba , zuciyar sa tayi wani ɗan ƙaramin zillo da yasa shi sake ɗago fuskar ta da sauri ya riƙe ta yana kallon ƙwarar idanun ta , muryar sa a tsakani maƙoshin sa yace "me kika faɗi Fatima sake faɗi naji ? Maimaita min ?

"Ina son ka dayawa dayawa ba adadi
Ta sake furta hakan tana kallon fuskar sa cikin ranta " godiya take yiwa Ubangiji da idan ba shi ba da ƙarfin ikon sa wa ya isa mallaka mata wannan mutumin ma'abocin kyau da cikar zati tare da kyaun nasaba ?

Muryar sa tana sake nitsewa saboda ƙasa da yayi da ita yace "dagaske Fatima ?

Hannuwan ta tasa akan nasa kafin tace "da duk gaskiyar zuciyata ina son ka dayawa ,

Wani irin sanyi yake ji tun daga ƙasan ran sa yana taso masa yana nitsar da idanun sa cikin nata yace " son da nake miki yafi wanda kike min yawa Fatima , son da nake miki ba shi da iyaka , ni ban san iyakar sa ba, kin yarda na gwada miki ɗigo dagga cikin sa ?

Kan ta ta gyaɗa masa tana murmushin da yake bayyana haƙoranta ,

Tazarar dake tsakanin su ya haɗe yana manne fuskar sa da ta ta , tare da shauƙin son da suke yiwa junan su suka himmantu wajen gwadawa junan su tatatciyar soyayyar da suke yiwa juna .

Ƙwanƙwasa ƙofar da Aka yi yasa su sa rabuwa da jikin juna ,

Ba'a jinkirta ba aka murɗo ƙofar a hankali ta shigo bakin ta ɗauke da Sallama .

Siyama ce ta shaida musu zuwan mai gyaran ƙafa .

Yousaouf ya masa iznin shigowa bayan ya gyara mata mayafi.

Ba ƙaramar azaba Falmata ta sha ba kafin ƙashin da ya fita ya koma saboda tsamin da ƙafar tayi kwana huɗu da targaɗe .

Siyama da Youssouf su suka dunga rige-rigen share mata hawaye da gumin da ta haÉ—a sharkaf duk kuwa da sanyin É—akin .

Bayan ta dawo cikin nutsuwar ta lokacin Youssouf ya bar ɗakin daga ita sai Hajja da ƙaramar murya ta cewa Hajja " Hajja ki bani wayar ki zan ƙira Mamana da Yakaka .

ÆŠan jim Hajja tayi kafin da sigar rarrashi tace "UwarÉ—akina Amma fa kar ki shaida musu abunda ya faru da ke domin ba'a sanar da su ba tun da Allah yasa kin fita lafiya kar ki faÉ—a musu kuma zuciyar su ta kasa nutsuwa da zaman ki anan .

"Ba zan faÉ—a musu ba Hajja kawai so nake naji muryar su mu gaisa .

"To babu laifi ga wayar ki ƙira su .

Sun jima suna Hira da ita da iyayen ta Khaalty Rahima da Amnee inda har suka yi ƙorafin cikin kwana biyun sun yi ta ƙiran layin Hajja bata ɗauka musamman ma a jiya da Yakaka ta koma Abuja .

Cikin É—oki Falmata take sake tambayar su 'Yakaka ta tafi gidan ta ?

Amnee ta bata amsa tana dariya da cewa "jiya suka tafi tare da yayan naku takwarata an zama 'yan Abuja ( kamar Ammi Haseen 🤣)

Cikin zaƙuwa Falmata ta fara ƙiran layin Yakaka bayan sun yi Sallama da su Amnee.

Sai dai ƙira biyu tayi ba'a ɗauka ba , yamutsa fuska tayi tana sake danna ƙiran take mitar " Yakaka ko ina ta ajiye wayar ???

ABUJA NIGERIA

Kai-kawo Yakaka ta cigaba da yi a cikin banɗakin da take tsaye , karo na barkatai ta sake sunkuyawa tana leƙe ta ƙafar ɗan makulli , da sauri tayi baya tana sakin wani ƙaramin ihu ƙiris ya rage ta faɗi saboda santsi jikin ta na karkawa ta dafe ƙirjin ta tana mayar da numfashi .

