Sashe 234
Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kina da zaɓi biyu ko dai na yanka ki a yanzu na kar ki na kar banza , na sa a ɗau gawar ki a yasar , ko kuwa kiyi duk abunda nace da ke ba tare da gardama ba , sannan ba kuma na son na sake jin tashin sautin muryar ki, ko numfashi mai ƙarfi kika jaa sai na yanke miki hanci bare ta kai ki ga magana babu makawa za ki tsinci halshen ki a ƙasa kina jina ko ?
Da sauri ta sake gyaÉ—a kai, wasu sabbin hawaye na sake tsiyayo mata .
"Hafsatouwa ki je ki kawo min rigar bayu da mayafi .
Kafin ta rufe baki Hafsatouwa ta yi waje ,
Nisawa Hajiya Mama tayi tana karkaɗa kafa cike da izza da mugunta tace "yarinya duk abun da kunnuwan ki suka jiye miki na kaddamar ina kuma kan gaɓar shirya wasu game da surukuwar ki da shi kan sa mijin ki haɗa da 'yal uwarki gasken gaske ne .
"Ki kuma tabbatar zan iya yin abunda yafi haka akan ki muddin kika yi kuskuren yi mini gaddama ko da sau É—aya ne .
"ÆŠauke idon ki daga kaina fitsararriya kin wani tsattsareni da ido uwa budurwar mujiya .
Ta ƙarasa zancen da tsawa da hargagin da yasa abun da ke cikin Falmata murɗawa.
Da sauri Falmata ta sunkuyar da kai tana jin tausayin kan ta na kawo mata , ita kuma irin tata kaddarar kenan mutuwa a hannun wannan azzalumar mata , da ita da abunda ke cikin ta , domin zuwa yanzu ta tabbatar babu wani mai tsaratar da ita sai fa Allah .
Dawowar Hafsatouwa riƙe da wasu tsummokara yasa Falmata sake tsorata "ka dai toshe mata hanci za suyi su hanata mumfashi har ta mutu ?
Saukar taunmokaran a jikin ta ya sa ta É—ago kan ta a firgice.
"Ki tashi ki saka kayan nan da gaugawa .
Babu yadda ta iya haka ta lafta waɗan nan kayan akan na jikin ta tana yi tana yunƙurin aman da yake taso mata sakamakon tsami da ɗoyin datti da kayan suke yi .
"Kiyi lulluɓi da kyau ki biyo ni a baya muddin kika yi wata alamar da tasa aka gane akwai wani abu wallahi kafin ki farga na soke ki.
Haka suka dunga ratsa sashi-sashi na gidan suna cin karo da bayu tsilla-tsillan da suke zubewa su gaishe da Hajiya Mama .
Har suka dangana da wani sashin da yafi kama da kango da yake can ƙuryar gidan da daga shi sai maƙabartan da take cikin gidan ta ɓaryar dama .
Da wani ɗan makulli Hajiya Mama tayi amfani ta buɗe ƙofar ainahin tangamemen falon da yake cikin sashin .
Ta ingiza Falmata wacce bata kai ga sanin cewa falon ya shiga ƙasa ba dan haka tana jefa ƙafar ta ta faɗa ciki ta gurɗe a ƙafa kiris ya rage ta faɗa a kan cikin ta Allah ya sa ta tokare ƙasa da hannuwan ta .
Lokacin da ta É—ago kai bata iya ganin fuskokin Hajiya Mama da Hafsatouwa saboda duhun da Falon yake É—auke da shi , da raunanan idanun ta hasken da yake shigowa daga can harabar gidan yayi kaÉ—an su iya gani tare da shi .
ÆŠallare mata ido da hasken wayar hannun ta da Hajiya Mama tayi yasa ta saurin runtse idanun ta kafin ta buÉ—e su da sauri jin abunda Hajiya Mamar take cewa .
" anan za ki cigaba da zama har zuwa lokacin da zan gama yanke hukunci kan matakin da zan ɗauka akan ki., idan kika yi yadda nake so ta hanyar zama salin-alin ba tare da kin yi wani motsin da zai sa asan kina nan ba , wataƙila na iya barin ki bayan na kafa miki sharɗaɗun cigaba da rayuwa a gidan nan .
"Muddin kuwa kika yi yunƙurin yin wani motsi da zai sa asan kina nan wallahi , wallahi , wallahi , ni ina iya kashe ki da hannu na kuma na sa a ɓatar da gawar ki .
