Sashe 185
Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin dare bacci ya ƙauracewa idanun Youssouf tunaninnika sun masa yawa , yana son ya san halin da Mama ke ciki yasan kashe wayar da yayi ma a halin yanzu kuskurene tunda yana da marar lafiya a asibiti ,
Dan haka ya miƙe zaune ya ɗau wayarsa tare da kunna ta , kan layin Hajja ya danna ƙira yana kallon agogo wayar da ya gwada masa ƙarfe ɗaya saura mintuna biyar ,
Yasan cewa dare yayi sosai amma ya zama dole ya san halin da É—iyar sa ke ciki tun bayan barin su wajen ta , da kuma yadda zata kwana ,
A can wayar ta ɗau ƙara , yaji alamun shigar ƙiran ,
Muryar da ta doki kunnuwan sa ya sanya shi miƙewa tsaye , yayi taku kaɗan , yana waiwayen Falmata ,
" Mai wayar tana bacci ,
  cewar Yakaka da ita ta ɗau wayar Hajja saboda ƙarar wayar kar ya tayar da Mama da ta samu bacci da kyar bayan kukan ciwo da take yi , tare da rikicin neman Iyayenta .
 " Yaya jikin Mama ?
Yace , yana fitowa daga É—akin zuwa falo domin kada ya tayar da Falmata daga bacci ,
Miƙewa tayi daga kujerar da take kai , tana jin tsanar sa na sake bijiro mata da jin sautin muryar sa ,
" Youssouf
  Ta ƙira shi , bata sauƙe mumfashi ba ta ɗora da cewa , "ina batun mu ? Kar ka manta da abunda na faɗa maka muddin kana son cigaba da ganin farin-cikin iyayen ka sannan....
Katse ta yayi ,
" yaya jikin É—iya ta nake tambayar ki ? Ke baki da tounani ne ? Baki ganin halin da Mama take ciki ? Ba yanzou bane lokacin yin wannan maganar kiyi hakuri don Allah .
" Yanzou ki tada Hajja daga barci ki bata wayar zan tambaye ta kan lafiyar ɗiya ta ,
Ƙit !
Yakaka ta kashe wayar har ita yake ƙira marar tunani ? Akwai marar tunani da ya wuce shi ? Duk sanadin waye suke cikin halin da suke ciki a yanzu ? Da bata haɗu da shi ba zata haifi Mama ne ? Ko kuwa yana nufin shi da ya gudu ya barta da cikin Mama ya fita ƙaunar Mama ɗin ne ? Yana da sani ne ko kaɗan akan irin wahalar da ta shiga na kwana a rumfar kasuwa tare da cikin Mama a jikinta ?
Guntun tsaki tayi tana komawa ta zauna a kujerar da ta tashi ,
 ta shafa kan Mama wacce take baccin zoma tana ɗan nishi kaɗan-kaɗan , duk da cewa an ƙara mata jini leda guda amma har yanzu ƙafa da hannunta fari sol alamun rashin jini
tausayinta yana sake kama ta , ko runtse bata runtsa ba , tun lokacin da Hajja ta faÉ—a mata cikin jikin Falmata damuwarta ta sake ninkuwa ,
Duk dogon nazarin nema mafita da tayi hankalinta yaƙi amincewa da ta ƙyale Youssouf ya cigaba da zama da ƙanwar ta ta gwammace ya saki Falmata su koma Nigeria tayi rainon cikin ta haihu idan yaso su ɗauko abunda aka haifa a kaiwa iyayensa tunda shi da Falmata aure suka yi ,
Dole iyayensa zasu riƙe abunda ta haifa , ita kuwa Mama 'ƴar ta ce da suka haifa ba tare da aure ba ta san iyayensa baza su riƙe Mama ba , Mama zata kasance tare da ita .
