Sashe 218
Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hafsa da zainab da duk abunda Hajja ke cewa daga ɗaki suna jin ta sarai saboda sama-sama take maganar sai suka haɗa ido kafin su duka ukun su kwashe da dariya , Falmata ma sai da ta ɗan dara , a ran ta tana aiyana wannan kaɗan ne daga halin Hajja , yadda aka san bata da wani aiki sai na faɗin yadda mace za ta farantawa miji Ho Hajja , ya dace a bawa Hajja shugabantar wata ƙungiya ta faɗakar da mata kan yadda ake tafiyar da Miji .
Hafsa ita ta rage dariyar ganin yayan su na tsaye yana kallon su , ita ma sai ta ɗan ɗaga murya lokacin da take miƙewa tsaye tace , "Ƙanwata Amarya ki fito kuyi sallama big bro zai tafi idan kuma ma mu kike jin kunya , kun ga ku zo mu bar wajen tace da sauran 'yan uwan ta , nan take suka miƙe suka yi ɗaki suna ƴar dariya tare da sake yiwa yayan su fatan Allah kiyaye hanya ,
Doctor Hamza da yake tsaye hannun sa a zube cikin Aljihun rigar rigar jumfa jikin sa , ya ɗan gyaɗa musu kai da murmushi a fuskar sa , shi ɗaya ne ƙwal ya rage a falon .
Ganin sa ya mayar kan ƙofar ɗakin Hajja lokacin da Yakaka ta buɗo ƙofar ta fito kan ta a ƙasa fuskar ta kadaran-kadahan , ɗan matsawa kaɗan tayi ta bayan kujerar falon ta ɗan durkusa , " ina yini yaya dakta ,
Bata jira ya amsa ba ta ƙara da cewa " Allah ya kiyaye hanya ,
Bata yarda ta dubi sashin da yake ba bare ta san cewa ya matso kusan ta sai da ta miƙe tana shirin wucewa ta shige ɗakin su da yake kusa da ita , sai kawai ta ji ya riƙo hannun ta ,
A hankali ya jawo ta ya kusan haɗe jikin su , hannuwan sa yasa ya kewaye kunkumin ta , yana kallon fuskar ta da taƙi yadda ta ɗago kai , muryar sa ƙasa-ƙasa yace " haka ake yin sallama ? Babu addu'a ? Baki ji Hajja tace ki min abunda zai bani kuzari bane ?
Da sauri ta ɗago kai , signal ya mata da duk girar idanunsa biyu , yana 'yar dariya da fararen haƙoran sa da suke da kyau sosai akan fuskar sa mai rangwamen haske .
ÆŠauke kai Yakaka tayi gefe can cikin ranta tana mamakin meyasa ta hango kamar sauyin mu'amala a tare da shi daga jiya zuwa yau ? muryar ta cikin sanyin tace " ai nace Allah ya kiyaye hanya na yi addu'a ,
Hannun yasa ya sake juyo da fuskar ta saitin sa , ya zarce da sanya É—an yatsan sa ya shafa saman idon ta , da yasa Yakaka ta lumshe idanun ta da sauri , " Ya idanun ki sun wuce ko ? Basu sake damun ki ba ko ? Ya tambaye ta da ragwan sauti ,
gyaɗa kan ta tayi tana ƙoƙarin kautar da fuskar ta , amma ya ƙi bata damar haka sai ma hannuwan sa duk biyu da yasa ya tallafi fuskar ta yana shafa kumatun ta masu taushi yace ," to ina saurarar ki ki min Duas kuma ki min abunda Hajja tace ki min , ko bakya so na samu kuzarin tuƙin ne ?
Sallamar wata baƙuwa ya sa Yakaka ta fisge jikin ta da ƙarfi da daman baki ɗaya a takure take damar gudu take ta son samu ,
Sai dai bai bata damar gudun ba ya riƙe hannun ta lokacin da suke gaisawa da matar ya san ta ɗaya daga cikin mutanen Amnee ce , ta zauna akan kujera.
" Ba za ki min Duas É—in ? ba yace yana jaan hannun Yakaka su fice daga falon , babu yadda ta iya ta bi shi sai dai suna fitowa suka hango Amnee na tahowa daga sashin Baa ,
" Yaa Doctor Allah ya kiyaye hanya ya kai ka lafiya , ya kare ka , ta harhaɗo kalmomin cikin sauri tana ƙoƙarin kwace hannun ta daga cikin nasa , kafin ƙarasowar Amnee ya sake ta da sauri ta taka tana komawa ciki , da murmushi ya bi bayan ta da kallo wani irin nishaɗi ne mai daɗi yake huɗa shi .
