Sashe 12
Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Fashewa da kuka tayi cikin shishiƙar kuka ta fara cewa yakaka sai da na faɗa miki kar mu taho kar mu taho kika ce sam sai mun taho ," kika nace ," gashi nan yanzu zamu mutu a cikin daji kura ta samu na kalaci ," ta karashe zance tana jaan majina .
Shiru yakaka da yagana suka yi domin a hakiƙanin gaskiya su dukkanin su biyun karfin hali kawai suke domin kuwa ƙarƙashin rayukan su cike yake taf da tsoron duhun daren da ya riga ya fara shigowa ne,"alhalin suna cikin ƙungurmin dajin da basu san gabas ba bare yamma ,"
Kiyi hakuri Falmata ni bana son yawan kukan nan da kike kin san dai baki da lafiyar idanu ," muyi ta addu'a kawai Allah yana tare da mu ," cewar yakaka
Eh Falmata addu'a ita ce mafita kuma ina jin kamar ma mun kusa isa maidugurin dan ina tunanin lokacin da aka kaini asibitin kamar ance wai bamu kwana a hanya ba wai awanni bi......
Ke ni dallah ki mana shiru ,"ke idan ana zancen waɗan da suka taɓa zuwa birnin maiduguri ma har kya sako baki ?
Wucewa gaba Falmata tayi a fusace tana lalube a ranta kuwa tana ayyanawa kome ta fanjama .
[6/24, 9:58 AM] +234 701 013 7848: Fikrah writers association
*MAFARI.......*
( _HARGITSIN RAYUWA_ )
*umm'muaz*
4
Ƙanƙame da juna suke kwance a ƙarƙashin duhuwar bishiyar kukar da duhun ta ya haɗu da duhun dare tare da na damina ya bada matsanancin duhun da ba'a ko iya ganin tafin hannu .
Falmata ce a tsakiyar su yakaka da yagana suna gefe-da-gefen ta ,ko ƙokkwaran motsi basa iya yi saboda tsabar zullumi da tsoron da ya cika musu rai ! Numfashi ma a sace suke yin sa yayin da kunnuwan su suke tarwai a buɗe daga jin motsin abun da yake nesa da su da kusan rabin kilomita .
Babu motsin kome a dajin da ya wuce kukan jemagu da kuma wasu ƙananun ƙwarin da ba'a iya tantance kukan su ," haɗi da wani kuka da suke ji daga nesa ƙadan da su wanda tsananin tsoron da suke ji ya sa suka kasa tantance kukan koh na menene ,"ya dai fi musa kama da kukan bijiman sa (shanu) sai kuma jifa-jifa kukan manyan namun dawa waɗanda suke nesa sosai daga wurin da suke .
Ƙasa-ƙasa muryoyin su suka fara tashi ,"
Umm Yakaka zan yi fitsari ,"
Fitsari kuma falmata dan Allah kiyi hakuri mu jira safe.
Falmata kawai kiyi fitsarin nan anan kwance a jikin mu ," cewar yagana
Motsin da suka fara ji mai ɗan karfi yana doso inda suke ne ya sanya su sake damuƙar junan su kafin jikin su ya ɗau karkarwa kar-kar-kar .
Shikenan muryoyin su sun jawo mu su .
Wani ɗumi yakaka da yagana suka ji a jikin su wanda yake tabbatar musu yawaitar motsin da suke ji tare da ƙarin gabato su da motsin ke yi shi ya sanya falmata sakin fitsarin da tace tana ji saboda tsabar tsoro
Haske suka fara hangowa wanda basa raba ɗaya biyu hasken tocila ne ," kafin su fara jin taƙun kafafun mutum ," tare da tashin muryoyin mutanen da baza su wuce biyu ba sai dai magana suke a cikin yaren da su yakaka basa fahimtar sa ,"
Gani suka yi an ɗan kau da hasken tocilan kafin su ji an taho har kurkusa da su ," karar zubar wani abu kamar ruwa ne ya fara sauka kunnuwan su kafin su ji ruwan mai ɗumi ya fara fallatsuwa akan fiskokin su a zaɓure suka miƙe zaune wanda a tunanin su koh ruwan zafi ake watsa musu ,"
Miƙewar da suka yi shi ya mutumin da yake tsaye shima ya zabura tare da yin eho a take kuma ya buɗe murya gami da yin magana da maɗaukakiyar murya cikin yaren sa nan take sai ga hasken tocila ya dallare fuskokin su yakaka ,"
*****
A tsugunne suke bisa gwaiwowin su tamkar mai laifi a gaban hukuma ," maza ne kimanin goma a zagaye da su dukkanin su hannun su rike da makamai kama tun daga kan ,sanduna , gatari ,takobi,kwari da baka , wuƙake , da ma bindigar harbi ka buya ,
Fahimta da suka yi su yakaka basa jin yaren su na hullanci ya sanya É—aya daga cikin su ya juya harce cikin yaren hausa
Yaro ku su waye ? Kuma daga ina kuke cikin daren nan ?
