Sashe 215
Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tana tura ƙofar idanun ta suka yi farin gani da kyakkyawar farar fuskar ta da yau hasken ta ya ninku har wani sheƙi take , tana ɗaukar idanu iyakar kyau Yakaka tayi sa cikin farar Lafayar da aka naɗa mata mai adon ƙananun flowers baby pink da ash color akan sissilkan yadin da aka mata siririyar doguwar riga da shima launin baby pink , kan ta an naɗa mata ɗaurin ɗankwali simple an soke mata shi a gashin ta .
Rungume ta Amnee tayi ta sumbaci goshin ta kafin ta kamo hannuwanta da suka sha ƙunshi irin zanen ƙunshin mutan chadi jazur da su sun yi gwanin sha'awa , da manyan awarwarayen zinaren da Amnee ce ta bata su , suka daɗa fiddo martaba da kyaun hannunwan nata .
" da hannu ta yafito Falmata wacce take tsaye daga bakin window da alama akwai abunda yake taɓa ran ta a dai-dai lokacin , taƙi yadda a mata makeup sai yar hoda da man baki masu kyau aka shafa mata a cewar ta idanun ta basu cika lafiya ba bata son makeup , ita ma shirye take cikin wani pink ɗin leshi da aka mata ɗinkin Buba da zane tayi kyau fes da ita an mata ɗaurin ɗankwalin da ya fiddo zagayayyar cikakkiyar fuskar ta da ta sake yin tuɓus-tuɓus tana sheƙi sakamakon gyaran Hajje Nadiya da fatar ta ta karɓa .
Haɗa hannuwan su waje ɗaya tayi , tana cewa Falmata ," ki je ki raka Yayar ki sashin Yayan ku Babba zata gaisa da baƙi , idan sun gaisa ki tabbatar kin dawo min da ita hannu na yadda na ɗanka miki ita kin san yau ita tafi lu'ulu'a daraja .
Ƴar kyakkyawar dariya Falmata tayi kafin tace " an gama Amnee watau yau ni ce ƴar jagora ba ni za'a jagoran ta ba kai Alhamdulillahi Allah mun gode maka da ka nuna mana wannan ranar,
Amnee tana dariya ta roko su har ƙofar sashin ta ko'ina suka gifta ana ga Amarya ga Amarya ana bin ta da kallon sha'awa har da masu yi mata hoto ,
Falmata ita ta fara yin sallama a ƙofar falon , da aka musu iznin shiga ma sai da ta kai kusan minti guda a ciki kafin Yakaka ta saɓile takalman ta ta sanya ƙafafun ta ciki kan ta a ƙasa ta samu gefe zata zauna daga ƙasa , da sauri Falmata ta riƙo ta dai-dai lokacin da Doctor Suleiman ma yake cewa
" Kai kai Amarya ya za ki zauna a ƙasa ? Tashi-tashi ƙanwata yau ai ranar ku ce kamata yayi ma a dunga miki yawo da kujera ta musamman dan zaman ki kin san yau ke da sarauniyar England matsayin ku kai-da-kai yake .
A hankali ta É—ago kanta bayan ta zauna akan kujerar da Falmata take kai suna gaisawa da Doctor Hamza
jin muryar sa raɗau tayi mata kama da na wanda ta sani , shima Doctor Suleiman yana ƴar dariyar tsokanar ta da yake sauran Kalaman bakin sa suka maƙale masa a maƙogoro ganin fuskar ta ɗauke da kwalliya da sheƙin Amarci bai hana shi ya gane ta ba duk kuwa da cewa ganin sa da fuskar tata sau biyu ne rak , amma ta riga ta zanu a zuciyar sa mafarkin ta a yanayi ya irin haka a gaban sa abune da ya jima yana yi ,
Sai dai a wannan karon zahiri ita ce a bayyane a gaban sa amma ba a matsayin ta sa ba da kullum yake hari , a matsayin matar aminsa na ƙud da ƙuɗ take , cike da ruɗanin da ya gagara ɓoyewa bayan ta ɗauke ido daga kan sa da sauri , yace
" Abokina daman wannan ce Amaryar ta ka ?
