← Book details Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 191 OF 269

Sashe 191

Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bayan sun idar gani tayi Falmata ta miƙe ta hau gadonta ta kwanta tare da jaan bargo har kai ta rufu , duk kuwa da cewa garin babu sanyi ,

Jugum tayi tana hangenta , kafin ta ce Falmata , garin ai babu sanyi meyasa kika rufu haka ?

Biris tayi da ita bata amsa ba , jikinta sai ya sake yin sanyin sanin da tayi cewa Falmatan tana jin ta sarai ƙin tankawa tayi ,

Sai ta miƙe ta naɗe sallayar , takunta ba ƙarfi ta fita ta ja mata ƙofar ɗakin bata yi taku uku ba ta ji ƙarar sanyawa ƙofar makulli da Falmata tayi ,

Sai ta waigo tana kallon ƙofar , tayi murmushi mai bayyana ciwon da zuciya ke yi , hawaye na taruwa a gurbin idanunta ƙwarai abunda ta fuskanta daga Falmata a yau ya taɓa ran ta , ɗakin Hajja ta koma bata sake bin ɗakin Falmata ba .

Daren ranar babu wanda ya ci abincin dare a tsakanin su Ukun Youssouf , Yakaka ,da kuma Falmata haka kowannen su ya kwana yana saƙa abunda yake ganin zai fissheshi ,

Ƙarfe huɗu da rabi da Hajja ta farka ta tarar Yakaka ta haɗa kayanta kaf , cikin ƴar jakar da ta zo da shi da tana zaune shiru ta jingina kanta da jikin bango ,

Tausayinta ya kama Hajja , bayan ta É—aura Alwala ta fito sai ta zauna a gefenta ,

"Yakaka uwar Mama

Ta ƙira sunanta , bata amsa ba amma ta maida hankalinta gareta ,

" Ya naga kin É—auko jakar kaya haka ?ko..

" Tafiya zan yi Hajja , yau zan koma Nigeria , daman domin na gansu na zo kuma ai na gansu , na ga mutuwar Mama a idanuna , babu sauran zama da zan sake yi zan tafi yau .

Ta ƙarasa zancen hawaye masu ɗumin gaske suna sauƙa daga idanunta

Kamo hannun ta Hajja tayi , muryar ta a tausashe tace

" kiyi haƙuri Yakaka dukkanin abunda kika ga ya faru ga Rayuwar Bawa tun gabannin a halicce sa yake a rubuce cikin kaddarar rayuwar sa ,  kar ki bari shaidan ya raba tsakanin zumuncin ku ke da ƴar uwar ki , kan abunda ya gabata ku duka uku kaddarar rayuwar ku ce ta zo a haka , ke kece Babba ki riƙe zumuncin ku ƙam kar ki bari kowanne mahaluƙi ya shiga tsakanin ku , ku biyu ne rak a duniya ko kuwa kuna da wanda ya wuce junan ku ne ??

Girgiza kai Yakaka tayi alamun a ah , sai kuma tace " Hajja Amma Falmata ta samu wanda ya fini tu.....

" kul kar ki bari zuciyarki ta miki mummunar saƙar da zata wargaza muku zumuncin ku , kiyi haƙuri ki maida kome ba kome ba , kiyi haƙuri da jarabawar Ubangiji Allah zai miki tukuici da mafificin abunda duk kika rasa kin ji ko ?

" to
Ta amsa tana share hawayenta , Hajja ta cigaba da cewa , "yadda kuka haɗu kuna murnar ganin juna kar ku rabu kuna zargin juna ku rabu da farin-cikin da zai ƙara danƙon zumuncin ku kin ji ko ?

" naji nagode Hajja ,

Shiru suka yi suna saurara lokacin da suka ji an taɓa ƙofar falon , sai dai basu kawo kome a rai ba ga zaton dukkanin su Falmata ce ta dawo daga turakar Mijinta ,

Hajja ta ɗora da cigaba da yiwa Yakaka nasiha tare da gwada mata girman zumunci. Da ya sa ta jin sabuwar ƙaunar 'yar uwarta na game mata jini ,

Lokacin da gari yayi shaa , sai ta fito falo da jakar kayanta tana jiran fitowar Falmata domin suyi sallama ta kuma sake neman yafiyarta , 'yan kuɗaɗenta kimsnin dubu goma sha uku a ƙulle a marar ta , sai ta ware dubu uku da ɗari hudu zata bawa Falmata kyautar su ita kuma ta san dubu goma zai sada ta da birnin Maiduguri har ƙwaryar gidan Prof .

Zaman fiye da mintoci goma ta yi lokacin da ta ji an shigo Falon a hankali ta kai ganinta kan sa yana shirye tsaf cikin kakinsa na soji , sai ta tuno da ganin da tayi masa a baya can ,

Da sauri ta ɗauke kanta ta mayar da ganinta ƙofar ɗakin Falmata ,

Shima a ɗarare ya ƙaraso falon fuskarsa babu walwala , a kusan tare suka furta kalmomin

"ina kwana ?

Shi ya riga ta amsawa da "lafiya ,

Sai duk suka yi shiru , shi bakinsa É—auke yake da jawabi duk da cewa a yau ya hango sassauci daga gareta a karon farko ,

Ƙarasowar Hajja wajen ya sa shi zama akan kujerar da take kusa da shi , gaisawa suka yi tana sake yi musu ta'aziya su duka biyun , har ta miƙe sai yace

"Hajja ina Fatima ?

Hajja tace tana ciki Babban soja , a ƙirata ne ?