**
Youssouf ya ji yadda ta katse ƙiran ba tare da ta bashi amsar da yake son ji ba , sauƙe wayar yayi bai sake ƙira ba ya juya ya koma ɗakin ,
Zama yayi a bakin gado , cikin ransa rikicin da Yakaka ta zo da shi ya kai matakin ƙure shi, ya fara neman mafitar yaya zai yi da Yakaka domin kuwa ko a mafarki ba zai yi mata yadda take so ba , ya saki Matarsa akan wanne dalili ? Aurensa da Falmata aurene da sai mutuwa ce kaɗai zata raba su ,
Yana son matar sa , yana ƙaunar ta ,yana tausayin ta , ya kuma shirya tsaf domin zamar mata bango abun jingina , idan ya rabu da ita taje ina ? Waye zai jiɓanci lamarin ta ? Wa suke da shi a duniya jigo ? Daga ita har Yakaka masu rauni ne domin kuwa mata ne tayaya zai sau aurenta ? Alhalin ga zuri'a a tsakani Allah ya fara basu ,
dangantakar su ba mai yankewa bace har abada ba zai rabu da ita ba ko da kuwa ace ita da karan kanta ta nemi da ya sake ta ba zai aikata hakan ba ,
bare wasu mutane daban da ba sune suke riƙe masa da igiyoyin auren sa ba , Fatima Zara matar sa ce har a lahira baya fatan rabuwar su .
Zai roƙi Yakaka da tayi hakuri ta yafe masa duk wani laifi da take zaton ya yi mata , tare da Alƙawarin kula da hidimar Rayuwar ta muddin zata yadda ta cigaba da rufe asirin tsakanin su daga sauran mutane , ciki har da Falmata da Mama idan ta girma .
sannan tayi haƙuri ta koma Nigeria ta samu miji tayi aure shi zai tsaya mata a wannan gaɓar .
muddin kuwa taƙi yadda da tayin salama , bai iya hasashen yadda ƙarshen lamarin su zai ƙarƙare , bai san ba gurin hukuntata akan yunƙurinta na raba shi da matar sa ko zai iya yi mata sassauci Albarkacin Mama ba?
abunda ya riga ya sani ne tun a ranar farkon ganin sa da ita ba soyayya ce ragamar tarayyar su ba illa musiba tare da sharrin shaiÉ—an da shi ya faÉ—awa a ciki , ita kuma ta gagara tsamo sa a madadin haka ma sai ta zama abokiyar taya shi ,ashe idan haka ne itama da nata laifin ,
Zai yi kome zai kuma jure kome domin ganin ya cigaba da rayuwa da matar sa da 'ya'yan sa ,
A hankali ya hau gadon ya rungume ta tsam a jikinsa , runtse ido tayi hawayen da suka taru mata suka zubo , tun daga tashin sa ta ji shi , ta ji wayar sa da Yakaka ,
Wanne irin sirri ne a tsakanin su da suke ɓoye mata basa so ta ji ? Jikinta yana bata rabuwar su da ita da Youssouf ta zo kusa.
Washegari
Tunda tayi sallar asuba gari yayi haske ta shiga kitchen duk kuwa da Youssouf ya so hana ta amma ta dage ,
"bai kyautu ba kuma Hajja ta dawo daga asibiti tayi mana girki zan iya ba abu mai wahala zan dafa ba kawai pasta ne zan yi , tace da shi .
Ba yadda ya iya saboda gaba ɗaya ta koma mishi kamar farkon auren su , sai janye jiki take da shi ,tana ƙin kallon sa , bata tsawaita zance da shi
Bayan ta gama girkin ta zuba ta rufe , ta zo ta wuce shi a falon yana zaune ba tare da tace masa kome ba ,
Da ta shiga ɗaki wanka tayi ta koma ta kwanta a gadon ta saboda tun ƙarfe ɗayan dare rabon ta da baccin kirki , lokacin da ta ji wayar da suka yi , tana kwanciya bata daɗe ba bacci ya ɗauke ta
Youssouf da ya gaji da jiranta ta zo suyi karin kumallo , tashi yayi ya leƙa ɗakin nata ,
A gado ya hangota tayi luf tana baccin ta , ransa yayi sanyi da yaga tana bacci sosai haka , a hankali ya taka zuwa cikin É—akin ,
Zama yayi a bakin gadon yana ƙarewa fuskarta kallo , ƙaunar ta na sake fisgar shi , gani yayi ta fi yi masa kyau idan tana bacci ,
Kamar motsi ya ji an taɓa ƙofar falon , dan haka ya miƙe ya fito yana dube-dube , sai dai bai kai ga ganin kome ba , tsayuwa ya cigaba da yi a harabar gidan ya zura hannu a aljihu yana tunanin zuci ,
"yana son zuwa Maraɗi ko domin iyayensa , amma tsoron abunda zai tarar a can ya hana shi samun ƙarfin zuwa ,
Ciki ya koma inda ya tarar wayar sa da ya ajiye akan kujerar da ya tashi tana ƙara ,
Zuciyar sa ta buga da ƙarfi ganin Mai ƙiran nasa da ba kasafai ta cika yin ƙiran waya ba , sai fa da Babban dalili ko kuma idan shi ya ƙira domin gaishe ta ,
"Adda Ammi ce Babbar yayar su baki É—aya da take aure a jahar Damagaram ,
Har wayar ta tsinke bai ɗauka ba saboda fargaba , amma bai jinkirta ba ya bi bayan ƙiran da hanzari ,
**
Daga cikin motar ƙirar Honda Accord da take tafiya da matsakaicin gudu akan titin Boulevard Mali Véro ,
Hamshaƙan matan su biyu masu kamanni ɗaya suke zaune , ɗaya tana daga gaba Babbar tana baya , ta gaban ta ɗan waiga kaɗan , lokacin da direban ya karya kan motar zuwa cikin unguwar da take gefe da su ,
"Adda Ammi kadda kice mini ke ma Youssoufa bai ɗau ƙiran ki ba ?
