Sashe 169
Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hankalin sa bai kwanta ba sai da ya yi masa jagora zuwa bakin ɗakin inda ya hango Falmata a kwance kan gado , an naɗe mata idanun nata da farin ƙyalle , da alama bacci take ,
Sanin da ya yi Mama bata cika lafiya ba ya sa dole ya bar asibitin tare da ita ya nufi gida da zummar dawowa zuwa anjima domin ba zai iya yin har tsawon wasu awanni masu yawa ba tare da ya gan ta ba , ya san halin da take ciki ba ,
Ko da suka dawo gida daga shi har Mama gidan bai musu daÉ—i ba ,
Mama kaɗai ya soyawa ƙwai tare da kifin gwangwani , ita ma bata wani ci na kirki ba ta ɗauke kai , Alamun ta ƙoshi ,
"Mama ki ci abinci sossai mana ,
Girgiza kai tayi tana ƙwalan-ƙwalan da ido ,
"Papa mu tafi wajen Mama yanzu ,
"zamu tafi idan kin ida cin abincin ki kin ji kou ?
Shiru tayi tana kallon sa ba tare da ta buɗe baki ta karɓi abincin da yake miƙa mata ba ,
Gajiya yayi da riƙe chokalin , ya ajiye gami da miƙewa yana jin yadda zuciyar sa ke cike da kewar ta , baki ɗayan hankalin sa na kan ta ,
Ya daÉ—e a zaune yana mata addu'a akan sallayar da ya idar da Sallar Azahar ,
Shafa kan Mama yayi wacce tayi bacci a gefen shinfiÉ—ar sallar sa ,
Cikin ran sa yana aiyana irin yawan kewar Mamar ta da tayi wanda ya duƙusar da walwalarta
ÆŠaukar ta yayi ya kaita É—aki ya kwantar tare da rufe ta da bargo , ya zauna daga bakin gadon ,
Wayar sa ya ɗauka ya latsa ƙiran layin Tafeeda da ya yi ƙiran sa a ɗazu lokacin da ake yiwa Falmata aiki , bai samu damar ɗaukar kiran nasa ba
Bayan sun gaisa , tare da Tambayar lafiyar juna Youssouf ya É—ora da tambayar sa Leila matar sa da É—an su Imran , ?
" duk lafiya suke É—an'ouwa , Yarima kana ji na kou ?
"ina jin ka da kyau É—an'ouwa ,
" Yarima kou kana da labarin mutanen da ka baro shekarun baya a Nigeria ?
Da ace Tafeeda na gaban shi a lokacin da zai iya hango firgicin dake zane ɓaro-ɓaro bisa fuskar sa ,
"waÉ—anne mutane Tafeeda ke magana kan su ?
Tambayar da zuciyar sa ke yi ya bayyana kan harshen sa ,
Jim! Tafeeda ya yi yana nazartar firgicin da yake iya jiyowa daga Muryar Youssouf É—in ,
"wannan É—iya da tsautsayi yassa ta samu a duniya , nace kou ka sake waiwayar ta ? Tafiya ta kama ni zouwa Nigeria shine nake biÉ—ar izni kan na tai na gan ta ko da ba kai tsaye ba ne na....
Cikin sauri Youssouf ya katse sa muryar sa a É—an sama kaÉ—an ,
"Tafeeda ban ma izni ba , batun wannan É—iya ai mun jima da ajje shi ghefe kou , ka kyale kawai wani lokaci idan Allah ya ida nufi ni naje da kaina na duba ta ,
 Ajiyar zuci Tafeeda yayi ,
"tou babu kome 'dan ouwa Allah shi gwada mouna lokacin da lafiya , Allah kouma shi ƙara rufa asiri ,
'Amin Amin 'dan ouwa ,
Shiru ya gifta tsakani sakamakon tunani mai zurfi da kowannen su ya faÉ—a ,
Babu shakka Tafeeda yana da wani dalili da ya sanya shi bijiro masa da zance Mama a dai-dai wannan lokacin da tsawon shekaru wajen shidda bai taɓa tambayar sa game da lamarin ta ba sai fa yau .
a daddafe ya iya kaiwa bayan la'asar a gida , ya sake shirya Mama da ita ma duk ta damu da son su koma wajen Falmata ,
Ko da ya isa asibitin har lau bai samu damar shiga É—akin da Falmatan take ba .