Daga Yakaka , Youssouf har falmata sai da zuciyoyin su suka sauya bugu da mabanbanta tunaninnika da ya musu dirar mikiya ,
Æangaren Doctor Hamza a take É“akin-cikin sa ya nemi dawowa sabo abunda yake gudu kenan tun farin farko da kuma ya sashi tsanar ta , cuÉ—anya da tayi ta yi da mazaje .
Da sautin da shima bai ɓoye ɓacin-ran sa ba a daƙile yace " eh ita ce , ki gaishe shi mana ku koma ciki .
Muryar Yakaka na maƙyar-ƙyartar da ta ƙarawa Doctor Hamza tabbacin rashin gaskiyar ta ta gaishe da Doctor Suleiman da gumi yake tsattsafowa a goshi , yana share gumin ya amsa da " lafiya lau Aminatu , nayi muku murna kin ji Allah ya sanya Alheri .
A ɗan kaikaice Doctor Hamza yake kallon sa lokacin da Yakaka da Falmata wacce jikinta yayi sanyi laƙwas da yanayin da ta gani a tare da su biyun suka fice daga falon .
Kafin Doctor Hamza yayi wani yunƙuri Doctor Suleiman da ya miƙe tsaye cikin wani irin yanayin da yake bayyana alhinin da zuciyar sa ke ciki yace " Hamza ka min shigar sauri , why ? Amina da nake baka labari ita ce wannan Abokina ita ka Aura .
Da sauri Doctor Hamza shima ya miƙe , kafin yace kome Doctor Suleiman ya sake katse shi cikin yanayin da yafi na ɗazu rauni , ya cigaba da cewa , " Na taya ka murna Abokina babu shakka Allah ya arzuta ka da kamilar Mace mai nagartattun halaye , ina taya ka murna sosai ina kuma yi muku addu'ar samun ɗorewar zaman lafiya babu shakka matar mutum daga gare shi take ...
Katse shi Doctor Hamza yayi a mamakance yake cewa ," kana nufin wannan Aminar ita ce Amina , Amina da kake bani labarin ta ?
" ƙwarai da gaske ita ce .
Shiru su biyun suka yi baƙon yanayin da ya ziyarce su yana samun damar mamayar tunanin su , muryar Doctor hamza ta sake ratso wajen da yake cewa " Abokina Dan Allah ka bani labarin haɗuwar ku da duk wani abunda ka sani game da Amina .
Bayan komawar su Yakaka cikin gida gaba É—aya sai ta rasa sukuni sarai ta gane ko wanene abokin Yaya dakta , shine mutumin da ya dunga bibiyar ta da sunan soyayya tsawon shekaru wanda har Malama Maryam da Lubna sun san shi , sai yau ta tuno rana ta farko da ta fara ganin shi a duniya ranar da suka fara haÉ—uwa da shi da kan sa Doctor Hamza tare ta fara ganin su , shine wannan abokin nasa da ya ji tausayin su a lokacin da Doctor Hamza yake hora su kan fitsarin da Falmata ta yi masa a office har ma ya basu kuÉ—i yace su sayi hijabi su suturta jikin su .
Sai yau ta gane shi gaba É—aya , amma yanayin da ta hango a fuskar Doctor hamza kafin barin su falon bayan Suleiman ya nuna ya san ta ya bata tsoro , sanin da tayi daman ita a wajen sa abar tuhuma da zargi ce , tsoronta ya ninku lokacin da tayi hasashen kar Suleiman ya sake dasa zarginta a zuciyar Doctor Hamza .
An cigaba da shagalin biki zuwa Yamma aka fara shirye-shiryen tafiya Dinner da dangin Mijin Rahima ne suka shirya saboda su nan Baa baya son ire-iren bidi'o'in baya yarda a kama waje a tafi biki kome za'a yi a harabar faffaɗan gidan ake yi , sai dai fa idan dangin miji ne suka shirya abunsu ko kuwa bayan an miƙa amarya gidan ta ayi ta can .
Shiri ake ta yi sosai saboda har Amnee da Khaalty Rahima ma zasu su a karon farko saboda ta roƙi Baa yau ɗaya tal ya bari su tafi tare har da Yakaka da Falmata tunda shi yaƙi yadda a shirya ayi daga Aljihun sa .
Albarkacin farin-cikin da yake ji na wannan ranar bai jaa gardama sosai ba yace su je amma a kula a kuma dawo da wuri .
