Sashe 129
Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ba shiri hajja me wurya ta zungure ta , tana satar kallon youssouf da yayi shiru yana sauraran ta ,
  Ƙasa-ƙasa tace
 Ka ji min sakarya auren da tun baki kai gidan ba kike fatan ki dawo , ??
Kawo ƙuɗin na riƙe mata Rahima, irin kunyar nan ce ta amare take gwada mana ,
 Â
Rahima da take murmushi a hankali ta miƙawa hajja me wurya kuɗin ,
Madallah Allah ya sanyawa auren ku Albarka Allah ya sa abokiyar arziki ce , Allah ya kauda shaiÉ—anun aljanu da na mutane a tsakanin ku , Allah ya sa mutuwa É—ai ita zata raba ku, Allah kuma ya baku zuri'a masu albarka irin wacce manzo Allah zai yi alfahari da ita !
  Laɓɓan Youssouf ne suka motsa a hankali da ,"Ameen .
  Rahima ita ta raka su har bakin mota tana jin yadda kewar su take taso mata , ai anyi sabo zaman watanni tare , duk da cewa ta so tafiyar su tafi haka tsawo sai dai damar bata samu ba , amma ko babu kome tayiwa fatima murnar samun ɗanɗasheshen mijin da ya ƙere sa'an auren ta ta ko'ina hakkun fatima me sa'a ce .
  Da wannan tunanin ta rufe musu ƙofar motar bangaren da falmata ta shiga inda suke zaune tare ita da hajja me wurya a bayan motar , Biyamuradi da direban sa suna gaba ," .
*****
Tafiya ce suka ɗora ta miƙaƙƙiya tun daga maiduguri zuwa sokoto , inda basu samu isa sokoto ba sai cikin dare misalin sha biyu da rabi , alamun gajiya da suka bayyana baro-baro ga falmata tare da baby mama wacce ta ke yin ƙananun rikici na gajiya da rikon hannun ya sa youssouf ya kama musu ƴan ɗakuna a wani ƙaramin guess inn da yake cikin garin na sokoto zuwa wayewar gari sun huta sun kuma sake shiri sai kuma su faɗa yankin niger ta," ilela ," su ɗau hanya ta birnin N'konni da zai ɗaura su kan kodoben da za su sadu da birnin Niamey ɗin niger ....!
Ba su suka samu isa Niamey ba sai ranar Asabat da misalin ƙarfe bakwai na dare duk kuwa da gudun da direban ya dunga shararawa tun da suka faɗa yankin niger kasancewar sun shigo ƙasar su , kowa yaga gilmawar motar su basu hanya ake ,
Kai tsaye direban ya wuce da su ( Radisson Blue hotel,) ƙarƙashin umarnin youssof , kasancewar shahararren hotel ɗin mafi yawan lokuta nan ne wajen sauƙar sa idan wani aiki ya kawo shi Niamey ɗin kasantuwar hotel ɗin kusa yake da manyan ma'aikatu masu muhimmanci na ƙasar da ke babban birnin Niamey ,
Babu ɓata lokaci ya kama musu ɗakuna inda hajja me wurya da falmata zasu zauna a ɗaki guda , (one bedroom Residence ) dake ƙasa shi kuma ya Kama nasa ɗakin a sama ( royal suite ) inda ya saba zama idan ya zo otel ɗin yayin da direba yayi tafiyar sa inda sauran abokanan aikin su suke , ya bar masa mukullin tare da motar , '
Bayan yayi wanka ya sallaci isha'i , misalin ƙarfe takwas da rabi ya sauko ƙasa , ɗakin da suke ya tasamma , ƙwanƙwas musu ƙofa yayi ,
Hajja me wurya tana sallar isha'i lokacin , falmata kuwa ta idar tana kwance bisa faffaÉ—an gadon ta sanya baby mama a gaba wacce take ta baccin gajiya bayan an cika mata ciki da madarar ta me É—umi ,
Sake ƙwanƙwasa ƙofar yayi a karo na biyu yana sake kallon number ɗakin da take rubuce a jikin wani ɗan katako dake sakale a jikin ƙofar ,"nan ne dai ɗakin nasu ,"
Miƙewa zaune tayi
  Hajja kamar ana buga ƙofa ko ?
Ƙyat ! Ƙyat
  Hajja ta mata alama da hannu
Oho sallah kike ?