Daga haka ta juya da sauri suka fita ita da Hafsatouwa daga inda Falmata take yashe tana iya jiyo saƙala ɗan makuba da aka yi aka kulle ta ta baya kafin ta fara jin sautin takun sawayen su akan busassun ganyayyakin bishiya su na barin wajen har dai zuwa lokacin da sautin su ya ɓace a kunnuwan ta .
Wani irin karkawa tsokar jiki zuwa gundarin zuciyar su ka shiga yi na tsananin tsoro da firgicin da ruhin ta ke ciki , kafin da wani irin sauti ta fashe da kuka , ta shiga rarrafawa da hannunwan ta da guiwar ta zuwa inda take tunanin nan ƙofar take ,
Lokacin da tayi karo da bango da hannuwanta duk biyu ta shiga bugun bangon cikin ɗimuwar rashin fahimtar ƙofa ce a wajen ko kuwa jikin bango ? .
Washegari da Asuba a Masallaci bayan sun idar da Sallah, Maimartaba tare da Youssoufa yana biye da shi a baya, kai tsaye sashin Maimartaba suka yiwa tsinke domin ganawa ta musamman .
Maimartaba yana sake tambayar Sa yanayin lafiyar jikin sa ?
Shi kuma yana amsa masa da cewa "yana cigaba da samun sauƙi sosai .
Bayan sun isa turakar Maimartaba Youssoufa zai zauna daga gefen shimfiÉ—ar da yake kai , yace masa "dawo nan kussa gareni mu tattauna yana masa nuni da kan shimfiÉ—a kusa da shi .
Da jin daÉ—i mai yawa Youssouf ya matsa kusa da shi .
Gyaran murya Maimartaba yayi kafin yace .
"Youssoufa wanne mataki kake É—auka bissa ga waÉ—an da suka ha'ince ka ?
Shiru Youssouf yayi kafin yace "Ranka shi daÉ—e dukkanin hukuncin da ka zartar .
Shiru mai martaba yayi kafin yace " Ubangiji Mai yawan yafiya ne , yana kuma ƙaunar bayin sa masu afouwa ga junan su a duk lokacin da aka zalunce su , shi yake tanada wa adalai taimako da kiyayewa, wato mutane masu aminci babu wani mugun abu da zai same su, amma mugaye ba za su sami kome ba, sai wahala bayan ubangiji ya bar su da kan su , Kada ka ɗaukar wa kanka fansa, ka dogara ga Ubangiji shi zai yi sakamako.
Youssoufa da yayi shiru yana sauraron sa , jin ya dakata ya sa shi É—ago kan sa a nutse
A kalaman maimartaba ya fahimci shawarar da ya ba shi cikin hikima ransa kuma ya sanyaya daga zafin da yake masa a duk lokacin da ya tuno da abunda aka masa dan haka sai yace "Nayi musu afouwa ranka shi daɗe amma ita ban iya sake riƙon Amren ta zan sauwaƙe mata daga can ta tai yankin su , mammadou kouma zan tafi mu dawo tare .
"Madallah da kai Youssoufa yadda kayi afouwa ga 'yan Adam da sunka maka ƙeta kai ma Allah shi maka afouwa bisa tarin laifukan ka .
"Amin Amin Baba .
Murmushi maimartaba yayi yana jin ƙaunar ɗan sa na kawo masa tabbas zuciyar wasu sassauƙa ce mai yawan yafiya .
"Yaushe za ka tafi Niamey domin kawo ƙarshen zaman su a magarƙama ? Ko kouwa saƙo za'a aika musu ?
"Da kaina zan je doumin na sanya hannu a takardar da zai sa a sake su sannan ita kuma zan sahale mata amre na , cikin kwanaki biyu masu zuwa zan tafi .
"Kafin tafiyar ka a sanya a tattara kayan ita wannan ɗiya a aika da su garin su , shiyar ta kouwa ni da kaina zan sa a shirya shi ga ita ɗiyar da muka amso amanar ta daga ƙasar su insha Allah ita tana cikin amintattun mu Allah ya cigaba da baku kariya baki ɗayan ku ya kuma dauwamar da zaman lafiya tare da zuri'a masu Albarka tsakanin ka da matayen ka .