Ana gaf da tafiyar bayan isha'i Doctor Hamza ya shigo gidan da tunda ya fita raka abokansa bai dawo ba ya zarce gidan su sofiya wacce tunda aka ɗaura auren take ƙiran sa a waya daga ya ɗaga sai ta fashe da kuka tana ihu tare da cewa sai ta kashe Yakaka ,
Tun abun na ba shi dariya har ya fara damuwa sosai tausayin ta ya tsirga masa , shi shaida ne akan irin son da take yi masa yana tsoron kar wani abu ya samu Æ´ar mutane ta dalilin haka dan haka da yayiwa su Suleiman rakiya suka rabu cikin raha da barkwanci sai ya kama hanyar gidan su Sofi
Kacha-kacha ya tarar da ita tayi manƙas cikin ƙwayoyin da ta dunga afawa , tun lokacin da labarin ɗaurin auren ya zo ma bayan a jiya sai da ta bi malamai kusan biyar akan lamarin duk kuma suka tabbatar mata kan cewa za'a yi aikin da zai sa a fasa auren a daren kafin gari ya waye , sai dai ga shi babu wanda aikin sa ya ci sai asarar kuɗi da ta tafka .
Tun kuma a jiyan ta dunga ƙiran layin Samy baby amma bata samun ta , damuwar ta ta ninku ba adadi .
abunda ya mummunan kaɗa masa ƴan hanji bai taɓa sanin Sofin sa na shan kayan maye ba , ashe duk ihun da take masa a waya bata cikin hayyacin ta ? Kwayoyi ta fara sha a sanadin ƙarin auren da yayi ?
Ƙwalla ne suka tarar masa a ido yana jin takaicin uwa irin Hajja Kori da baza ta iya tanƙwara ƴar ta ba , tayi ko ta bari , da ya shigo gidan ma bai ganta ba ko tana ina ? oho
Haka da kyar ya sha kokuwa da ita tana doddoke shi tana zagin Yakaka wasu lokutan har da Amnee da Baa , haka dai ya daure ya sa tayi wanka ya taya ta shirya yana yi yana rarrashin ta , ya rubuta Allurar da yake son yayi mata ya bawa maigadi ya sayo ya kawo ya danna mata , bayan ya haÉ—a mata tea ta sha kaÉ—an tayi bacci .
A gajiye liƙis ya baro gidan , zuciyar sa cike da tunanin maganganun da Suleiman ya faɗa masa game da Yakaka yana zakwaɗin samun tabbacin sahihancin su .
Rungume ta Amnee tayi ta sumbaci goshin ta kafin ta kamo hannuwanta da suka sha ƙunshi irin zanen ƙunshin mutan chadi jazur da su sun yi gwanin sha'awa , da manyan awarwarayen zinaren da Amnee ce ta bata su , suka daɗa fiddo martaba da kyaun hannunwan nata .
" da hannu ta yafito Falmata wacce take tsaye daga bakin window da alama akwai abunda yake taɓa ran ta a dai-dai lokacin , taƙi yadda a mata makeup sai yar hoda da man baki masu kyau aka shafa mata a cewar ta idanun ta basu cika lafiya ba bata son makeup , ita ma shirye take cikin wani pink ɗin leshi da aka mata ɗinkin Buba da zane tayi kyau fes da ita an mata ɗaurin ɗankwalin da ya fiddo zagayayyar cikakkiyar fuskar ta da ta sake yin tuɓus-tuɓus tana sheƙi sakamakon gyaran Hajje Nadiya da fatar ta ta karɓa .
Haɗa hannuwan su waje ɗaya tayi , tana cewa Falmata ," ki je ki raka Yayar ki sashin Yayan ku Babba zata gaisa da baƙi , idan sun gaisa ki tabbatar kin dawo min da ita hannu na yadda na ɗanka miki ita kin san yau ita tafi lu'ulu'a daraja .