Sake bugun ƙofar aka yi da ɗan ƙarfi da ya sanyata miƙewa a hankali bayan ta zura hijabin ta ,
Ƙasantuwar É—akin ba wani babba sosai bane taku kaÉ—an tayi ta isa jikin bango , dan haka ta fara shafawa bata sha wahala ba hannun ta ya sauka jikin Æ™ofar,Â
  Waye ne ?
  Ni ne buɗe min ƙofa
  Ta shaida muryar sa
 kama mariƙar ƙofar tayi ta murɗa sai dai bata ji alamun ƙofar ta buɗu ba ,
Ban iya ba
Â
tace da shi cikin ƴar ƙaramar muryar ta ,
  ,'Bata iya buɗe ƙofa ba ? Ya tambayi kan sa ,"
 Hajiya batta cikin ɗakin ??
 Tana sallah ,
   ta ce masa
 Bai ce kome ba ya gyara tsayuwa gami da jingina da jikin bangon ɗakin ,
  Cigaba tayi da tsayuwa tana ɗan laluba jikin ƙofar ko zata ji wajen buɗewa ,
  Ba'a ɗauki lokaci ba hajja ta idar da sallah ,
  Ke kam wannan yarinya anyi bagidajiya , yanzu ace buɗe ƙofa ma kin kasa ? Ni gusa ki ban guri ,
 buɗe masa ƙofar tayi ya shigo suka gaisa ,
  Hajja akwai abunda kuke buƙata ne ?
  Babu abunda muke buƙata ɗan nan , mun gode ƙwarai da hidima ,
  Idon sa ya ɗora kan baby mama ,
 Â
Ta daina rigimou kou ? Ba ku buƙatar kome kou ?
Shiru falmata tayi domin bata ma san da ita yake ba ,
Hajja ta ce
fatima maigidan na magana
 Â
  Wanne maigida hajja ??
Wata ƙatuwar harara hajja ta wurga mata , tamkar falmatan tana ganin ta a ƙufule tace
  Baban jaririyar ta ki
A sanyaye ta ce me yace ? Wai zai tafi da baby ?
 Da sauri youssouf yace
Ban faɗi hakka ba fatima cewa nayi ba ku buƙatar kome ?
Eh !
  Ta bashi amsa tana zama bakin gado ta shiga laluben baby mama, hannun ta ya sauka bisa kan ta ta shiga shafawa a hankali ,
Ya juya ga hajja , ni zan shiga gari wajen aiki na , akwai yiwuwar gobe sai yammaci zan shigo , duk idan kun buƙaci wanni abu ku ƙira ma'aikatan otel ɗin ta kan wayar tarho ,
 Ga ta nan ,"
ya nuna mata telphone ɗin dake ajiye daga saman ƴar durowar gefen gado "
madallah hajiya ina sake godiya
Mune da godiya ai É—an nan mune da godiya , to to babu kome Allah shi taimaka muna nan muna addu'a
Ameen hajja sai gobe
  Ya juya yana barin ɗakin
Da sauri hajja ta zunguri falmata ,
  Ke baki san ki gaishe da miji ko kiyiwa miji addu'a bane ? yau ni hauwa'u na ga abunda ya fi ƙarfi na me zan gani haka ? Yanzu ashe haka za ki dunga gwada rashin hankali a gidan auren na ki ? Ko kuwa taƙamar yarinta kike ? To bari ki ji na faɗa miki ni lokacin da aka min auren fari ma ban kai ki cika ba , kin fini ƙugu da ƙirji da sharaɓa da kome ke har shekaru ma domin ni lokacin da aka min aure ma sha huɗu nake ko nonon arziƙi bani da su , amma billahil azeem ban yi irin wannan haukar da na hango somi-somin ta a tare da ke ba ,
  Ke kenan sai ƙwalafacin ƴa , alhalin kina gwadawa uban ta halin ko in kula , idan taƙamar ki son ƴaƴa ai sai ki kwantar da kai kema ki samu ki tara naki ba ki dunga gwada naci akan ƴar wasu ba ,
  Falmata wacce ta fara jin haushin hajja akan takurar da ta ke mata, muryar ta a cunkushe tace ,
 To a ta ya zan tara nawa ƴaƴan ??
  Sororo hajja tayi ,
 Ah lalle abun naki na yi ne, 'an biyawa bazaura hajji , to sai ki cigaba da tambaya ta , ranar bada amsa tana zuwa , aikin banza yarinya sai sokonci kika iya ,.