Ƙarfe uku ya ɗau hanyar Abuja tare da sofiya wacce ya biya gidan su ya ɗauke ta dole bayan ya mata jaan ido tare da barazanar barin ta ta cigaba da zama a gidan su na wasu kwanaki da take son yi dai-dai yake da rabuwar su baki ɗaya , jin haka ba shiri ta tattaro ƴan kayan ta ta bi shi, ba tare da ta kula Momy kori sun yi wata sallamar kirki ba saboda haushin ta da momy kori take ji .
ASSALAM ALAIKUM MASU KARATU DA FATAN KUNA LAFIYA ?
INA GODIYA DA YADDA DAI HAR KULLUM KUKE HAƘURI DA NI .
INSHA ALLAH SHAFI NA GABA SHINE ƘARSHEN LITTAFIN MHR DA ZAI BIYO BAYA NAN BA DA JIMAWA BA.
NAGODE
[1/17, 9:40 PM] +234 706 503 6187: MAFARI
( Hargitsin Rayuwa)
Umm'muaz
49
MARADI-NIGER
Kwanakin da suka biyo bayan bayyanuwar mummunan aikin da Gimbiya maimounatou ta aikatawa Biyamuradi Youssouf , tare da sa hannun Mammadou da Hajiya Mama ,
Masarautar maraÉ—i ta kasance cikin alhini mai tarin yawa , kusan kullum aka yi zaman fada da Waziri ne ke jagoranta ba'a da wani batu da ya wuce na sake tattaunawa kan wannan mummunan lamari haÉ—i da yiwa Biyamuradi Addu'ar samun lafiya tare da fatan dawowar Maimartaba .
Da har yau da suke cika kwanaki ishirin da ɗaya basu baro india ba , Amma ana saka ran dawowar tasu a yau ko gobe saboda saƙon yiwuwar dawowar tasu ya iso musu .
Akwai labari daga majiya mai tushe cewar gimbiya Siyama tare da ƙanin Biyamuradi Youssouf , 'Bilal wanda shine mai binsa a haihuwa sun fara shirin tafiya India domin cigaba da jinyar sa da har kawo yau babu wanda yasan takamaimai a halin da lafiyar Youssouf ɗin ke ciki .
Ta ɓangaren Hajiya Mama kuwa duk yadda ta kai ga sanyawa idanun ta toka ta mustsiƙe ta cigaba da yin harkokin ta yadda ta saba , amma ta gagara domin yadda labarin sa hannunta da na ɗan ta wajen yunƙurin kisan da Matar Biyamuradi tayi masa , ya bazu ba a bakin bayu da hadiman cikin masarautar Maradi kaɗai ba har jama'ar gari da na wasu jahohin labari ya kai musu .
Ake kuma kucin-cina labarin tare da sake liƙa masa baƙaƙen sassa ana sake munana sa ba ƙaramin tasiri hakan yayi wajen kassara mata duk wani karsashi haɗi da ɗagawar da take tinƙaho da shi na kasancewar ta matar Sarki .
Dan haka gaba ɗaya sai take neman zama mujiya , tsarguwa take da irin kallon da bayun gidan suke mata , gefe guda ga dumuwowi birjik da suka mata ƙawanya , wanda bata saba shiga makamantan su ba , mafi girman su halin da ɗan ta tilo namiji yake ciki wanda yake tamkar ga ƙoshi ga kwana yunwa a wajen ta , domin kuwa tasan muddin Youssouf ya rasa ransa, cikin hakan akwai yiwuwar shima Mammadou ayi masa huƙunci mai tsauri da ka iya kawo ƙarshen shima tasa rayuwar .
Ga Maimartaba da bata san matsayin ta takamaimai a wajen sa ba , bayan tonon sililin da Maimounatou tayi mata a gaban sa , gefe guda kuma ga Mairamar sarki da take autar ta sannan mafi soyuwa a wajenta cikin 'ya'ya da tun bayan faruwar wannan lamarin da ta samu labarin kome bayan kuka bata wani taɓuka abun kirki ,
Rufe kanta take a ɗakin ta da yake sashin uwar-riƙon ta , ( Hajiya Umma ) ta ci kuka ,domin lamarin ya mata tsauri wajen ɗauka duka biyu a lokaci guda ,
dan kuwa bayan kasantuwar Youssouf yayan ta mafi kusanci da yawan ƙauna a tsakanin su fiye da duk sauran 'yan uwan ta , ta shaƙu da shi tunda ta buɗi ido ta ga kanta riƙe a hannuwan sa , shiga hatsarin rasa shi ba abune mai sauƙi a wajen ta ba .
