← Book details Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 195 OF 269

Sashe 195

Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Cikin nutsuwa matar da take zaune a kan ɗaya daga cikin sabbin kujerun falon tana saƙa da zaren ul da kwarashi, ta ɗago kanta , idanun ta suka sauƙa akan Falmata da itama take iya hango alamun farar fatar ta daga inda take ,

Muryarta bata fita sosai ta amsa sallamar ,

Su dukkanin su shiru suka yi suna kallon juna ,

Cikin sanyin jiki falmata ta kalato murmushi ta É—ora bisa fuskar ta, zuciyar ta na bata cewa Rahima ce wannan take hangowa A hankali tace

"Rahima ni ce fa, ni ce Falmata ƙanwar Yakaka baki gane ni bane ?

Kwarashin hannun Khaalty Rahima ya faɗi ƙasa bata kula ba ta miƙe tsaye ta nufi inda Falmata take , zuciyarta na bata tabbacin cewa mafarki take , wataƙila kuma gizo take yi mata ,

Tana zuwa ta miƙa tafukanta biyu ta dafa kafaɗun Falmata idanunta suna jiran ɓacewar ta daga ganinsu ,

Ƴar dariya Falmata tayi , kafin tace ,

"Rahima kina mamakin gani na ko ? Yakaka ma ai tana zuwa wataƙila gobe zata iso ba tare muka zo ba Rahima....

Hannun Rahima da taji yana tattaɓa mata fuska , yasa ta haɗiye sauran kalmomin ta , ta riƙe hannuwan tana ƙoƙarin sauƙe su daga fuskarta , da wani irin sauti ƙasa-ƙasa , Khaalty Rahima tace

"Falmatana ke ce ? Ke ce wannan Falmata ? Ke ce ? Ina Yakakana ?

Rungumo ta tayi gaba É—aya zuwa cikin jikinta tana fashewa da kuka mai sauti ...

Assalamu Alaikum masu karatu .

Da fatan duk kuna lafiya ??

Ina mai baku haƙurin ji na shiru da kuka yi wasu hidindumu ne suka sha kaina , da fatan kun min uzuri ? ❤

Nagode .
[12/16/2019, 6:36 AM] +234 706 503 6187: MAFARI
( Hargitsin Rayuwa )

Umm'muaz

45

Da rashin yadda a fuskar Falmata , ta ɓanɓare jikinta daga na khaalty Rahima , Muryar ta na ɗan ƙyarma tace ,

"wacece  ? Rahima kece ?

Zuwa lokacin Murmushi Khaalty Rahima take , murmushin da har ya bayyana haƙoranta , sake riƙe hannun Falmata tayi , da sautin muryar ta mai ɗan ƙarfi tace , "Falmatana ni ce Mamar ku , ni ce , ashe kuna raye Falmata , ina Yakaka ?

Da wani irin yanayi Falmata take sake wara idanunta tana ganin dusu-dusun fuskar matar da take gabanta , tana jin wani irin bugu da zuciyarta ta sauya a take da ziyarta ruÉ—ani a tare da ita tace, "Mama na ? Ke ce Maman mu ?
   Sai tayi baya da sauri kamar zata gudu , ta waiga dama da hagunta , da wani sauti tace , "Yakaka ina kike ? Kina ina ? Ki zo ki ganta wai wannan Maman mu ce ? Wai da gaske ita ce ?

Murmushin fuskar Khaalty Rahima bai ɗauke ba lokacin da hawayen fuskarta suke cigaba da sauƙa ta matsa tana sake kusantar ta , sai ta miƙa hannu ta jaa hancin Falmata da bai wani ciƙa tsayi ba , ta zarce da riƙe kumatunta duk biyu da hannuwanta , sannan ta haɗa goshin su guri guda , tana sake cewa ,"Ni ce Mamanku Faɗimah-Zahra ni ce Ina Amina ?

Wani irin yanayi ne na zallar Farin-ciki mai tafe da sanyi mai samar da nutsuwa ,  taji yana bin duk wata jijiyar jikinta , a sanyaye ta karkata kanta , muryarta da rangwamen sauti tace ," Maman mu ke ce ? Ke ce Mama da gaske ba mafarki ko gizo ba ? Mama daman kina Raye ? Mamana .
   Bata jira ta amsa mata ba ta zarce da rungumeta ,tana sakin kuka da ƙaramin sauti , irin kukan da Ɗa yake irin sa a lokacin da ya tsinci kansa a gaban Mahaifiyar sa bayan tsawon lokacin da ya ɗauka yana haɗiyar baƙin-ciki cikin kewar ta .

  Khaalty Rahima ta sa hannu biyu ta rumgumeta , tana jin wani irin tarin farin-ciki marar misaltuwa , ashe daman rayuwa zata sake iya yi mata sauyi mai tattare da farin-ciki irin wanda ta fidda rai da samun sa , ashe watarana zata zo da zata sake ganin ƴa'ƴan ta ? Allah abin godiya .

   Sauƙowar Amnee daga Sama ita ta jaa hankalinta, da mamaki ta ƙaraso tana kallon su , da har zuwa lokaci , Falmata take kwakume da Mamanta bata bar kuka ba , da alamar tambaya a muryarta tace

   "Ukhtee Rahima me ya faru ? wacece wannan ?

, jin sautin muryarta yasa Falmata ɗago kanta , kafin ta bi bayan Khaalty Rahima da take riƙe da hannunta , suka ƙarasa gaban Amnee , da murmushi Khaalty Rahima ta haɗa hannun Falmata da na Amnee , tana cewa

   " wannan ita ce 'Ya ta Falmata da na baku labarin su ina zaton sun mutu ita da yayar ta mai sunanki Amina da ake mata laƙabi da Yakaka , ikon Allah da girma sai ga shi ya kawo min ita har gabana .
     Sai ta waiga ga Falmata , tare da cigaba da cewa , "Fatima ya akayi kika san ina nan ?