Nan take yagana wacce da alamu ta fi su yakaka fahimtar hausa ta ce mu Æ´an gudun hijira ne daga garin Bama nake waÉ—anan kuma "tana nuna su yakaka " abokan tafiya ta ne daga nan kauyen mairambiri suke ," Æ´an tawayen boko haram ne suka tarwatsa mana garuruwan mu ,"
Duk bayanin nan da suke yi yakaka da yagana basu samu damar ganin fuskokin su waye a tsaye zagaye da su ba su dai sun san mutane ne , kuma a ƙalla sun ji saukin tashin hankalin da suke ciki akan sanin da suka yi ashe akwai mutane dayawa haka kurkusa da su ,".
Juya harshe wannan mutumin da ya tambayi su yakaka yayi ,"tare da yi wa abokan tafiyar sa fassarar bayanin da yagana tayi cikin yaren su na hullanci ," nan take hayaniyar su ta ƙaure a wurin da alama Tausayawa yaran suke tare da Allah wadai da ƴan tawayen boko haram wanda sun riga sun san da zaman su ," kuma tsakanin su da su babu kare bin damo "abun nufi ko da sun haɗu cikin daji basa shiga harkar juna ," ( Makiyaya da ƴan tawayen boko haram )
Bayan doguwar muhawarar da suka yi a tsakanin su nan mutumin ya juya ga su yakaka yace ":
Yaro yanzu ku ina kuka nufa ?
Maiduguri zamu ," ance gwamnati ta tanada mana wurin zama ', za'a kula da mu cin mu da shan mu sutura da wurin kwana har ma ance za'a samu a makarantun gwamnati ," abincin cin mu ma na....
Katse ta mutumin yayi :
Yaro kun san hanyar Maidugurin ne ?
Nan falmata wacce take fahimtar mafi yawan kalmomin nasu ," mayar da magana cikin hausar ne ke yi mata wahala ,
Tayi tsagal tace Baba wallahi bamu san hanya ba", dan Allah ku taimaka ku kai mu Maiduguri dan Allah ta karashe zancen tana matsar ƙwallar wahalar da ta ciko mata ido,"
Yaro zamu taimaka muku amma mu ba Maiduguri muka nufa ba ," mu daga nan ikko muka nufa ,"amma zamu raka ku har inda muke ganin kun wuce hatsari sai mu gwada muku sauran hanyar ," nan wurin da kuke akwai hatsari sosai ,
Juyawa ya sake yi suka yi magana da Æ´an uwan sa ," sannan ya juyo tare da cewa ku biyo mu ,"
Lumshe matsakaitan idanun ta tayi lokacin da ɗumin madarar saniyar sabuwar tatsa ya sauka a cikin ta ," dago kan ta tayi daga cikin ƙoƙon da yake cike taf da madarar ta maida kallon ta ga fuskar kanwar ta wacce tayi kasaƙe hannun ta rike da nata ƙoƙon da bata tunanin ma ta kai bakin ta ," idanun ta suna sheƙin ruwan da ya taru a cikin su a tsaye idanun na ta suke ƙem wuri guda ," da alamar tayi zurfi cikin tunani ," a hankali taga ƙwallar da ta taru a gurbin idanun nata sun silalo da gudu sun sauko bisa ƙuncin ta ," da sauri ta ajiye ƙoƙon madarar ta gami da ƙarasawa inda falmata take zaune akan wani ɗan dutse ," dire gwaiwowin ta tayi a ƙasa lokaci ɗaya kuma ta sanya hannu gami da goge mata ƙwallar da suke cigaba da fitowa
Yakaka yau kwanaki biyu kenan muna wayar gari ba tare da iyayen mu da sauran Æ´an uwan mu ba ," Allah ya jikan Baba ya gafarta masa ,"insha Allah shi mutuwa hutu ce a gareshi ,"