 Â
Washegari biyamuradi youssouf bashi zaune bashh&
har sai da ya samu wani É—an madai-daicin gida irin wanda yake so a unguwar ,(Banifandou 2) ya kamawa su falmata hayar sa ya biya kuÉ—in shekara guda cif ,
Ƙarfe hudu tayi masa a shahararren company ƙera kayan katako da shirya gida ,(sunwe) inda ya faɗa musu buƙatar sa na son a kai masa kaya dai-dai da tsari da fasalin gidan sa ,
Basu yi ƙasa a guiwa ba suka tashi ma'aikatan su har su huɗu suka je ganin gidan ,
Hotunan gadaje , kujeru da sauran kayan adon gida aka dunga nuna masa tare da kuÉ—aÉ—en su ,
Bai yi zari ba ya zabi dai-dai kudin sa , tare da matsayin Falmata a wajen sa ,
Ma'aikatan da kan su suka kwashi kayan a motar su zuwa gidan inda gobe zasu je su shirya kayan da safe ,
Sai sha biyun dare Youssouf ya koma hotel ɗin saboda tun ƙarfe takwas na dare yana tare da manyan su suna wata ganawa ta musamman da lieutenant-Gènèral da Major Général , waɗanda sune ƙashin bayan samun ɗaukakar sa a fannin aiki ,
Ya so ya je ya ga ɗiyar sa da yadda suka wuni amma ganin yadda dare ya riga yayi sai ya yi wucewar ɗakin sa kai tsaye , da zummar gobe zai gana da su cikin rashin sanin sa yini baby mama tayi da matsanancin zazzabi tare da mura , banda kuka babu abunda take , tun falmata na rarrashi ita kaɗai har hajja ma ta karɓa , duk da haka ta ƙi shiru , zuwa dare har shiɗewa take gaba ɗaya hankalin su ya gama tashi banda kuka babu abunda falmata take ko abinci sun gagara ci ,
Ganin duhu ya sawo kai ga youssouf bai zo ba ya sa hajja me wurya fitowa daga É—akin ba tare da ta san takamaimai ina zata nufa ba , Allah ya taikaita mata wahala ya gama ta da É—aya daga cikin ma'aikatan otel É—in da ya kawo musu abincin rana ,
  Ƙasa-ƙasa tace
 Ka ji min sakarya auren da tun baki kai gidan ba kike fatan ki dawo , ??
Kawo ƙuɗin na riƙe mata Rahima, irin kunyar nan ce ta amare take gwada mana ,
 Â
Rahima da take murmushi a hankali ta miƙawa hajja me wurya kuɗin ,
Madallah Allah ya sanyawa auren ku Albarka Allah ya sa abokiyar arziki ce , Allah ya kauda shaiÉ—anun aljanu da na mutane a tsakanin ku , Allah ya sa mutuwa É—ai ita zata raba ku, Allah kuma ya baku zuri'a masu albarka irin wacce manzo Allah zai yi alfahari da ita !
  Laɓɓan Youssouf ne suka motsa a hankali da ,"Ameen .
  Rahima ita ta raka su har bakin mota tana jin yadda kewar su take taso mata , ai anyi sabo zaman watanni tare , duk da cewa ta so tafiyar su tafi haka tsawo sai dai damar bata samu ba , amma ko babu kome tayiwa fatima murnar samun ɗanɗasheshen mijin da ya ƙere sa'an auren ta ta ko'ina hakkun fatima me sa'a ce .
  Da wannan tunanin ta rufe musu ƙofar motar bangaren da falmata ta shiga inda suke zaune tare ita da hajja me wurya a bayan motar , Biyamuradi da direban sa suna gaba ," .
*****
Tafiya ce suka ɗora ta miƙaƙƙiya tun daga maiduguri zuwa sokoto , inda basu samu isa sokoto ba sai cikin dare misalin sha biyu da rabi , alamun gajiya da suka bayyana baro-baro ga falmata tare da baby mama wacce ta ke yin ƙananun rikici na gajiya da rikon hannun ya sa youssouf ya kama musu ƴan ɗakuna a wani ƙaramin guess inn da yake cikin garin na sokoto zuwa wayewar gari sun huta sun kuma sake shiri sai kuma su faɗa yankin niger ta," ilela ," su ɗau hanya ta birnin N'konni da zai ɗaura su kan kodoben da za su sadu da birnin Niamey ɗin niger ....!