  Da bayyanuwar murna Amnee ta zarce da rungume Falmata , kafin ta ɗora da cewa , Alhamdulillah , Alhamdulillah , ashe ba haka nan ba na so yaran nan tun a rana ta farko da na fara ganin su , ace 'ya'ya nane , jini na , 'ya'yan 'yar'uwa ta , Ukhtee Rahima ai nasan Fatima da Yakaka tun shekarun baya suke rayuwa tare da 'yan uwansu a gidan nan ba tare da sun san dangantakar su da juna ba , kai Alhamdulillah .

Saman kujerun wajen suka zauna ,suna sanya Falmata a tsakiyar su , khaalty Rahima ta ce ,

     "Ikon Allah Ukhtee ashe ma kun san su ? Ashe suna hannun ku ?

    " ƙwarai na san su , ai yayan Zainab ( Doctor Hamza )  shine ya kawo su gidan nan a matsayin ƴan gudun Hijira , a gidan nan suke tsawon shekaru kusan biyar zuwa shidda  ,  ikon Allah kenan ai kuwa  ko zuwan Yakaka na kwanan nan taje har wajena ta gaishe ni ,  ai itace wacce kika ji na tambayi Rahima shekaranjiya kan ina take ta shaida min ta tafi Niger wajen Ƙanwar ta da 'yar ta , Allah ya saɓa haɗuwar ku ai da gidan nan zaki tarar da ita .

   "Ikon Allah ,  to Alhamdulillah , Alhamdulillah , sune kalmomin da Khaalty Rahima take faɗi farin-ciki na sake gauraya ta , ji da tayi ashe ma 'ya'yan ta gida suka dawo , ashe ma tare suke da yayun su , ƙarƙashin kulawar mutumin da yake mazaunin Uba a wajenta , Babu shakka tare da dukkanin tsanani akwai sauƙi , kuma ba'a fidda rai daga Rahamar Ubangiji .

  A kusan tare suka jefawa Falmata tambaya ,
    "Fatima ina Amina da 'yar ta ?

Shiru Falmata tayi da famin raunin cikin ranta , a hankali ta ce da su ,
    "Allah ya yiwa Mama rasuwa kwanaki huɗu da suka wuce ,
   "Innalillahi wa inna ilaihi raji'oon,  Innalillahi wa inna ilaihi raji'oon,"  suka haɗa baki wajen cewa , shiru kuma ya gifta tsakanin su cike da jimamin rashin jikar su da basu kai ga samun damar ko da ganin fuskarta ba a zahiri , babu shakka Allah baya barin wani domin wani ya ji daɗi .

   " Ina Maisunan Ukhtee ita kuma ? Ba wajen ki ta tafi ba ?

      Ƙhaalty Rahima ta sake tambayar Falmata ,
   Shiru Falmata tayi tana sunkuyar da kanta ,

  Wani busasshen yawu Khaalty Rahima ta haɗiye tana jin tashin hankalin da yake farmata , kada dai ace wani mummunan lamari ne ya afku ga ɗiyar ta mafi soyuwa gareta ?

    Matsa hannun Falmata dake cikin nata tayi da ɗan ƙarfi , ta ɗan ɗaga sauti tana sake maimaita tambayar " Falmata ina kika baro Yakaka ??

***

A Niamey tunda Yakaka ta dawo daga tasha , bayan samun tabbacin Falmata ta riga ta tafi Nigeria ta wannan mummunar hanyar mai cike da hatsarin Æ´an kungiyar Boko Haram ,

bayan kuka babu abunda take yi , gabadaya ta ɗora laifin gudun Falmata akanta , tayi danasanin zuwanta ƙasar baki ɗaya yafi a ƙirga , ganinta da ace bata zo ba da Falmata bata gudu ba , sai ta ji inama da ta zauna akan batun Youssouf da yace su rufa asirin tsakanin su kada Falmata ta sani a tun farko , ƙila da suna da damar da zasu haɗu ita da Youssouf su wanke kansu a wajen Falmata bayan sun ƙaryata ƴan uwansa a gabanta ,  da kuma lamarin bai kwaɓe ya haka ba ,

Ganin kuka ba zai mata magani ba yasa ta miƙe tsaye ɗauke da jakar kayanta , Hajja wacce take zaune zugum ta dube ta tare da cewa ,
     "Babba uwar Mama ke kuma ina za ki ? Kadda kice min kema gudun fanfalaƙin za kiyi ? Kiyi wa Allah ƴar nan ki tsaya mu ji da damuwa ɗaya kadda ki ɓaro mana wata sabuwa , guje-gujen nan ba kana bane , 'ya'yan nan ai ƙwarya ta gari tana ragaya , kamar yadda darajar ɗiya mace ɗakin Mijinta kar ki tafi ko'ina Dan Allah ,

Ba tare da Yakaka ta dubi Hajja ba tana share hawayenta da gefen hijabinta tace ,

"Hajja gara na tafi saboda Falmata fa ko da taje Maiduguri lafiya , bata fa san hanyar gidan Baa prof ba, kuma bata san kowa ba a garin bayan shi , dole zanyi hanzarin tafiya nima ko Allah zai sa na haɗu da ita a tasha , na tarye ta Hajja ina ƙaunar Falmata ita ce kaɗai jinina a duniya ina tsoron rasa ta Hajja , zan tafi bazan iya zama ba nima .

Guntuwar ƙwallar da ta tarawa Hajja a ido ta sa hannu biyu ta shafe fuskarta ta muttsuƙe ,
Chapter 195 · 0% Book details