To amma yakaka mama fa da sauran kannen mu a wane hali suke ciki ? Wataƙila suma ƴan tawayen boko haram sun kashe su irin yadda suka yi wa Baba ," idan kuwa har suna raye tabbas mama tana cikin mawuyacin halin da ya fi wanda muke ciki a yanzu ,"
Yakaka muna shiga birnin Maiduguri abu na farko da zamu fara yi shine neman maman mu ,"
Ƙai hannunta tayi ta lalubo fuskar yakaka jin tayi shiru bata cewa kome duk bayanin da take yi , nan taji ruwan hawayen da suka faca-faca akan fuskar ta ," share mata hawayen tayi kafin a hankali ta kai kanta ta ɗora akan kafaɗun ƴar uwar ta , idan ke kika yi kuka a halin yanzu ni me kike so nayi yakaka ? ,kiyi haƙuri ki daina kuka insha Allah zamu haɗu da maman mu ,"
Nemo yatsun hannun falmatan tayi ta sarƙe su cikin nata hannun "falmata ba ina kuka bane a domin wahala koh raunin zuciya akan halin da muke ciki ba," ina kuka ne akan tunanin halin da mama da ƙannena suke ciki ina kuka akan wahalar rayuwar da kike ciki a halin yanzu alhalin bani da karfin taimakon ki ,"dubi kafar ki falmata ta ɗago kafar falmatan da take ɗaure da ɗankwalin ita yakaka,"
Duk ƙafar ta soke da kayoyi daga idon sawun ƙafar kuma a kumbure yake in da ta faɗa rami a jiya ," Falmata tun tasowar mu ban taɓa ganin ciwo irin wannan a jikin ki ba ,"duk da cewa muna rayuwa cikin talauci amma iyayen mu suna tattalin mu ,da lafiyar mu" amma ki duba daga shekaranjiya zuwa yau da rikon ki ya dawo kaina na gaza wurin baki kulawa gashi duk kin ji rauni ," sai nake ganin laifin kaina da zan iya falmata da goyon ki zan yi nasan da mama ce da ta sauke Bulama ta goye ki amm dubi ni ...
Shiru yakaka da yagana suka yi domin a hakiƙanin gaskiya su dukkanin su biyun karfin hali kawai suke domin kuwa ƙarƙashin rayukan su cike yake taf da tsoron duhun daren da ya riga ya fara shigowa ne,"alhalin suna cikin ƙungurmin dajin da basu san gabas ba bare yamma ,"
Kiyi hakuri Falmata ni bana son yawan kukan nan da kike kin san dai baki da lafiyar idanu ," muyi ta addu'a kawai Allah yana tare da mu ," cewar yakaka
Eh Falmata addu'a ita ce mafita kuma ina jin kamar ma mun kusa isa maidugurin dan ina tunanin lokacin da aka kaini asibitin kamar ance wai bamu kwana a hanya ba wai awanni bi......
Ke ni dallah ki mana shiru ,"ke idan ana zancen waɗan da suka taɓa zuwa birnin maiduguri ma har kya sako baki ?
Wucewa gaba Falmata tayi a fusace tana lalube a ranta kuwa tana ayyanawa kome ta fanjama .
[6/24, 9:58 AM] +234 701 013 7848: Fikrah writers association
*MAFARI.......*
( _HARGITSIN RAYUWA_ )
*umm'muaz*
4
Ƙanƙame da juna suke kwance a ƙarƙashin duhuwar bishiyar kukar da duhun ta ya haɗu da duhun dare tare da na damina ya bada matsanancin duhun da ba'a ko iya ganin tafin hannu .
Falmata ce a tsakiyar su yakaka da yagana suna gefe-da-gefen ta ,ko ƙokkwaran motsi basa iya yi saboda tsabar zullumi da tsoron da ya cika musu rai ! Numfashi ma a sace suke yin sa yayin da kunnuwan su suke tarwai a buɗe daga jin motsin abun da yake nesa da su da kusan rabin kilomita .