Zata yi magana wayar ta ta É—au kiÉ—an shigowar kiran sa ,
" ga shi ya biyo sawun ƙiran ,
  Tace ba tare da ta ɗaga ƙiran ba ,
Tafeeda wanda shi yake jaan motar ya juyo kaɗan kafin ya maida hankalin sa ga tuƙin yana cewa "ai ga gidan can ma mun iso Adda Ammi ,
Duk suka zubawa gidan ido ta cikin gilashin motar suna kallo ,bayan ya dai-daita tsayuwar motar , suna shirin fitowa lokacin da suka ga an buɗo ta ƙaramar ƙofar gidan a hankali an fito ,
Su dukkanin su wara ido suka yi suna kallon sa da Mamaki ,
" Mouhammadou ?
Tafeeda ya ƙira sunan sa da mamaki a muryar sa ,
suna ganin yadda yake dube-dube yana sauri , ya miƙa kan titin unguwar da babu kowa shal , sai fa giftawar motoci jifa-jifa , ba tare da shi ya gan su ba saboda gilashin motar da yake da duhu ,
Shiru ne ya gifta tsakanin su , kafin Ubbo ta ce
Dan haka ya miƙe zaune ya ɗau wayarsa tare da kunna ta , kan layin Hajja ya danna ƙira yana kallon agogo wayar da ya gwada masa ƙarfe ɗaya saura mintuna biyar ,
Yasan cewa dare yayi sosai amma ya zama dole ya san halin da É—iyar sa ke ciki tun bayan barin su wajen ta , da kuma yadda zata kwana ,
A can wayar ta ɗau ƙara , yaji alamun shigar ƙiran ,
Muryar da ta doki kunnuwan sa ya sanya shi miƙewa tsaye , yayi taku kaɗan , yana waiwayen Falmata ,
" Mai wayar tana bacci ,
  cewar Yakaka da ita ta ɗau wayar Hajja saboda ƙarar wayar kar ya tayar da Mama da ta samu bacci da kyar bayan kukan ciwo da take yi , tare da rikicin neman Iyayenta .
 " Yaya jikin Mama ?
Yace , yana fitowa daga É—akin zuwa falo domin kada ya tayar da Falmata daga bacci ,
Miƙewa tayi daga kujerar da take kai , tana jin tsanar sa na sake bijiro mata da jin sautin muryar sa ,
" Youssouf
  Ta ƙira shi , bata sauƙe mumfashi ba ta ɗora da cewa , "ina batun mu ? Kar ka manta da abunda na faɗa maka muddin kana son cigaba da ganin farin-cikin iyayen ka sannan....
Katse ta yayi ,
" yaya jikin É—iya ta nake tambayar ki ? Ke baki da tounani ne ? Baki ganin halin da Mama take ciki ? Ba yanzou bane lokacin yin wannan maganar kiyi hakuri don Allah .
" Yanzou ki tada Hajja daga barci ki bata wayar zan tambaye ta kan lafiyar ɗiya ta ,
Ƙit !
