Sashe 214
Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"to ai ga shi nan kin fara gani kishiyar rana tsaka ,baki da ko darajar da za'a sanar dake bare a miki abunda ake yiwa mata a al'adance idan aka tashi musu kishiya , idan baki bar gindin auren ɗan Amina ba kaɗan ma kika fara gani daga cikin irin ƙiyayyar da zata zuba miki ,
A haukace Sofiya ta warce hannun ta daga cikin na Momy kori , da ƙaraji a muryar ta tace ,
" ki bar ni Momy , nace ki bar ni wayyo Allah na na shiga uku Doctor meyasa za ka min haka duk irin kula da son da nake nuna maka irin sakayyar da za ka min kenan ?
Wani mummunan tsaki Momy kori ta jaa a fusaace tace , " to kar ki tashi dan uban ubanki ki zauna kina kuka anan , kina sambatun wofi akan wani lusarin yaron da bashi da zaɓin kan sa , shegiya mahaukaciya zauna anan nace ,
Daga haka ta fice a fusace , wasu daga cikin dangi da suke 'yan kanzagin ta suka rufa mata baya , wasu kuma duuu suka yi kan sofiya wacce take ta rafsa ihu kamar wacce uwar ta da ubanta suka mutu a haÉ—arin mota .
Yakaka wacce duk haukar da Sofiya take yi tana kallon ta , a hankali ta fara jaan ƙafafun ta tana yin baya-baya zuciyar ta kuwa cike da tsoron kar Sofiya ta gan ta ,
Ai kuwa bata yi nasara ba domin kamar ancewa Sofiya É—ago kan ki karaf ta sauke idanunta akan Yakaka ,
Wata irin zabura tayi ta miƙe har tana ture matan da suka taru suna rarrashin ta dayawa daga cikin su rayukan su a ɓace yake da irin cin zarafin da suke ganin an yiwa 'yar uwar su , yi mata kishiya ba tare da an sanar da ita ba , sai a wajen bikin ta samu labari babu shakka a wajen mata wannan shine iyakar cin zarafin da ɗa Namiji zai iya yi musu .
Kukan kura tayi ta kaiwa Yakaka cafka , da gudu Yakaka ta kewaya ta bayan kujeru tayi ɗakin Amnee dai-dai da murɗo ƙofar da Doctor Hamza yayi ya fito daga ɗakin ,
Tana zuwa ta shige jikin sa ta ƙanƙame shi , a bazata ya ji shigar sa jikin sa , dan haka ya ɗago kai a firgice dai-dai tahowar Sofiya , a cikin ƙanƙanin lokaci ƙwaƙwalwar sa ta fahimci abunda ke faruwa dan haka ya juya baya da sauri , dukan da Sofiya ta kawo gami da chafkar da taso yiwa maƙogoron Yakaka ya sauƙa a bayan sa ,
Tun ƙarfinta ta shiga dukan bayan sa da ya yiwa Yakaka rumfa da shi , tana ɗura ashar tare da shan alwashin a kan sai ta kashe Yakaka ,
Da kyar ya ɓanɓare Yakaka daga jikin sa wacce ta shige masa jiki ta runtse ido gam zuciyar ta bayan bugu ba abinda take yi , addu'o'i iri-iri bata gama wata take kama wata .
Ƙofar ɗakin Amnee ta murɗo ta leƙo , lokacin da yake zare Yakaka daga jikin sa ,
" Menene kuma hakan ?
Amnee ta tambaya a tsawace , Yakaka tana jin muryar ta ta juya da gudu ta kutsa ta bayan ta ta tsaya tana kallon Sofiya , tsintar kan ta tayi da kwashewa da irin dariyar nan ta na tsira , da kuma ƙarin ganin yadda Makeup ɗin da Sofi tayi duk ya mata muzu-muzu a fuska ya kwaɓe mata , kamar wata dodo .
Ganin Amnee bai sa Sofiya ta bar zage-zagen da take yi ba , sai ma daɗa zabura da take yi tana son kamo Yakaka , wacce har lokacin dariya take yi da gajerun fararen haƙoran ta ,
Dariyar ta ta shagaltar da Doctor Hamza wanda yake ta faman rirriƙe Sofiya kamar wata tunkiyar da take rawar turke , fuskar sa da ɓoyayyen murmushin da ya barranta da yanayin da yake ciki a zahiri a sace yake kallon Yakaka , yaƙi matsawa daga wajen kamar wanda aka dasa shi banda kokawa babu abunda yake da sofiya .