Haƙuri likitar da take da Alhakin kula da ita ta bashi , akan ba zai yiwu ya shiga inda take a yau ba sai ko zuwa gobe da yammaci
Haka suka ƙaraci zama daga gefen ɗakin da take ciki har duhu ya fara shiga, dan dolen sa ya miƙe da Mama ya ƙarasa jikin ƙofar ɗakin da take ,
Ya yi mata addu'a , kafin su bar asibitin zuwa gida ,
Daren ranar bai zo masa da sauƙi ba , baki ɗaya sai juye-juye yake yi ya gaza yin baccin kirki , bai san da haka ƙaunar ta ta rarake masa zuciya ba sai da ya gaza bacci saboda damuwa da son sanin halin da take ci gami da kewar ta mai tarin yawa ,
Abunda bai taɓa jin kwatankwacin sa kan kowacce ɗiya mace ba , ko da kuwa Maimounatu ,
Salon ƙaunar da yake yiwa Fatima daban ne da yake tafe da wani irin yanayi mai tasiri sossai a gare shi ,
Sai gefen asuba bacci ya É—auke shi cike da mafarkai iri-iri , da har ya sanya shi makara wajen yin sallar asubahi .
Tara na safe suka samu isa asibitin , inda kuma cikin sa'a ya samu damar shiga ɗakin da Falmatan take ƙarƙashin jagorancin likitan ta ,
Da takun ƙafar su ta san da shigowar su ɗakin da take da ita ma ta kwana cikin kewar su duk kuwa da zogi da idon ke yi mata lokaci zuwa lokaci , amma ta fi damuwa da ta san a wanne hali Mama da Baban ta suke ?
"Mama , Maama
Suka haɗa baki wajen ƙiran sunan junan su ita da Mama wacce da shigowar ta ɗakin ta hango Falmata , ta tafi da gudun ta ,
ÆŠago ta Falmata tayi ta rungume ta a jikin ta , tana jin yadda sanyin Æ™aunar ta ke ratsa zuciyar ta , babu shakka Æ™aunar Mama magani ce ga ta ta zuciyar ,Â
Da murmushin samun nutsuwa ya ƙaraso bakin gadon ,
"Fatima yaya jikin naki ? Babu inda ke miki ciwo kou ? Baki cikin damuwa kouma ?
Waigawa tayi sashin da take jin tashin muryar sa ,
"Baban Mama ina kwana ? Yaya Mama ta kwana ? Bata yi ciwo ba ko ?Â
ÆŠan tsayirtawa tayi , kafin ta É—ora da cewa
"bana jin damuwa ko ciwo mai tsanani , amma ina son a warware min idon nawa wannan abunda suka rufe min ido da shi yana damuna ,
"likitan da duk yana jin abunda take faÉ—i tare da taimakon na'urar kunnen sa ,
Ya matsa yana sake rarrashin ta tare da yiwa Youssouf bayani kan cewa kafin su warware mata idon zuwa gobe anfi buƙatar idon ya zauna a rufe haka , har sai bayan awanni arba'in ,
A cikin É—akin suka wuni tare , sau biyu Gimbiya maimounatu na Æ™iran wayar sa , ya gaza É—aukar Æ™iran .Â
Bai san dalili ba amma can cikin ran sa ya gujewa yin hira da maimounatu ne saboda gudun ɓacin ran Falmata .
Washegari kamar yadda suka sharÉ—anta , awanni arba'in da huÉ—u da 'yan mintoci ,
Misalin ƙarfe goma na safe likitocin suka yi da'ira , a kan ta ,
Babba daga cikin su wanda kuma shine ainahin wanda ya yi mata aikin , shi ya warware mata idon ,
Bayan sassauta haske tare da sauya launin hasken zuwa marar kaifi , cike da fatan nasara likitan ya umarci Falmata da ta buÉ—e idanun ta ,
Babu karsashi ta fara wara idanun da suka mata wani irin nawi , hasken da ta ji kamar ya chaki idon shi yasa ta saurin runtse idanun ta kai tafukan ta biyu ta rufe fuskar ta ,
Cikin sauri likitar da ke gefen ta ta sauke hannunwan nata ,
Rarrashi da kalaman ƙarfafawa suka shiga yi mata cikin kwantar da murya , suna umartar ta da ta buɗe idon ta zata ga duniya ,
Sannu kan hankali ta ware idanun da suke rawa kaɗan-kaɗan , baƙon yanayi ne ya ziyarci ƙwaƙwalwa zuwa gangar jikin ta lokacin da raunanan jijiyoyin idanun ta suka fara ɗaukar jirkitattun hotuna suna aikawa da shi zuwa cikin ƙwaƙwalwarta da sauri ,
Wajen ya ɗauki shiru , likitocin suna ƙure ganin su akan ta da take gwale idon cike da burin son samun ƙarin ƙarfin ganin da tare kuma da son fahimtar abubuwan da take iya ganin hotunan su duru-duru , shin wannan shine hasken duniyar ? Haka kuma suffofin mutanen yake a zahiri ?