Damuwar ta tana sake hauhawa da hango rugujewar zancen auren ta , tare da ma guntilewar alaƙar su ita da masoyinta da suka ɗibi tsawon shekaru uku suna soyayya wanda yake yaya ne ga gimbiya Maimounatou , uwa ɗaya uba ɗaya gaf ma ake da yanke ranar auren su cikin watannin gaba kaɗan a sha biki , sai ga shi wannan mummunan lamarin ya shata layi a tsakanin su , domin kuwa ko ba'a sanar da ita ba ta san makomar soyayyar su ita da Khaalifa , sannan tun kafin a hana ta ita ya kamata ta fara zare soyayyar sa daga ran ta , bayan abunda ƙanwar sa ta aikata ga Biyamuradi ai babu wani sauran alaƙa mai girma da zai sake shiga tsakanin masarautun nasu biyu .
Ba tun yau ba ta riga ta san wasu daga cikin munanan halayen Mahaifiyar su da ita koyaushe huɗubar ta tare da yunƙurin ta bai wuce na ganin ta raba kyakkyawar alaƙar da ke tsakanin ta da uwar-goyon ta tare da sauran ƴan uwan ta da suka haɗa uba ɗaya ba ,
da ita kuma ko kusa bata ganin aibun su , sannan duk wasu laifuka nasu da hajiya Mama ke faɗin sun aikata ko suna kan aikatawa , ita bata kai ga kama su da ko guda ba dan haka koyaushe take biris da huɗubar ta , tare da toshe kunnuwan ta , ƙaunar ƴan uwanta a jinin ta yake tana ƙaunar su kwatankwacin ƙauna tare da zallar kulawa da su ma suke nuna mata a matsayin ta na ƙaramar ƙanwar su ,
ga hajiya Umma kuwa ba zata ce kome ba da ya wuce fatan alheri tare da godiya ,riƙo ta mata na haƙiƙa ba irin riƙon ƴar kishiya ba , dan haka take jinta basu da wata maraba da Hajiya Mama , sau dayawa ma tafi kusanci da Hajiya Umma akan ita Hajiya Mama ,( goyo guba )
Hafsa ita ta rage dariyar ganin yayan su na tsaye yana kallon su , ita ma sai ta ɗan ɗaga murya lokacin da take miƙewa tsaye tace , "Ƙanwata Amarya ki fito kuyi sallama big bro zai tafi idan kuma ma mu kike jin kunya , kun ga ku zo mu bar wajen tace da sauran 'yan uwan ta , nan take suka miƙe suka yi ɗaki suna ƴar dariya tare da sake yiwa yayan su fatan Allah kiyaye hanya ,
Doctor Hamza da yake tsaye hannun sa a zube cikin Aljihun rigar rigar jumfa jikin sa , ya ɗan gyaɗa musu kai da murmushi a fuskar sa , shi ɗaya ne ƙwal ya rage a falon .
Ganin sa ya mayar kan ƙofar ɗakin Hajja lokacin da Yakaka ta buɗo ƙofar ta fito kan ta a ƙasa fuskar ta kadaran-kadahan , ɗan matsawa kaɗan tayi ta bayan kujerar falon ta ɗan durkusa , " ina yini yaya dakta ,
Bata jira ya amsa ba ta ƙara da cewa " Allah ya kiyaye hanya ,
Bata yarda ta dubi sashin da yake ba bare ta san cewa ya matso kusan ta sai da ta miƙe tana shirin wucewa ta shige ɗakin su da yake kusa da ita , sai kawai ta ji ya riƙo hannun ta ,
A hankali ya jawo ta ya kusan haɗe jikin su , hannuwan sa yasa ya kewaye kunkumin ta , yana kallon fuskar ta da taƙi yadda ta ɗago kai , muryar sa ƙasa-ƙasa yace " haka ake yin sallama ? Babu addu'a ? Baki ji Hajja tace ki min abunda zai bani kuzari bane ?
Da sauri ta ɗago kai , signal ya mata da duk girar idanunsa biyu , yana 'yar dariya da fararen haƙoran sa da suke da kyau sosai akan fuskar sa mai rangwamen haske .