Ƴar kyakkyawar dariya Falmata tayi kafin tace " an gama Amnee watau yau ni ce ƴar jagora ba ni za'a jagoran ta ba kai Alhamdulillahi Allah mun gode maka da ka nuna mana wannan ranar,
Amnee tana dariya ta roko su har ƙofar sashin ta ko'ina suka gifta ana ga Amarya ga Amarya ana bin ta da kallon sha'awa har da masu yi mata hoto ,
Falmata ita ta fara yin sallama a ƙofar falon , da aka musu iznin shiga ma sai da ta kai kusan minti guda a ciki kafin Yakaka ta saɓile takalman ta ta sanya ƙafafun ta ciki kan ta a ƙasa ta samu gefe zata zauna daga ƙasa , da sauri Falmata ta riƙo ta dai-dai lokacin da Doctor Suleiman ma yake cewa
" Kai kai Amarya ya za ki zauna a ƙasa ? Tashi-tashi ƙanwata yau ai ranar ku ce kamata yayi ma a dunga miki yawo da kujera ta musamman dan zaman ki kin san yau ke da sarauniyar England matsayin ku kai-da-kai yake .
A hankali ta É—ago kanta bayan ta zauna akan kujerar da Falmata take kai suna gaisawa da Doctor Hamza
jin muryar sa raɗau tayi mata kama da na wanda ta sani , shima Doctor Suleiman yana ƴar dariyar tsokanar ta da yake sauran Kalaman bakin sa suka maƙale masa a maƙogoro ganin fuskar ta ɗauke da kwalliya da sheƙin Amarci bai hana shi ya gane ta ba duk kuwa da cewa ganin sa da fuskar tata sau biyu ne rak , amma ta riga ta zanu a zuciyar sa mafarkin ta a yanayi ya irin haka a gaban sa abune da ya jima yana yi ,
Sai dai a wannan karon zahiri ita ce a bayyane a gaban sa amma ba a matsayin ta sa ba da kullum yake hari , a matsayin matar aminsa na ƙud da ƙuɗ take , cike da ruɗanin da ya gagara ɓoyewa bayan ta ɗauke ido daga kan sa da sauri , yace
" Abokina daman wannan ce Amaryar ta ka ?
Daga Yakaka , Youssouf har falmata sai da zuciyoyin su suka sauya bugu da mabanbanta tunaninnika da ya musu dirar mikiya ,
Æangaren Doctor Hamza a take É“akin-cikin sa ya nemi dawowa sabo abunda yake gudu kenan tun farin farko da kuma ya sashi tsanar ta , cuÉ—anya da tayi ta yi da mazaje .
Da sautin da shima bai ɓoye ɓacin-ran sa ba a daƙile yace " eh ita ce , ki gaishe shi mana ku koma ciki .
Muryar Yakaka na maƙyar-ƙyartar da ta ƙarawa Doctor Hamza tabbacin rashin gaskiyar ta ta gaishe da Doctor Suleiman da gumi yake tsattsafowa a goshi , yana share gumin ya amsa da " lafiya lau Aminatu , nayi muku murna kin ji Allah ya sanya Alheri .
A ɗan kaikaice Doctor Hamza yake kallon sa lokacin da Yakaka da Falmata wacce jikinta yayi sanyi laƙwas da yanayin da ta gani a tare da su biyun suka fice daga falon .
Kafin Doctor Hamza yayi wani yunƙuri Doctor Suleiman da ya miƙe tsaye cikin wani irin yanayin da yake bayyana alhinin da zuciyar sa ke ciki yace " Hamza ka min shigar sauri , why ? Amina da nake baka labari ita ce wannan Abokina ita ka Aura .
Da sauri Doctor Hamza shima ya miƙe , kafin yace kome Doctor Suleiman ya sake katse shi cikin yanayin da yafi na ɗazu rauni , ya cigaba da cewa , " Na taya ka murna Abokina babu shakka Allah ya arzuta ka da kamilar Mace mai nagartattun halaye , ina taya ka murna sosai ina kuma yi muku addu'ar samun ɗorewar zaman lafiya babu shakka matar mutum daga gare shi take ...
Katse shi Doctor Hamza yayi a mamakance yake cewa ," kana nufin wannan Aminar ita ce Amina , Amina da kake bani labarin ta ?
" ƙwarai da gaske ita ce .
Shiru su biyun suka yi baƙon yanayin da ya ziyarce su yana samun damar mamayar tunanin su , muryar Doctor hamza ta sake ratso wajen da yake cewa " Abokina Dan Allah ka bani labarin haɗuwar ku da duk wani abunda ka sani game da Amina .