A sama ta tsinto muryoyin su lokacin da suka cigaba da yi mata magana , dusu-dusu take iya ganin kusantowar motsin wani abu kafin ta tsinkayi muryar likitan yana tambayar ta ko tana iya ganin alamun motsin sa ??
Bata amsa ba illa kan ta da ta gyaÉ—a ,
Hannu ya kai yana ɗaukar wani baƙin tabarau mai haɗe da 'yar na'ura na musamman wanda cikin awanni arba'in aka yi shi domin Falmata ,
Ya sanya mata a fuska tare da daidaita mata shi , ya miƙe tsaye da murmushi a fuskar sa cike da burin nasara , ya tambaye ta ko tana iya ganin sa ?
Zuba masa ido tayi tana iya ganin shatin sa fiye da É—azu , suffar sa ta mutum ta bayyana duk da ba tarwai take iya gani sa ba ,
a hankali ta juya ƙwayar idanun ta zuwa kan kome da yake sararin wajen daki-daki take ƙure musu kallo , duk da ba sosai take ganin abubuwa ba ba kuma fahimtar su take yi ba ,
A hankali likitocin suka dare , tare da bada hanya ga Youssouf da Mama da babban likitan ya yi umarnin su shigo ,
Hannun sa yana riƙe da Mama suka shigo ,
Kamar koyaushe takun Mama ya fara isa ga dodon kunnen ta ,
Dan haka take ware ido cike da buri , burin da ada ta ɗauka ta haƙura da shi ,
'yar ƙaramar halittar da ke kusantota ta ɗorawa ido ,
Ko ba'a faɗa mata ba , ko da cewa bata taɓa ganin wata halitta da idanun ta ba , ta san wannan ita ce Mama ,
" Mama ,
Mama ta ƙira sunan ta dai-dai da ƙarasowar ta gaban ta ,
Sanin da ya yi Mama bata cika lafiya ba ya sa dole ya bar asibitin tare da ita ya nufi gida da zummar dawowa zuwa anjima domin ba zai iya yin har tsawon wasu awanni masu yawa ba tare da ya gan ta ba , ya san halin da take ciki ba ,
Ko da suka dawo gida daga shi har Mama gidan bai musu daÉ—i ba ,
Mama kaɗai ya soyawa ƙwai tare da kifin gwangwani , ita ma bata wani ci na kirki ba ta ɗauke kai , Alamun ta ƙoshi ,
"Mama ki ci abinci sossai mana ,
Girgiza kai tayi tana ƙwalan-ƙwalan da ido ,
"Papa mu tafi wajen Mama yanzu ,
"zamu tafi idan kin ida cin abincin ki kin ji kou ?
Shiru tayi tana kallon sa ba tare da ta buɗe baki ta karɓi abincin da yake miƙa mata ba ,
Gajiya yayi da riƙe chokalin , ya ajiye gami da miƙewa yana jin yadda zuciyar sa ke cike da kewar ta , baki ɗayan hankalin sa na kan ta ,
Ya daÉ—e a zaune yana mata addu'a akan sallayar da ya idar da Sallar Azahar ,
Shafa kan Mama yayi wacce tayi bacci a gefen shinfiÉ—ar sallar sa ,
Cikin ran sa yana aiyana irin yawan kewar Mamar ta da tayi wanda ya duƙusar da walwalarta
ÆŠaukar ta yayi ya kaita É—aki ya kwantar tare da rufe ta da bargo , ya zauna daga bakin gadon ,
Wayar sa ya ɗauka ya latsa ƙiran layin Tafeeda da ya yi ƙiran sa a ɗazu lokacin da ake yiwa Falmata aiki , bai samu damar ɗaukar kiran nasa ba
Bayan sun gaisa , tare da Tambayar lafiyar juna Youssouf ya É—ora da tambayar sa Leila matar sa da É—an su Imran , ?
" duk lafiya suke É—an'ouwa , Yarima kana ji na kou ?