Yakaka ta kashe wayar har ita yake ƙira marar tunani ? Akwai marar tunani da ya wuce shi ? Duk sanadin waye suke cikin halin da suke ciki a yanzu ? Da bata haɗu da shi ba zata haifi Mama ne ? Ko kuwa yana nufin shi da ya gudu ya barta da cikin Mama ya fita ƙaunar Mama ɗin ne ? Yana da sani ne ko kaɗan akan irin wahalar da ta shiga na kwana a rumfar kasuwa tare da cikin Mama a jikinta ?
Guntun tsaki tayi tana komawa ta zauna a kujerar da ta tashi ,
 ta shafa kan Mama wacce take baccin zoma tana ɗan nishi kaɗan-kaɗan , duk da cewa an ƙara mata jini leda guda amma har yanzu ƙafa da hannunta fari sol alamun rashin jini
tausayinta yana sake kama ta , ko runtse bata runtsa ba , tun lokacin da Hajja ta faÉ—a mata cikin jikin Falmata damuwarta ta sake ninkuwa ,
Duk dogon nazarin nema mafita da tayi hankalinta yaƙi amincewa da ta ƙyale Youssouf ya cigaba da zama da ƙanwar ta ta gwammace ya saki Falmata su koma Nigeria tayi rainon cikin ta haihu idan yaso su ɗauko abunda aka haifa a kaiwa iyayensa tunda shi da Falmata aure suka yi ,
Dole iyayensa zasu riƙe abunda ta haifa , ita kuwa Mama 'ƴar ta ce da suka haifa ba tare da aure ba ta san iyayensa baza su riƙe Mama ba , Mama zata kasance tare da ita .
**
Youssouf ya ji yadda ta katse ƙiran ba tare da ta bashi amsar da yake son ji ba , sauƙe wayar yayi bai sake ƙira ba ya juya ya koma ɗakin ,
Zama yayi a bakin gado , cikin ransa rikicin da Yakaka ta zo da shi ya kai matakin ƙure shi, ya fara neman mafitar yaya zai yi da Yakaka domin kuwa ko a mafarki ba zai yi mata yadda take so ba , ya saki Matarsa akan wanne dalili ? Aurensa da Falmata aurene da sai mutuwa ce kaɗai zata raba su ,
Yana son matar sa , yana ƙaunar ta ,yana tausayin ta , ya kuma shirya tsaf domin zamar mata bango abun jingina , idan ya rabu da ita taje ina ? Waye zai jiɓanci lamarin ta ? Wa suke da shi a duniya jigo ? Daga ita har Yakaka masu rauni ne domin kuwa mata ne tayaya zai sau aurenta ? Alhalin ga zuri'a a tsakani Allah ya fara basu ,
dangantakar su ba mai yankewa bace har abada ba zai rabu da ita ba ko da kuwa ace ita da karan kanta ta nemi da ya sake ta ba zai aikata hakan ba ,
bare wasu mutane daban da ba sune suke riƙe masa da igiyoyin auren sa ba , Fatima Zara matar sa ce har a lahira baya fatan rabuwar su .
Zai roƙi Yakaka da tayi hakuri ta yafe masa duk wani laifi da take zaton ya yi mata , tare da Alƙawarin kula da hidimar Rayuwar ta muddin zata yadda ta cigaba da rufe asirin tsakanin su daga sauran mutane , ciki har da Falmata da Mama idan ta girma .
sannan tayi haƙuri ta koma Nigeria ta samu miji tayi aure shi zai tsaya mata a wannan gaɓar .
muddin kuwa taƙi yadda da tayin salama , bai iya hasashen yadda ƙarshen lamarin su zai ƙarƙare , bai san ba gurin hukuntata akan yunƙurinta na raba shi da matar sa ko zai iya yi mata sassauci Albarkacin Mama ba?
abunda ya riga ya sani ne tun a ranar farkon ganin sa da ita ba soyayya ce ragamar tarayyar su ba illa musiba tare da sharrin shaiÉ—an da shi ya faÉ—awa a ciki , ita kuma ta gagara tsamo sa a madadin haka ma sai ta zama abokiyar taya shi ,ashe idan haka ne itama da nata laifin ,
Zai yi kome zai kuma jure kome domin ganin ya cigaba da rayuwa da matar sa da 'ya'yan sa ,
A hankali ya hau gadon ya rungume ta tsam a jikinsa , runtse ido tayi hawayen da suka taru mata suka zubo , tun daga tashin sa ta ji shi , ta ji wayar sa da Yakaka ,
Wanne irin sirri ne a tsakanin su da suke ɓoye mata basa so ta ji ? Jikinta yana bata rabuwar su da ita da Youssouf ta zo kusa.