Babu motsin kome a dajin da ya wuce kukan jemagu da kuma wasu ƙananun ƙwarin da ba'a iya tantance kukan su ," haɗi da wani kuka da suke ji daga nesa ƙadan da su wanda tsananin tsoron da suke ji ya sa suka kasa tantance kukan koh na menene ,"ya dai fi musa kama da kukan bijiman sa (shanu) sai kuma jifa-jifa kukan manyan namun dawa waɗanda suke nesa sosai daga wurin da suke .
Ƙasa-ƙasa muryoyin su suka fara tashi ,"
Umm Yakaka zan yi fitsari ,"
Fitsari kuma falmata dan Allah kiyi hakuri mu jira safe.
Falmata kawai kiyi fitsarin nan anan kwance a jikin mu ," cewar yagana
Motsin da suka fara ji mai ɗan karfi yana doso inda suke ne ya sanya su sake damuƙar junan su kafin jikin su ya ɗau karkarwa kar-kar-kar .
Shikenan muryoyin su sun jawo mu su .
Wani ɗumi yakaka da yagana suka ji a jikin su wanda yake tabbatar musu yawaitar motsin da suke ji tare da ƙarin gabato su da motsin ke yi shi ya sanya falmata sakin fitsarin da tace tana ji saboda tsabar tsoro
Haske suka fara hangowa wanda basa raba ɗaya biyu hasken tocila ne ," kafin su fara jin taƙun kafafun mutum ," tare da tashin muryoyin mutanen da baza su wuce biyu ba sai dai magana suke a cikin yaren da su yakaka basa fahimtar sa ,"
Gani suka yi an ɗan kau da hasken tocilan kafin su ji an taho har kurkusa da su ," karar zubar wani abu kamar ruwa ne ya fara sauka kunnuwan su kafin su ji ruwan mai ɗumi ya fara fallatsuwa akan fiskokin su a zaɓure suka miƙe zaune wanda a tunanin su koh ruwan zafi ake watsa musu ,"
Miƙewar da suka yi shi ya mutumin da yake tsaye shima ya zabura tare da yin eho a take kuma ya buɗe murya gami da yin magana da maɗaukakiyar murya cikin yaren sa nan take sai ga hasken tocila ya dallare fuskokin su yakaka ,"
*****
A tsugunne suke bisa gwaiwowin su tamkar mai laifi a gaban hukuma ," maza ne kimanin goma a zagaye da su dukkanin su hannun su rike da makamai kama tun daga kan ,sanduna , gatari ,takobi,kwari da baka , wuƙake , da ma bindigar harbi ka buya ,
Fahimta da suka yi su yakaka basa jin yaren su na hullanci ya sanya É—aya daga cikin su ya juya harce cikin yaren hausa
Yaro ku su waye ? Kuma daga ina kuke cikin daren nan ?
Nan take yagana wacce da alamu ta fi su yakaka fahimtar hausa ta ce mu Æ´an gudun hijira ne daga garin Bama nake waÉ—anan kuma "tana nuna su yakaka " abokan tafiya ta ne daga nan kauyen mairambiri suke ," Æ´an tawayen boko haram ne suka tarwatsa mana garuruwan mu ,"
Duk bayanin nan da suke yi yakaka da yagana basu samu damar ganin fuskokin su waye a tsaye zagaye da su ba su dai sun san mutane ne , kuma a ƙalla sun ji saukin tashin hankalin da suke ciki akan sanin da suka yi ashe akwai mutane dayawa haka kurkusa da su ,".
Juya harshe wannan mutumin da ya tambayi su yakaka yayi ,"tare da yi wa abokan tafiyar sa fassarar bayanin da yagana tayi cikin yaren su na hullanci ," nan take hayaniyar su ta ƙaure a wurin da alama Tausayawa yaran suke tare da Allah wadai da ƴan tawayen boko haram wanda sun riga sun san da zaman su ," kuma tsakanin su da su babu kare bin damo "abun nufi ko da sun haɗu cikin daji basa shiga harkar juna ," ( Makiyaya da ƴan tawayen boko haram )
Bayan doguwar muhawarar da suka yi a tsakanin su nan mutumin ya juya ga su yakaka yace ":
Yaro yanzu ku ina kuka nufa ?
Maiduguri zamu ," ance gwamnati ta tanada mana wurin zama ', za'a kula da mu cin mu da shan mu sutura da wurin kwana har ma ance za'a samu a makarantun gwamnati ," abincin cin mu ma na....