Bayan komawar su Yakaka cikin gida gaba É—aya sai ta rasa sukuni sarai ta gane ko wanene abokin Yaya dakta , shine mutumin da ya dunga bibiyar ta da sunan soyayya tsawon shekaru wanda har Malama Maryam da Lubna sun san shi , sai yau ta tuno rana ta farko da ta fara ganin shi a duniya ranar da suka fara haÉ—uwa da shi da kan sa Doctor Hamza tare ta fara ganin su , shine wannan abokin nasa da ya ji tausayin su a lokacin da Doctor Hamza yake hora su kan fitsarin da Falmata ta yi masa a office har ma ya basu kuÉ—i yace su sayi hijabi su suturta jikin su .
Sai yau ta gane shi gaba É—aya , amma yanayin da ta hango a fuskar Doctor hamza kafin barin su falon bayan Suleiman ya nuna ya san ta ya bata tsoro , sanin da tayi daman ita a wajen sa abar tuhuma da zargi ce , tsoronta ya ninku lokacin da tayi hasashen kar Suleiman ya sake dasa zarginta a zuciyar Doctor Hamza .
An cigaba da shagalin biki zuwa Yamma aka fara shirye-shiryen tafiya Dinner da dangin Mijin Rahima ne suka shirya saboda su nan Baa baya son ire-iren bidi'o'in baya yarda a kama waje a tafi biki kome za'a yi a harabar faffaɗan gidan ake yi , sai dai fa idan dangin miji ne suka shirya abunsu ko kuwa bayan an miƙa amarya gidan ta ayi ta can .
Shiri ake ta yi sosai saboda har Amnee da Khaalty Rahima ma zasu su a karon farko saboda ta roƙi Baa yau ɗaya tal ya bari su tafi tare har da Yakaka da Falmata tunda shi yaƙi yadda a shirya ayi daga Aljihun sa .
Albarkacin farin-cikin da yake ji na wannan ranar bai jaa gardama sosai ba yace su je amma a kula a kuma dawo da wuri .
Ana gaf da tafiyar bayan isha'i Doctor Hamza ya shigo gidan da tunda ya fita raka abokansa bai dawo ba ya zarce gidan su sofiya wacce tunda aka ɗaura auren take ƙiran sa a waya daga ya ɗaga sai ta fashe da kuka tana ihu tare da cewa sai ta kashe Yakaka ,
Tun abun na ba shi dariya har ya fara damuwa sosai tausayin ta ya tsirga masa , shi shaida ne akan irin son da take yi masa yana tsoron kar wani abu ya samu Æ´ar mutane ta dalilin haka dan haka da yayiwa su Suleiman rakiya suka rabu cikin raha da barkwanci sai ya kama hanyar gidan su Sofi
Kacha-kacha ya tarar da ita tayi manƙas cikin ƙwayoyin da ta dunga afawa , tun lokacin da labarin ɗaurin auren ya zo ma bayan a jiya sai da ta bi malamai kusan biyar akan lamarin duk kuma suka tabbatar mata kan cewa za'a yi aikin da zai sa a fasa auren a daren kafin gari ya waye , sai dai ga shi babu wanda aikin sa ya ci sai asarar kuɗi da ta tafka .
Tun kuma a jiyan ta dunga ƙiran layin Samy baby amma bata samun ta , damuwar ta ta ninku ba adadi .
abunda ya mummunan kaɗa masa ƴan hanji bai taɓa sanin Sofin sa na shan kayan maye ba , ashe duk ihun da take masa a waya bata cikin hayyacin ta ? Kwayoyi ta fara sha a sanadin ƙarin auren da yayi ?
Ƙwalla ne suka tarar masa a ido yana jin takaicin uwa irin Hajja Kori da baza ta iya tanƙwara ƴar ta ba , tayi ko ta bari , da ya shigo gidan ma bai ganta ba ko tana ina ? oho
Haka da kyar ya sha kokuwa da ita tana doddoke shi tana zagin Yakaka wasu lokutan har da Amnee da Baa , haka dai ya daure ya sa tayi wanka ya taya ta shirya yana yi yana rarrashin ta , ya rubuta Allurar da yake son yayi mata ya bawa maigadi ya sayo ya kawo ya danna mata , bayan ya haÉ—a mata tea ta sha kaÉ—an tayi bacci .
A gajiye liƙis ya baro gidan , zuciyar sa cike da tunanin maganganun da Suleiman ya faɗa masa game da Yakaka yana zakwaɗin samun tabbacin sahihancin su .