"ina jin ka da kyau É—an'ouwa ,
" Yarima kou kana da labarin mutanen da ka baro shekarun baya a Nigeria ?
Da ace Tafeeda na gaban shi a lokacin da zai iya hango firgicin dake zane ɓaro-ɓaro bisa fuskar sa ,
"waÉ—anne mutane Tafeeda ke magana kan su ?
Tambayar da zuciyar sa ke yi ya bayyana kan harshen sa ,
Jim! Tafeeda ya yi yana nazartar firgicin da yake iya jiyowa daga Muryar Youssouf É—in ,
"wannan É—iya da tsautsayi yassa ta samu a duniya , nace kou ka sake waiwayar ta ? Tafiya ta kama ni zouwa Nigeria shine nake biÉ—ar izni kan na tai na gan ta ko da ba kai tsaye ba ne na....
Cikin sauri Youssouf ya katse sa muryar sa a É—an sama kaÉ—an ,
"Tafeeda ban ma izni ba , batun wannan É—iya ai mun jima da ajje shi ghefe kou , ka kyale kawai wani lokaci idan Allah ya ida nufi ni naje da kaina na duba ta ,
 Ajiyar zuci Tafeeda yayi ,
"tou babu kome 'dan ouwa Allah shi gwada mouna lokacin da lafiya , Allah kouma shi ƙara rufa asiri ,
'Amin Amin 'dan ouwa ,
Shiru ya gifta tsakani sakamakon tunani mai zurfi da kowannen su ya faÉ—a ,
Babu shakka Tafeeda yana da wani dalili da ya sanya shi bijiro masa da zance Mama a dai-dai wannan lokacin da tsawon shekaru wajen shidda bai taɓa tambayar sa game da lamarin ta ba sai fa yau .
a daddafe ya iya kaiwa bayan la'asar a gida , ya sake shirya Mama da ita ma duk ta damu da son su koma wajen Falmata ,
Ko da ya isa asibitin har lau bai samu damar shiga É—akin da Falmatan take ba .
Haƙuri likitar da take da Alhakin kula da ita ta bashi , akan ba zai yiwu ya shiga inda take a yau ba sai ko zuwa gobe da yammaci
Haka suka ƙaraci zama daga gefen ɗakin da take ciki har duhu ya fara shiga, dan dolen sa ya miƙe da Mama ya ƙarasa jikin ƙofar ɗakin da take ,
Ya yi mata addu'a , kafin su bar asibitin zuwa gida ,
Daren ranar bai zo masa da sauƙi ba , baki ɗaya sai juye-juye yake yi ya gaza yin baccin kirki , bai san da haka ƙaunar ta ta rarake masa zuciya ba sai da ya gaza bacci saboda damuwa da son sanin halin da take ci gami da kewar ta mai tarin yawa ,
Abunda bai taɓa jin kwatankwacin sa kan kowacce ɗiya mace ba , ko da kuwa Maimounatu ,
Salon ƙaunar da yake yiwa Fatima daban ne da yake tafe da wani irin yanayi mai tasiri sossai a gare shi ,
Sai gefen asuba bacci ya É—auke shi cike da mafarkai iri-iri , da har ya sanya shi makara wajen yin sallar asubahi .
Tara na safe suka samu isa asibitin , inda kuma cikin sa'a ya samu damar shiga ɗakin da Falmatan take ƙarƙashin jagorancin likitan ta ,
Da takun ƙafar su ta san da shigowar su ɗakin da take da ita ma ta kwana cikin kewar su duk kuwa da zogi da idon ke yi mata lokaci zuwa lokaci , amma ta fi damuwa da ta san a wanne hali Mama da Baban ta suke ?
"Mama , Maama
Suka haɗa baki wajen ƙiran sunan junan su ita da Mama wacce da shigowar ta ɗakin ta hango Falmata , ta tafi da gudun ta ,
ÆŠago ta Falmata tayi ta rungume ta a jikin ta , tana jin yadda sanyin Æ™aunar ta ke ratsa zuciyar ta , babu shakka Æ™aunar Mama magani ce ga ta ta zuciyar ,Â
Da murmushin samun nutsuwa ya ƙaraso bakin gadon ,
"Fatima yaya jikin naki ? Babu inda ke miki ciwo kou ? Baki cikin damuwa kouma ?