Katse ta mutumin yayi :
Yaro kun san hanyar Maidugurin ne ?
Nan falmata wacce take fahimtar mafi yawan kalmomin nasu ," mayar da magana cikin hausar ne ke yi mata wahala ,
Tayi tsagal tace Baba wallahi bamu san hanya ba", dan Allah ku taimaka ku kai mu Maiduguri dan Allah ta karashe zancen tana matsar ƙwallar wahalar da ta ciko mata ido,"
Yaro zamu taimaka muku amma mu ba Maiduguri muka nufa ba ," mu daga nan ikko muka nufa ,"amma zamu raka ku har inda muke ganin kun wuce hatsari sai mu gwada muku sauran hanyar ," nan wurin da kuke akwai hatsari sosai ,
Juyawa ya sake yi suka yi magana da Æ´an uwan sa ," sannan ya juyo tare da cewa ku biyo mu ,"
Lumshe matsakaitan idanun ta tayi lokacin da ɗumin madarar saniyar sabuwar tatsa ya sauka a cikin ta ," dago kan ta tayi daga cikin ƙoƙon da yake cike taf da madarar ta maida kallon ta ga fuskar kanwar ta wacce tayi kasaƙe hannun ta rike da nata ƙoƙon da bata tunanin ma ta kai bakin ta ," idanun ta suna sheƙin ruwan da ya taru a cikin su a tsaye idanun na ta suke ƙem wuri guda ," da alamar tayi zurfi cikin tunani ," a hankali taga ƙwallar da ta taru a gurbin idanun nata sun silalo da gudu sun sauko bisa ƙuncin ta ," da sauri ta ajiye ƙoƙon madarar ta gami da ƙarasawa inda falmata take zaune akan wani ɗan dutse ," dire gwaiwowin ta tayi a ƙasa lokaci ɗaya kuma ta sanya hannu gami da goge mata ƙwallar da suke cigaba da fitowa
Yakaka yau kwanaki biyu kenan muna wayar gari ba tare da iyayen mu da sauran Æ´an uwan mu ba ," Allah ya jikan Baba ya gafarta masa ,"insha Allah shi mutuwa hutu ce a gareshi ,"
To amma yakaka mama fa da sauran kannen mu a wane hali suke ciki ? Wataƙila suma ƴan tawayen boko haram sun kashe su irin yadda suka yi wa Baba ," idan kuwa har suna raye tabbas mama tana cikin mawuyacin halin da ya fi wanda muke ciki a yanzu ,"
Yakaka muna shiga birnin Maiduguri abu na farko da zamu fara yi shine neman maman mu ,"
Ƙai hannunta tayi ta lalubo fuskar yakaka jin tayi shiru bata cewa kome duk bayanin da take yi , nan taji ruwan hawayen da suka faca-faca akan fuskar ta ," share mata hawayen tayi kafin a hankali ta kai kanta ta ɗora akan kafaɗun ƴar uwar ta , idan ke kika yi kuka a halin yanzu ni me kike so nayi yakaka ? ,kiyi haƙuri ki daina kuka insha Allah zamu haɗu da maman mu ,"
Nemo yatsun hannun falmatan tayi ta sarƙe su cikin nata hannun "falmata ba ina kuka bane a domin wahala koh raunin zuciya akan halin da muke ciki ba," ina kuka ne akan tunanin halin da mama da ƙannena suke ciki ina kuka akan wahalar rayuwar da kike ciki a halin yanzu alhalin bani da karfin taimakon ki ,"dubi kafar ki falmata ta ɗago kafar falmatan da take ɗaure da ɗankwalin ita yakaka,"
Duk ƙafar ta soke da kayoyi daga idon sawun ƙafar kuma a kumbure yake in da ta faɗa rami a jiya ," Falmata tun tasowar mu ban taɓa ganin ciwo irin wannan a jikin ki ba ,"duk da cewa muna rayuwa cikin talauci amma iyayen mu suna tattalin mu ,da lafiyar mu" amma ki duba daga shekaranjiya zuwa yau da rikon ki ya dawo kaina na gaza wurin baki kulawa gashi duk kin ji rauni ," sai nake ganin laifin kaina da zan iya falmata da goyon ki zan yi nasan da mama ce da ta sauke Bulama ta goye ki amm dubi ni ...