Ba su suka samu isa Niamey ba sai ranar Asabat da misalin ƙarfe bakwai na dare duk kuwa da gudun da direban ya dunga shararawa tun da suka faɗa yankin niger kasancewar sun shigo ƙasar su , kowa yaga gilmawar motar su basu hanya ake ,
Kai tsaye direban ya wuce da su ( Radisson Blue hotel,) ƙarƙashin umarnin youssof , kasancewar shahararren hotel ɗin mafi yawan lokuta nan ne wajen sauƙar sa idan wani aiki ya kawo shi Niamey ɗin kasantuwar hotel ɗin kusa yake da manyan ma'aikatu masu muhimmanci na ƙasar da ke babban birnin Niamey ,
Babu ɓata lokaci ya kama musu ɗakuna inda hajja me wurya da falmata zasu zauna a ɗaki guda , (one bedroom Residence ) dake ƙasa shi kuma ya Kama nasa ɗakin a sama ( royal suite ) inda ya saba zama idan ya zo otel ɗin yayin da direba yayi tafiyar sa inda sauran abokanan aikin su suke , ya bar masa mukullin tare da motar , '
Bayan yayi wanka ya sallaci isha'i , misalin ƙarfe takwas da rabi ya sauko ƙasa , ɗakin da suke ya tasamma , ƙwanƙwas musu ƙofa yayi ,
Hajja me wurya tana sallar isha'i lokacin , falmata kuwa ta idar tana kwance bisa faffaÉ—an gadon ta sanya baby mama a gaba wacce take ta baccin gajiya bayan an cika mata ciki da madarar ta me É—umi ,
Sake ƙwanƙwasa ƙofar yayi a karo na biyu yana sake kallon number ɗakin da take rubuce a jikin wani ɗan katako dake sakale a jikin ƙofar ,"nan ne dai ɗakin nasu ,"
Miƙewa zaune tayi
  Hajja kamar ana buga ƙofa ko ?
Ƙyat ! Ƙyat
  Hajja ta mata alama da hannu
Oho sallah kike ?
Sake bugun ƙofar aka yi da ɗan ƙarfi da ya sanyata miƙewa a hankali bayan ta zura hijabin ta ,
Ƙasantuwar É—akin ba wani babba sosai bane taku kaÉ—an tayi ta isa jikin bango , dan haka ta fara shafawa bata sha wahala ba hannun ta ya sauka jikin Æ™ofar,Â
  Waye ne ?
  Ni ne buɗe min ƙofa
  Ta shaida muryar sa
 kama mariƙar ƙofar tayi ta murɗa sai dai bata ji alamun ƙofar ta buɗu ba ,
Ban iya ba
Â
tace da shi cikin ƴar ƙaramar muryar ta ,
  ,'Bata iya buɗe ƙofa ba ? Ya tambayi kan sa ,"
 Hajiya batta cikin ɗakin ??
 Tana sallah ,
   ta ce masa
 Bai ce kome ba ya gyara tsayuwa gami da jingina da jikin bangon ɗakin ,
  Cigaba tayi da tsayuwa tana ɗan laluba jikin ƙofar ko zata ji wajen buɗewa ,
  Ba'a ɗauki lokaci ba hajja ta idar da sallah ,
  Ke kam wannan yarinya anyi bagidajiya , yanzu ace buɗe ƙofa ma kin kasa ? Ni gusa ki ban guri ,
 buɗe masa ƙofar tayi ya shigo suka gaisa ,
  Hajja akwai abunda kuke buƙata ne ?
  Babu abunda muke buƙata ɗan nan , mun gode ƙwarai da hidima ,
  Idon sa ya ɗora kan baby mama ,
 Â
Ta daina rigimou kou ? Ba ku buƙatar kome kou ?
Shiru falmata tayi domin bata ma san da ita yake ba ,
Hajja ta ce
fatima maigidan na magana
 Â
  Wanne maigida hajja ??
Wata ƙatuwar harara hajja ta wurga mata , tamkar falmatan tana ganin ta a ƙufule tace
  Baban jaririyar ta ki
A sanyaye ta ce me yace ? Wai zai tafi da baby ?
 Da sauri youssouf yace
Ban faɗi hakka ba fatima cewa nayi ba ku buƙatar kome ?
Eh !