Wani irin farin-ciki Youssouf ya ji yana ratsa shi jin cewa ashe Maimartaba da kan sa ya sa aka dawo da Falmata har ma kuma ga shi zai sa a shirya mata wajen zama a gidan hakan yana nufin samun 'yanci tare da tabbacin zaman sa har abada da Fatima , idan hakane yana godiya ga Allah da duk wasu hatsararruka da ya tsallaƙe tunda ya tsira da Fatima-zahra.
"Amin Nagode Nagode ranka shi daɗe Allah ya ƙara girma tare da nisan kwana .
"Allah shine abun godiya Youssoufa .
Sun jima suna tattaunawa Maimartaba yana ba shi shawarwari cikin hikima tare da yi masa nasiha har hantsi ya É—aga lokacin zaman fada ya gabato ,
Tare suka yi karin kumallo kafin yayi bankwana da Maimartaba zuciyar sa cike taf da farin-ciki gami da nutsuwa ta musamman , tabbas wanda duk yayi dace da iyaye na ƙwarai ya samu rabi na daga nasarar rayuwar sa .
Gefe guda yana sake jin haƙaƙewa akan rabuwa da Maimounatou bayan ta amsa masa tarin tambayoyin da kullum yake bitar su cikin ransa tare da burin jin amsa daga bakin ta .
Bai koma sashin su ba sai ya zarce shiyar Hajiya Umma zuciyar sa cike da ɗokin son ganin Fuskar Falmata a hasken ranar da ta fara ɗagowa , yana da tabbacin a shiyar Hajiya Umma anan aka mata masauƙi .
Abun Mamakin da ya tarar lokacin da ya riski falon Hajiya Umma bai wuce ganin ta tare da Hajiya Mama da sauran 'yan uwan sa baki É—aya ciki har da 'yan É—akin Hajiya Mama duk suna karin kumallo tare da hakan sosai yake sabon lamari a wajensu baki É—aya .
Cike da jin daɗin ganin su haka a tare ya ƙarasa falon kai tsaye kusa da Hajiya Umma ya zauna , yana gaishe ta kafin ya juya ya gaishe da Hajiya Mama wacce ta amsa cikin nuna tsantsar farin-ciki kafin ta ɗora da tambayar sa ƙarfin jikin sa ? A ƙarshe ta bi shi da wata doguwar addu'ar da yasa zuciyar Hajiya Umma haske har ma ta fara samun 'yar nutsuwa akan ta karo na farko , fuskar ta ta cika da annashuwa tana amsa jerin addu'o'in da Hajiya Mama ke yi .
Da wata irin kulawa da ta zarce ƙa'ida Hajiya Mama tace
Da sauri ta sake gyaÉ—a kai, wasu sabbin hawaye na sake tsiyayo mata .
"Hafsatouwa ki je ki kawo min rigar bayu da mayafi .
Kafin ta rufe baki Hafsatouwa ta yi waje ,
Nisawa Hajiya Mama tayi tana karkaɗa kafa cike da izza da mugunta tace "yarinya duk abun da kunnuwan ki suka jiye miki na kaddamar ina kuma kan gaɓar shirya wasu game da surukuwar ki da shi kan sa mijin ki haɗa da 'yal uwarki gasken gaske ne .
"Ki kuma tabbatar zan iya yin abunda yafi haka akan ki muddin kika yi kuskuren yi mini gaddama ko da sau É—aya ne .
"ÆŠauke idon ki daga kaina fitsararriya kin wani tsattsareni da ido uwa budurwar mujiya .
Ta ƙarasa zancen da tsawa da hargagin da yasa abun da ke cikin Falmata murɗawa.
Da sauri Falmata ta sunkuyar da kai tana jin tausayin kan ta na kawo mata , ita kuma irin tata kaddarar kenan mutuwa a hannun wannan azzalumar mata , da ita da abunda ke cikin ta , domin zuwa yanzu ta tabbatar babu wani mai tsaratar da ita sai fa Allah .
Dawowar Hafsatouwa riƙe da wasu tsummokara yasa Falmata sake tsorata "ka dai toshe mata hanci za suyi su hanata mumfashi har ta mutu ?
Saukar taunmokaran a jikin ta ya sa ta É—ago kan ta a firgice.
"Ki tashi ki saka kayan nan da gaugawa .
Babu yadda ta iya haka ta lafta waɗan nan kayan akan na jikin ta tana yi tana yunƙurin aman da yake taso mata sakamakon tsami da ɗoyin datti da kayan suke yi .
"Kiyi lulluɓi da kyau ki biyo ni a baya muddin kika yi wata alamar da tasa aka gane akwai wani abu wallahi kafin ki farga na soke ki.