"eh Hajja a ƙirata ,

Hajja ta nufi É—akin Falmata ,

Haka kawai Yakaka ta ji zuciyarta ta tsinke , a karo na farko ta ji tsoron kar Youssouf ya furta cewa ya saki Falmata da tun-tuni ta fahimci ta faɗawa son shi , tausayi take ji , ita ta san yadda raɗaɗin so yake , bata fatan Falmata ta ɗan-ɗana zogin rasa masoyi , a yanzu zata so Falmata ta tsira da masoyinta , abunda ke cikinta kuma ya rayu kusa da mahaifinsa ƙarƙashin gatan uwa da uba a lokaci guda ,

Dan haka ta yunƙuro da zummar yin magana ta shaida janyewar ƙudirinta akan sa ,

fitowar Hajja ya katse ta , inda take sanar da su Falmata bata É—akin ,

"tana ina Hajja ?

Youssouf ya tambaya da É—an shakku a muryar sa ,

"ban sani ba Babban soja kuma bata can sashin naka ?

Ya miƙe tsaye lokacin da yake cewa

"bata can ai Fatima batta je ga sashi na ba ,

su dukkanin su sai suka yi tsaye cikin É—arsuwar sabon tashin hankali a rayukan su

Kamar haɗin baki sai suka bazama neman ta , lungu da saƙo na gidan , Youssouf da Yakaka suna haɗawa da ƙwalla ƙiran sunanta , amma ko alamu babu kurwar ta a gidan , dawowa suka yi suka haɗu a falon zuwa lokacin Yakaka kuka take yi , shi kuwa Youssouf idanunsa ne suka kaɗa jawur ,  da wani irin tasowar mummunan ɓacin rai lokacin da tunanin sa ya gama hasaso masa abunda ke faruwa ya dubi Yakaka da wani irin sauti yace

" Ina kika kai ta ? Ina kika ɓoye min Matata ?  Kiyi gaugawar sanar da ni kafin ki riski fushina Yakaka ..

Yakaka ta zaro ido da maÉ—aukakin mamaki tana kallon sa ,

"ita Youssouf yake nufin ta sace Falmata ƙanwarta ? Wanne irin mummunar kalma ne wannan yake jifatan ta da su ??
   Saɓon ɓacin rai ya bijiro mata .

Assalamu Alaikum masu karatu dafatan kuna lafiya ?

Wannan shafin kachokam ɗinsa sadauƙarwa ne ga duk wasu iyayen masu ɗauke da cutar Amosanin jini ,( Sickle Cell Disease)

Ku sani ya ƴan uwa Allah ya ɗora mana ne domin ya san zamu iya , wataƙila kuma domin hakan ya zamto hanyar samun Rahamar Ubangiji a  gare mu mu iyayen da kuma su da suke ɗauke da cutar ( muna fatan haka )

Ku sani cewa cuta irin wannan mai wahalarwa baiwa ce da ba kowa Allah ke ɗorawa ba , dan haka muyi ƙoƙari wajen basu kulawa tare da haƙuri domin cinye jarabawar da Allah ya yi muna ta dalilinsu .

Kada mu danƙwafar da su , kada kuma mu banbanta su da sauran ƴan uwansu masu lafiya , ƙarfafawar mu tamkar ƙara musu lafiya da walwala take yi a gare su, saɓanin haka zai iya sawa suyi rauni su ji tamkar su basu da amfani a lokaci guda su ji sun gaji da duniya .

Cuta bata nuni izuwa ga mutuwa kamar yadda lafiya bata nufin tsawitar rayuwa ( nisan Kwana )  fatan mu Allah shi iyar muna , ya yi mana maganin abunda ya gagare mu , ya wadace mu da lafiya mai amfani .

Ina miƙa ta'aziyya ga dukkanin iyaye ,kakanni 'ƴan uwa na waɗanda suka rasa rayukan nasu ta sanadin ciwon Amosanin jini Sickle Cell Disease .

Jinjinar kuma ta tafi gare ku gawurtattun mayakan da Allah ya ratayawa cuta mai wahalarwa,  Da ku nake ( sickle cell Warriors ) ku din ai JARUMAI ne da suka banbanta da saura , ku cigaba da nuna jarumta watarana akwai waraka zata zo inshaAllah .

Nagode .
[12/10/2019, 2:44 PM] +234 706 503 6187: MAFARI
( Hargitsin Rayuwa)

Umm'muaz

44

Cikin motar ƙirar Golf 2 Wagon da take shilla gudu akan titin da zai sadu da jahar Tahoua .

Falmata ce a zaune daga kujerar da take daura da Direban da bakinsa yake cike da goro ,  yana ta bin wakar Sa'adu bori mai taken 'soyayya abun yi ce ,da take tashi ta cikin sifikun motar kamar zai fasa mata dodon kunne ,  ta  kare fiye da rabin fuskarta da ɗankwalin doguwar rigar jikinta da ta sanya hijabi a madadin sa

Ita ɗaya ce ƙwal mace a cikin motar sauran mazauna gidan baya na motar duk maza ne matasa majiya ƙarfi

***

Lokacin da ta samu isa tashar mota na birnin Niamey da misalin ƙarfe biyar da rabi na asubahi , babu yawaitar mutane a tashar da kyar ta samu wani dattijon ɗan kamasho inda ta shida masa Maidugurin Jahar Bornon Nigeria take son zuwa ,

A mamakance dattijon yake kallon ta , kafin yace mata ,

"kai tsaye Borno zaki tai dagga nan yarinya ?ko dai Sokoton Nigeria zaki tai dagga nan , a can kuma ki tai Borno ?

"Maiduguri zan tafi daga nan Baba, dan Allah ka kaini motar da zata tafi can .

ta bashi amsa tana share ƙwallar da taƙi tsayawa a idanunta ,

Da sauri ya tare ta da cewa ,
Chapter 191 · 0% Book details