ÆŠauke kai Yakaka tayi gefe can cikin ranta tana mamakin meyasa ta hango kamar sauyin mu'amala a tare da shi daga jiya zuwa yau ? muryar ta cikin sanyin tace " ai nace Allah ya kiyaye hanya na yi addu'a ,
Hannun yasa ya sake juyo da fuskar ta saitin sa , ya zarce da sanya É—an yatsan sa ya shafa saman idon ta , da yasa Yakaka ta lumshe idanun ta da sauri , " Ya idanun ki sun wuce ko ? Basu sake damun ki ba ko ? Ya tambaye ta da ragwan sauti ,
gyaɗa kan ta tayi tana ƙoƙarin kautar da fuskar ta , amma ya ƙi bata damar haka sai ma hannuwan sa duk biyu da yasa ya tallafi fuskar ta yana shafa kumatun ta masu taushi yace ," to ina saurarar ki ki min Duas kuma ki min abunda Hajja tace ki min , ko bakya so na samu kuzarin tuƙin ne ?
Sallamar wata baƙuwa ya sa Yakaka ta fisge jikin ta da ƙarfi da daman baki ɗaya a takure take damar gudu take ta son samu ,
Sai dai bai bata damar gudun ba ya riƙe hannun ta lokacin da suke gaisawa da matar ya san ta ɗaya daga cikin mutanen Amnee ce , ta zauna akan kujera.
" Ba za ki min Duas É—in ? ba yace yana jaan hannun Yakaka su fice daga falon , babu yadda ta iya ta bi shi sai dai suna fitowa suka hango Amnee na tahowa daga sashin Baa ,
" Yaa Doctor Allah ya kiyaye hanya ya kai ka lafiya , ya kare ka , ta harhaɗo kalmomin cikin sauri tana ƙoƙarin kwace hannun ta daga cikin nasa , kafin ƙarasowar Amnee ya sake ta da sauri ta taka tana komawa ciki , da murmushi ya bi bayan ta da kallo wani irin nishaɗi ne mai daɗi yake huɗa shi .
Ƙarfe uku ya ɗau hanyar Abuja tare da sofiya wacce ya biya gidan su ya ɗauke ta dole bayan ya mata jaan ido tare da barazanar barin ta ta cigaba da zama a gidan su na wasu kwanaki da take son yi dai-dai yake da rabuwar su baki ɗaya , jin haka ba shiri ta tattaro ƴan kayan ta ta bi shi, ba tare da ta kula Momy kori sun yi wata sallamar kirki ba saboda haushin ta da momy kori take ji .
ASSALAM ALAIKUM MASU KARATU DA FATAN KUNA LAFIYA ?
INA GODIYA DA YADDA DAI HAR KULLUM KUKE HAƘURI DA NI .
INSHA ALLAH SHAFI NA GABA SHINE ƘARSHEN LITTAFIN MHR DA ZAI BIYO BAYA NAN BA DA JIMAWA BA.
NAGODE
[1/17, 9:40 PM] +234 706 503 6187: MAFARI
( Hargitsin Rayuwa)
Umm'muaz
49
MARADI-NIGER
Kwanakin da suka biyo bayan bayyanuwar mummunan aikin da Gimbiya maimounatou ta aikatawa Biyamuradi Youssouf , tare da sa hannun Mammadou da Hajiya Mama ,
Masarautar maraÉ—i ta kasance cikin alhini mai tarin yawa , kusan kullum aka yi zaman fada da Waziri ne ke jagoranta ba'a da wani batu da ya wuce na sake tattaunawa kan wannan mummunan lamari haÉ—i da yiwa Biyamuradi Addu'ar samun lafiya tare da fatan dawowar Maimartaba .
Da har yau da suke cika kwanaki ishirin da ɗaya basu baro india ba , Amma ana saka ran dawowar tasu a yau ko gobe saboda saƙon yiwuwar dawowar tasu ya iso musu .
Akwai labari daga majiya mai tushe cewar gimbiya Siyama tare da ƙanin Biyamuradi Youssouf , 'Bilal wanda shine mai binsa a haihuwa sun fara shirin tafiya India domin cigaba da jinyar sa da har kawo yau babu wanda yasan takamaimai a halin da lafiyar Youssouf ɗin ke ciki .