  Ta bashi amsa tana zama bakin gado ta shiga laluben baby mama, hannun ta ya sauka bisa kan ta ta shiga shafawa a hankali ,
Ya juya ga hajja , ni zan shiga gari wajen aiki na , akwai yiwuwar gobe sai yammaci zan shigo , duk idan kun buƙaci wanni abu ku ƙira ma'aikatan otel ɗin ta kan wayar tarho ,
 Ga ta nan ,"
ya nuna mata telphone ɗin dake ajiye daga saman ƴar durowar gefen gado "
madallah hajiya ina sake godiya
Mune da godiya ai É—an nan mune da godiya , to to babu kome Allah shi taimaka muna nan muna addu'a
Ameen hajja sai gobe
  Ya juya yana barin ɗakin
Da sauri hajja ta zunguri falmata ,
  Ke baki san ki gaishe da miji ko kiyiwa miji addu'a bane ? yau ni hauwa'u na ga abunda ya fi ƙarfi na me zan gani haka ? Yanzu ashe haka za ki dunga gwada rashin hankali a gidan auren na ki ? Ko kuwa taƙamar yarinta kike ? To bari ki ji na faɗa miki ni lokacin da aka min auren fari ma ban kai ki cika ba , kin fini ƙugu da ƙirji da sharaɓa da kome ke har shekaru ma domin ni lokacin da aka min aure ma sha huɗu nake ko nonon arziƙi bani da su , amma billahil azeem ban yi irin wannan haukar da na hango somi-somin ta a tare da ke ba ,
  Ke kenan sai ƙwalafacin ƴa , alhalin kina gwadawa uban ta halin ko in kula , idan taƙamar ki son ƴaƴa ai sai ki kwantar da kai kema ki samu ki tara naki ba ki dunga gwada naci akan ƴar wasu ba ,
  Falmata wacce ta fara jin haushin hajja akan takurar da ta ke mata, muryar ta a cunkushe tace ,
 To a ta ya zan tara nawa ƴaƴan ??
  Sororo hajja tayi ,
 Ah lalle abun naki na yi ne, 'an biyawa bazaura hajji , to sai ki cigaba da tambaya ta , ranar bada amsa tana zuwa , aikin banza yarinya sai sokonci kika iya ,.
 Â
Washegari biyamuradi youssouf bashi zaune bashh&
har sai da ya samu wani É—an madai-daicin gida irin wanda yake so a unguwar ,(Banifandou 2) ya kamawa su falmata hayar sa ya biya kuÉ—in shekara guda cif ,
Ƙarfe hudu tayi masa a shahararren company ƙera kayan katako da shirya gida ,(sunwe) inda ya faɗa musu buƙatar sa na son a kai masa kaya dai-dai da tsari da fasalin gidan sa ,
Basu yi ƙasa a guiwa ba suka tashi ma'aikatan su har su huɗu suka je ganin gidan ,
Hotunan gadaje , kujeru da sauran kayan adon gida aka dunga nuna masa tare da kuÉ—aÉ—en su ,
Bai yi zari ba ya zabi dai-dai kudin sa , tare da matsayin Falmata a wajen sa ,
Ma'aikatan da kan su suka kwashi kayan a motar su zuwa gidan inda gobe zasu je su shirya kayan da safe ,
Sai sha biyun dare Youssouf ya koma hotel ɗin saboda tun ƙarfe takwas na dare yana tare da manyan su suna wata ganawa ta musamman da lieutenant-Gènèral da Major Général , waɗanda sune ƙashin bayan samun ɗaukakar sa a fannin aiki ,
Ya so ya je ya ga ɗiyar sa da yadda suka wuni amma ganin yadda dare ya riga yayi sai ya yi wucewar ɗakin sa kai tsaye , da zummar gobe zai gana da su cikin rashin sanin sa yini baby mama tayi da matsanancin zazzabi tare da mura , banda kuka babu abunda take , tun falmata na rarrashi ita kaɗai har hajja ma ta karɓa , duk da haka ta ƙi shiru , zuwa dare har shiɗewa take gaba ɗaya hankalin su ya gama tashi banda kuka babu abunda falmata take ko abinci sun gagara ci ,
Ganin duhu ya sawo kai ga youssouf bai zo ba ya sa hajja me wurya fitowa daga É—akin ba tare da ta san takamaimai ina zata nufa ba , Allah ya taikaita mata wahala ya gama ta da É—aya daga cikin ma'aikatan otel É—in da ya kawo musu abincin rana ,