Haka suka dunga ratsa sashi-sashi na gidan suna cin karo da bayu tsilla-tsillan da suke zubewa su gaishe da Hajiya Mama .
Har suka dangana da wani sashin da yafi kama da kango da yake can ƙuryar gidan da daga shi sai maƙabartan da take cikin gidan ta ɓaryar dama .
Da wani ɗan makulli Hajiya Mama tayi amfani ta buɗe ƙofar ainahin tangamemen falon da yake cikin sashin .
Ta ingiza Falmata wacce bata kai ga sanin cewa falon ya shiga ƙasa ba dan haka tana jefa ƙafar ta ta faɗa ciki ta gurɗe a ƙafa kiris ya rage ta faɗa a kan cikin ta Allah ya sa ta tokare ƙasa da hannuwan ta .
Lokacin da ta É—ago kai bata iya ganin fuskokin Hajiya Mama da Hafsatouwa saboda duhun da Falon yake É—auke da shi , da raunanan idanun ta hasken da yake shigowa daga can harabar gidan yayi kaÉ—an su iya gani tare da shi .
ÆŠallare mata ido da hasken wayar hannun ta da Hajiya Mama tayi yasa ta saurin runtse idanun ta kafin ta buÉ—e su da sauri jin abunda Hajiya Mamar take cewa .
" anan za ki cigaba da zama har zuwa lokacin da zan gama yanke hukunci kan matakin da zan ɗauka akan ki., idan kika yi yadda nake so ta hanyar zama salin-alin ba tare da kin yi wani motsin da zai sa asan kina nan ba , wataƙila na iya barin ki bayan na kafa miki sharɗaɗun cigaba da rayuwa a gidan nan .
"Muddin kuwa kika yi yunƙurin yin wani motsi da zai sa asan kina nan wallahi , wallahi , wallahi , ni ina iya kashe ki da hannu na kuma na sa a ɓatar da gawar ki .
Daga haka ta juya da sauri suka fita ita da Hafsatouwa daga inda Falmata take yashe tana iya jiyo saƙala ɗan makuba da aka yi aka kulle ta ta baya kafin ta fara jin sautin takun sawayen su akan busassun ganyayyakin bishiya su na barin wajen har dai zuwa lokacin da sautin su ya ɓace a kunnuwan ta .
Wani irin karkawa tsokar jiki zuwa gundarin zuciyar su ka shiga yi na tsananin tsoro da firgicin da ruhin ta ke ciki , kafin da wani irin sauti ta fashe da kuka , ta shiga rarrafawa da hannunwan ta da guiwar ta zuwa inda take tunanin nan ƙofar take ,
Lokacin da tayi karo da bango da hannuwanta duk biyu ta shiga bugun bangon cikin ɗimuwar rashin fahimtar ƙofa ce a wajen ko kuwa jikin bango ? .
Washegari da Asuba a Masallaci bayan sun idar da Sallah, Maimartaba tare da Youssoufa yana biye da shi a baya, kai tsaye sashin Maimartaba suka yiwa tsinke domin ganawa ta musamman .
Maimartaba yana sake tambayar Sa yanayin lafiyar jikin sa ?
Shi kuma yana amsa masa da cewa "yana cigaba da samun sauƙi sosai .
Bayan sun isa turakar Maimartaba Youssoufa zai zauna daga gefen shimfiÉ—ar da yake kai , yace masa "dawo nan kussa gareni mu tattauna yana masa nuni da kan shimfiÉ—a kusa da shi .
Da jin daÉ—i mai yawa Youssouf ya matsa kusa da shi .
Gyaran murya Maimartaba yayi kafin yace .
"Youssoufa wanne mataki kake É—auka bissa ga waÉ—an da suka ha'ince ka ?
Shiru Youssouf yayi kafin yace "Ranka shi daÉ—e dukkanin hukuncin da ka zartar .
Shiru mai martaba yayi kafin yace " Ubangiji Mai yawan yafiya ne , yana kuma ƙaunar bayin sa masu afouwa ga junan su a duk lokacin da aka zalunce su , shi yake tanada wa adalai taimako da kiyayewa, wato mutane masu aminci babu wani mugun abu da zai same su, amma mugaye ba za su sami kome ba, sai wahala bayan ubangiji ya bar su da kan su , Kada ka ɗaukar wa kanka fansa, ka dogara ga Ubangiji shi zai yi sakamako.