Ta ɓangaren Hajiya Mama kuwa duk yadda ta kai ga sanyawa idanun ta toka ta mustsiƙe ta cigaba da yin harkokin ta yadda ta saba , amma ta gagara domin yadda labarin sa hannunta da na ɗan ta wajen yunƙurin kisan da Matar Biyamuradi tayi masa , ya bazu ba a bakin bayu da hadiman cikin masarautar Maradi kaɗai ba har jama'ar gari da na wasu jahohin labari ya kai musu .
Ake kuma kucin-cina labarin tare da sake liƙa masa baƙaƙen sassa ana sake munana sa ba ƙaramin tasiri hakan yayi wajen kassara mata duk wani karsashi haɗi da ɗagawar da take tinƙaho da shi na kasancewar ta matar Sarki .
Dan haka gaba ɗaya sai take neman zama mujiya , tsarguwa take da irin kallon da bayun gidan suke mata , gefe guda ga dumuwowi birjik da suka mata ƙawanya , wanda bata saba shiga makamantan su ba , mafi girman su halin da ɗan ta tilo namiji yake ciki wanda yake tamkar ga ƙoshi ga kwana yunwa a wajen ta , domin kuwa tasan muddin Youssouf ya rasa ransa, cikin hakan akwai yiwuwar shima Mammadou ayi masa huƙunci mai tsauri da ka iya kawo ƙarshen shima tasa rayuwar .
Ga Maimartaba da bata san matsayin ta takamaimai a wajen sa ba , bayan tonon sililin da Maimounatou tayi mata a gaban sa , gefe guda kuma ga Mairamar sarki da take autar ta sannan mafi soyuwa a wajenta cikin 'ya'ya da tun bayan faruwar wannan lamarin da ta samu labarin kome bayan kuka bata wani taɓuka abun kirki ,
Rufe kanta take a ɗakin ta da yake sashin uwar-riƙon ta , ( Hajiya Umma ) ta ci kuka ,domin lamarin ya mata tsauri wajen ɗauka duka biyu a lokaci guda ,
dan kuwa bayan kasantuwar Youssouf yayan ta mafi kusanci da yawan ƙauna a tsakanin su fiye da duk sauran 'yan uwan ta , ta shaƙu da shi tunda ta buɗi ido ta ga kanta riƙe a hannuwan sa , shiga hatsarin rasa shi ba abune mai sauƙi a wajen ta ba .
Damuwar ta tana sake hauhawa da hango rugujewar zancen auren ta , tare da ma guntilewar alaƙar su ita da masoyinta da suka ɗibi tsawon shekaru uku suna soyayya wanda yake yaya ne ga gimbiya Maimounatou , uwa ɗaya uba ɗaya gaf ma ake da yanke ranar auren su cikin watannin gaba kaɗan a sha biki , sai ga shi wannan mummunan lamarin ya shata layi a tsakanin su , domin kuwa ko ba'a sanar da ita ba ta san makomar soyayyar su ita da Khaalifa , sannan tun kafin a hana ta ita ya kamata ta fara zare soyayyar sa daga ran ta , bayan abunda ƙanwar sa ta aikata ga Biyamuradi ai babu wani sauran alaƙa mai girma da zai sake shiga tsakanin masarautun nasu biyu .
Ba tun yau ba ta riga ta san wasu daga cikin munanan halayen Mahaifiyar su da ita koyaushe huɗubar ta tare da yunƙurin ta bai wuce na ganin ta raba kyakkyawar alaƙar da ke tsakanin ta da uwar-goyon ta tare da sauran ƴan uwan ta da suka haɗa uba ɗaya ba ,
da ita kuma ko kusa bata ganin aibun su , sannan duk wasu laifuka nasu da hajiya Mama ke faɗin sun aikata ko suna kan aikatawa , ita bata kai ga kama su da ko guda ba dan haka koyaushe take biris da huɗubar ta , tare da toshe kunnuwan ta , ƙaunar ƴan uwanta a jinin ta yake tana ƙaunar su kwatankwacin ƙauna tare da zallar kulawa da su ma suke nuna mata a matsayin ta na ƙaramar ƙanwar su ,
ga hajiya Umma kuwa ba zata ce kome ba da ya wuce fatan alheri tare da godiya ,riƙo ta mata na haƙiƙa ba irin riƙon ƴar kishiya ba , dan haka take jinta basu da wata maraba da Hajiya Mama , sau dayawa ma tafi kusanci da Hajiya Umma akan ita Hajiya Mama ,( goyo guba )