Waigawa tayi sashin da take jin tashin muryar sa ,
"Baban Mama ina kwana ? Yaya Mama ta kwana ? Bata yi ciwo ba ko ?Â
ÆŠan tsayirtawa tayi , kafin ta É—ora da cewa
"bana jin damuwa ko ciwo mai tsanani , amma ina son a warware min idon nawa wannan abunda suka rufe min ido da shi yana damuna ,
"likitan da duk yana jin abunda take faÉ—i tare da taimakon na'urar kunnen sa ,
Ya matsa yana sake rarrashin ta tare da yiwa Youssouf bayani kan cewa kafin su warware mata idon zuwa gobe anfi buƙatar idon ya zauna a rufe haka , har sai bayan awanni arba'in ,
A cikin É—akin suka wuni tare , sau biyu Gimbiya maimounatu na Æ™iran wayar sa , ya gaza É—aukar Æ™iran .Â
Bai san dalili ba amma can cikin ran sa ya gujewa yin hira da maimounatu ne saboda gudun ɓacin ran Falmata .
Washegari kamar yadda suka sharÉ—anta , awanni arba'in da huÉ—u da 'yan mintoci ,
Misalin ƙarfe goma na safe likitocin suka yi da'ira , a kan ta ,
Babba daga cikin su wanda kuma shine ainahin wanda ya yi mata aikin , shi ya warware mata idon ,
Bayan sassauta haske tare da sauya launin hasken zuwa marar kaifi , cike da fatan nasara likitan ya umarci Falmata da ta buÉ—e idanun ta ,
Babu karsashi ta fara wara idanun da suka mata wani irin nawi , hasken da ta ji kamar ya chaki idon shi yasa ta saurin runtse idanun ta kai tafukan ta biyu ta rufe fuskar ta ,
Cikin sauri likitar da ke gefen ta ta sauke hannunwan nata ,
Rarrashi da kalaman ƙarfafawa suka shiga yi mata cikin kwantar da murya , suna umartar ta da ta buɗe idon ta zata ga duniya ,
Sannu kan hankali ta ware idanun da suke rawa kaɗan-kaɗan , baƙon yanayi ne ya ziyarci ƙwaƙwalwa zuwa gangar jikin ta lokacin da raunanan jijiyoyin idanun ta suka fara ɗaukar jirkitattun hotuna suna aikawa da shi zuwa cikin ƙwaƙwalwarta da sauri ,
Wajen ya ɗauki shiru , likitocin suna ƙure ganin su akan ta da take gwale idon cike da burin son samun ƙarin ƙarfin ganin da tare kuma da son fahimtar abubuwan da take iya ganin hotunan su duru-duru , shin wannan shine hasken duniyar ? Haka kuma suffofin mutanen yake a zahiri ?
A sama ta tsinto muryoyin su lokacin da suka cigaba da yi mata magana , dusu-dusu take iya ganin kusantowar motsin wani abu kafin ta tsinkayi muryar likitan yana tambayar ta ko tana iya ganin alamun motsin sa ??
Bata amsa ba illa kan ta da ta gyaÉ—a ,
Hannu ya kai yana ɗaukar wani baƙin tabarau mai haɗe da 'yar na'ura na musamman wanda cikin awanni arba'in aka yi shi domin Falmata ,
Ya sanya mata a fuska tare da daidaita mata shi , ya miƙe tsaye da murmushi a fuskar sa cike da burin nasara , ya tambaye ta ko tana iya ganin sa ?
Zuba masa ido tayi tana iya ganin shatin sa fiye da É—azu , suffar sa ta mutum ta bayyana duk da ba tarwai take iya gani sa ba ,
a hankali ta juya ƙwayar idanun ta zuwa kan kome da yake sararin wajen daki-daki take ƙure musu kallo , duk da ba sosai take ganin abubuwa ba ba kuma fahimtar su take yi ba ,
A hankali likitocin suka dare , tare da bada hanya ga Youssouf da Mama da babban likitan ya yi umarnin su shigo ,
Hannun sa yana riƙe da Mama suka shigo ,
Kamar koyaushe takun Mama ya fara isa ga dodon kunnen ta ,
Dan haka take ware ido cike da buri , burin da ada ta ɗauka ta haƙura da shi ,
'yar ƙaramar halittar da ke kusantota ta ɗorawa ido ,
Ko ba'a faɗa mata ba , ko da cewa bata taɓa ganin wata halitta da idanun ta ba , ta san wannan ita ce Mama ,
" Mama ,
Mama ta ƙira sunan ta dai-dai da ƙarasowar ta gaban ta ,