Washegari
Tunda tayi sallar asuba gari yayi haske ta shiga kitchen duk kuwa da Youssouf ya so hana ta amma ta dage ,
"bai kyautu ba kuma Hajja ta dawo daga asibiti tayi mana girki zan iya ba abu mai wahala zan dafa ba kawai pasta ne zan yi , tace da shi .
Ba yadda ya iya saboda gaba ɗaya ta koma mishi kamar farkon auren su , sai janye jiki take da shi ,tana ƙin kallon sa , bata tsawaita zance da shi
Bayan ta gama girkin ta zuba ta rufe , ta zo ta wuce shi a falon yana zaune ba tare da tace masa kome ba ,
Da ta shiga ɗaki wanka tayi ta koma ta kwanta a gadon ta saboda tun ƙarfe ɗayan dare rabon ta da baccin kirki , lokacin da ta ji wayar da suka yi , tana kwanciya bata daɗe ba bacci ya ɗauke ta
Youssouf da ya gaji da jiranta ta zo suyi karin kumallo , tashi yayi ya leƙa ɗakin nata ,
A gado ya hangota tayi luf tana baccin ta , ransa yayi sanyi da yaga tana bacci sosai haka , a hankali ya taka zuwa cikin É—akin ,
Zama yayi a bakin gadon yana ƙarewa fuskarta kallo , ƙaunar ta na sake fisgar shi , gani yayi ta fi yi masa kyau idan tana bacci ,
Kamar motsi ya ji an taɓa ƙofar falon , dan haka ya miƙe ya fito yana dube-dube , sai dai bai kai ga ganin kome ba , tsayuwa ya cigaba da yi a harabar gidan ya zura hannu a aljihu yana tunanin zuci ,
"yana son zuwa Maraɗi ko domin iyayensa , amma tsoron abunda zai tarar a can ya hana shi samun ƙarfin zuwa ,
Ciki ya koma inda ya tarar wayar sa da ya ajiye akan kujerar da ya tashi tana ƙara ,
Zuciyar sa ta buga da ƙarfi ganin Mai ƙiran nasa da ba kasafai ta cika yin ƙiran waya ba , sai fa da Babban dalili ko kuma idan shi ya ƙira domin gaishe ta ,
"Adda Ammi ce Babbar yayar su baki É—aya da take aure a jahar Damagaram ,
Har wayar ta tsinke bai ɗauka ba saboda fargaba , amma bai jinkirta ba ya bi bayan ƙiran da hanzari ,
**
Daga cikin motar ƙirar Honda Accord da take tafiya da matsakaicin gudu akan titin Boulevard Mali Véro ,
Hamshaƙan matan su biyu masu kamanni ɗaya suke zaune , ɗaya tana daga gaba Babbar tana baya , ta gaban ta ɗan waiga kaɗan , lokacin da direban ya karya kan motar zuwa cikin unguwar da take gefe da su ,
"Adda Ammi kadda kice mini ke ma Youssoufa bai ɗau ƙiran ki ba ?
Zata yi magana wayar ta ta É—au kiÉ—an shigowar kiran sa ,
" ga shi ya biyo sawun ƙiran ,
  Tace ba tare da ta ɗaga ƙiran ba ,
Tafeeda wanda shi yake jaan motar ya juyo kaɗan kafin ya maida hankalin sa ga tuƙin yana cewa "ai ga gidan can ma mun iso Adda Ammi ,
Duk suka zubawa gidan ido ta cikin gilashin motar suna kallo ,bayan ya dai-daita tsayuwar motar , suna shirin fitowa lokacin da suka ga an buɗo ta ƙaramar ƙofar gidan a hankali an fito ,
Su dukkanin su wara ido suka yi suna kallon sa da Mamaki ,
" Mouhammadou ?
Tafeeda ya ƙira sunan sa da mamaki a muryar sa ,
suna ganin yadda yake dube-dube yana sauri , ya miƙa kan titin unguwar da babu kowa shal , sai fa giftawar motoci jifa-jifa , ba tare da shi ya gan su ba saboda gilashin motar da yake da duhu ,
Shiru ne ya gifta tsakanin su , kafin Ubbo ta ce