Idanun ta ba ƙarya suka mata ba tirƙeƙen karen da take hangowa tun safe a can nesa daga tsakiyar ɗakin wani lokaci kuma ta hango shi a gefe shine ta gan shi daf da ƙofar a yanzu kamar ma shima leƙen ta yake ta inda take leƙawa dan babu shakka sun yi ido huɗu ita da shi..

Zamewa tayi ta zauna a ƙasa dirshan cikin banɗakin daga inda take tana iya jin wayar ta dake ƙara lokaci zuwa lokaci tsawon yinin amma ba damar fitowa ta ɗau wayar saboda tirƙeƙen karen da yake ta shawagin sa a ɗakin har gado yake hawa yana sauƙa .

A hankali ta saki wani sabon kukan da aƙalla tayi irin sa fiye da sau goma daga safe zuwa yanzu da ta tabbatar yamma tayi rana kuma tana gaf da faɗuwa .

Assalamu Alaikum masu karatu da fatan kuna lafiya ?

Yau dai bakina da goro ba zan ce kome ba bayan fatan alheri da nake muku a koyaushe.

Nagode.[3/7, 3:55 PM] +234 706 503 6187: Mafari
( Hargitsin Rayuwa )

Umm'muaz

52

Ƙarar Turo ƙofar daƙin da Yakaka ta ji yasa ta tashi da sauri daga inda ta rakuɓe tana kuka ta zo jikin ƙofar ta ƙafar ɗan makulli ta leƙa .

Sofi ta hango ta shigo, duk da halin firgicin da take ciki bai sa ta kasa ganin irin kwalliya ta É—aukar magana tare da jaan hankalin duk wani É—a namijin da ya É—ora idanun sa akan ta ba da Sofia tayi .

Wani ɗan fito Sofi ta yiwa ɗirkeken karen nan ( Working dog ) sai ga shi ya dako tsalle daga kan gadon da Yakaka bata san yaushe ya haye ba , ya taho jikin ƙafafun Sofi yana kaɗa jela tare da sunsuna ta .

Ƙaramar dariya Sofi tayi kafin ta ɗan yi sunkuyo ta shafa kan karen da farin ciki a sautin ta tace " oh Sam do you know how handsome you are ? You've got the best underbite, and the best butt muscles , Oh Sam I Love you , you really did a good job baby.

Lokacin da ta ɗago kan ta wata ƙatuwar harara ta wurga a saitin ƙofar banɗakin kafin ta jaa wani dogon tsaki tana juyawa akan ƙafafun ta Sam ya bi bayan ta da ɗan gudun sa suka ƙarasa ficewa a ɗakin.

Wata doguwar ajiyar zuciya Yakaka ta jaa tana dafe ƙirjin ta kafin ta ƙarasa zama a ƙasa tana jin wata 'Yar nutsuwa na safko mata, "Anty sofi Muguwa ce , ta aiyana hakan a cikin ran ta lokacin da ta tuno yadda tsakanin su yakasance a ɗazu da safe bayan fitar Doctor Hamza da yayi sammako ƙarfe shida na safe ya bar gida .

Bayan fitar sa ta tashi tana son tattara ɗakin kafin ta fita gaishe da Sofi ta dawo ta hau gado ramuwar baccin gajiyar hanya da suka sha saboda a jiya basu iso gidan ba sai wajen ƙarfe sha biyu na dare dan haka ko da Matar gidan basu gaisa ba .

Ƙarar turo ƙofar da aka yi yasa ta ɗago kan ta Sofi ta gani jikin ta da rigar baccin da take bayyana rashin kamun kan ta a sarari kan ta ko ɗan kwali babu , da sauri ta sunkuyar da kai tana janye ganin ta .

Ta buɗe baki da nufin gaishe ta kalmomin ta suka ƙaƙare lokaci ɗaya numfashin ta ya shiga kai kawo yana ƙoƙarin fisgewa daga jikin ta lokacin da tayi ido huɗu da wani ƙaton mummmunan baƙin kare da ya taho yayi tsaye a bayan Sofi kamar ɗan matashin zaki .
Chapter 241 · 0% Book details