Youssoufa da yayi shiru yana sauraron sa , jin ya dakata ya sa shi É—ago kan sa a nutse
A kalaman maimartaba ya fahimci shawarar da ya ba shi cikin hikima ransa kuma ya sanyaya daga zafin da yake masa a duk lokacin da ya tuno da abunda aka masa dan haka sai yace "Nayi musu afouwa ranka shi daɗe amma ita ban iya sake riƙon Amren ta zan sauwaƙe mata daga can ta tai yankin su , mammadou kouma zan tafi mu dawo tare .
"Madallah da kai Youssoufa yadda kayi afouwa ga 'yan Adam da sunka maka ƙeta kai ma Allah shi maka afouwa bisa tarin laifukan ka .
"Amin Amin Baba .
Murmushi maimartaba yayi yana jin ƙaunar ɗan sa na kawo masa tabbas zuciyar wasu sassauƙa ce mai yawan yafiya .
"Yaushe za ka tafi Niamey domin kawo ƙarshen zaman su a magarƙama ? Ko kouwa saƙo za'a aika musu ?
"Da kaina zan je doumin na sanya hannu a takardar da zai sa a sake su sannan ita kuma zan sahale mata amre na , cikin kwanaki biyu masu zuwa zan tafi .
"Kafin tafiyar ka a sanya a tattara kayan ita wannan ɗiya a aika da su garin su , shiyar ta kouwa ni da kaina zan sa a shirya shi ga ita ɗiyar da muka amso amanar ta daga ƙasar su insha Allah ita tana cikin amintattun mu Allah ya cigaba da baku kariya baki ɗayan ku ya kuma dauwamar da zaman lafiya tare da zuri'a masu Albarka tsakanin ka da matayen ka .
Wani irin farin-ciki Youssouf ya ji yana ratsa shi jin cewa ashe Maimartaba da kan sa ya sa aka dawo da Falmata har ma kuma ga shi zai sa a shirya mata wajen zama a gidan hakan yana nufin samun 'yanci tare da tabbacin zaman sa har abada da Fatima , idan hakane yana godiya ga Allah da duk wasu hatsararruka da ya tsallaƙe tunda ya tsira da Fatima-zahra.
"Amin Nagode Nagode ranka shi daɗe Allah ya ƙara girma tare da nisan kwana .
"Allah shine abun godiya Youssoufa .
Sun jima suna tattaunawa Maimartaba yana ba shi shawarwari cikin hikima tare da yi masa nasiha har hantsi ya É—aga lokacin zaman fada ya gabato ,
Tare suka yi karin kumallo kafin yayi bankwana da Maimartaba zuciyar sa cike taf da farin-ciki gami da nutsuwa ta musamman , tabbas wanda duk yayi dace da iyaye na ƙwarai ya samu rabi na daga nasarar rayuwar sa .
Gefe guda yana sake jin haƙaƙewa akan rabuwa da Maimounatou bayan ta amsa masa tarin tambayoyin da kullum yake bitar su cikin ransa tare da burin jin amsa daga bakin ta .
Bai koma sashin su ba sai ya zarce shiyar Hajiya Umma zuciyar sa cike da ɗokin son ganin Fuskar Falmata a hasken ranar da ta fara ɗagowa , yana da tabbacin a shiyar Hajiya Umma anan aka mata masauƙi .
Abun Mamakin da ya tarar lokacin da ya riski falon Hajiya Umma bai wuce ganin ta tare da Hajiya Mama da sauran 'yan uwan sa baki É—aya ciki har da 'yan É—akin Hajiya Mama duk suna karin kumallo tare da hakan sosai yake sabon lamari a wajensu baki É—aya .
Cike da jin daɗin ganin su haka a tare ya ƙarasa falon kai tsaye kusa da Hajiya Umma ya zauna , yana gaishe ta kafin ya juya ya gaishe da Hajiya Mama wacce ta amsa cikin nuna tsantsar farin-ciki kafin ta ɗora da tambayar sa ƙarfin jikin sa ? A ƙarshe ta bi shi da wata doguwar addu'ar da yasa zuciyar Hajiya Umma haske har ma ta fara samun 'yar nutsuwa akan ta karo na farko , fuskar ta ta cika da annashuwa tana amsa jerin addu'o'in da Hajiya Mama ke yi .
Da wata irin kulawa da ta zarce ƙa'ida Hajiya Mama tace