Muryar Amnee ce ta dawo da shi cikin hankalin sa , inda take cewa ,
" ka jaa ta ku bar nan wajen nace bana son hauka da rashin kunya kana jina ko ?
Da ƙarfi ya murɗa hannun sofiya , muryarsa cike da gargaɗi yace " ki nutsu Sofiya meye kike ne haka ? Ki zo mu tafi .
Ta tsakanin Mata da yaran da suke tsaye carko-carko suka wuce yana riƙe da tsintsiyar hannun ta
Sun zo kusa da sashin sa ta warce hannun ta da ƙarfi , muryar ta tana rawar kuka tace
" Ka daina jana Hamza , ina wai za ka kaini ? so nake kawai ka faÉ—a min gaskiya , dan ni har yanzu ban yadda da abunda yake shirin faruwa ba .
Matsowa yayi daf da ita yana satar kallon tsirarun mutanen da suke sabgogin su a harabar gidan yace " Sofiya kiyi haƙuri dan Allah muje ki nutsu na miki bayani..
Da ƙarin ƙarfin kukan da ta take yi tace " Bayani ? Bayanin me za ka min ? Doctor meye bana yi maka a zaman mu na aure da za ka min kishiya da wannan ƙazamar kuchakar Yarinyar ? Kuma ma wai har ka ɓoye min Doctor ka ƙi sanar da ni tun wuri da na yiwa tufka hanci .
Kwantar da murya yayi yace " Sofiya wallahi ba ni nace zan aure ta ba Baa da Amnee ne suka haÉ—a lamarin nan , ki bari zan miki bayani sosai idan mun zauna, yanzu ki bar kukan da kike muje cikin É—akina ki wanke fuskar ki , kin ga magariba ta gabato bana so na rasa jam'i ,
Juyawa tayi maimakon ta É—au hanyar cikin gidan sai ta kama hanyar sashin Prof , a tsorace ya sha gaban ta wannan karon fuskar sa babu alamun wasa yace " Ina za ki ?
Ita ma da wata irin faffaɗar murya tace " wajen sa zan je naji dalilin da zai sa ya mun haka , sannan kuma na roƙe shi dan Allah ya warware wannan mummunan ƙullin da yake son yiwa rayuwata ,
Muryar sa a dake da bayyanuwar ɓacin rai yace " Sofiya ki nutsu ki shiga hankalin ki , iyayena fa ba abun wasan ki bane , naga duk irin haukar da kika yi a gaban Amnee dan na miki uzuri dalilin cewa ke ma an miki kuskure ba hakan ne zai sa ki dunga yin duk abunda kika ga dama ba akan su , ki nutsu nan gaba zan iya ɗaukar mummunan mataki akan ki muddin kika nemi cin zarafin iyayena ,
Daga haka ya wuce ya bar ta a wajen , wajen famfon dake zubar ruwa ya nufa yana daura alwala ,
Da saurin da ya wuce ƙima Sofiya ta tasamma ƙofar gidan ta fita tamkar zata kifa ,
Zuciyar sa babu daɗi ya bita da kallo , wannan tashin hankalin yake gudu daga gareta yasa tun farko ya kasa sanar da ita , sam shi ba mutum bane mai ƙaunar hayaniya .
Yana kammala Alwala ya shiga motar sa ya tayar aka buɗe masa ƙofa , yana fita kafin ya dai-daita kan motar a bisa titi ya hango motocin su Doctor Suleiman tare da na wasu abokan sa su huɗu , motoci biyar kenan , a sarari yayi tsaki kafin yace " wannan kuma Uban 'yan didimar sai da ya min gayyar da na ce bana so .
Hannu kawai ya É—aga musu tare da matsa ham , ya bi bayan sofiya wacce ya hango har ta kusa titi .
Da kyar ta yadda ta shiga motar ya miƙa ta gidan su , sai dai ko ficewa a layin gidan nasu bai yi ba ita ma ta sake fitowa a cikin motar Momy kori da gudun gaske ta ɗau hanyar gidan gogaggen Malamin ta da ta yadda da shi ɗari cikin ɗari aikin sa na ci , aifa zama bai gan ta ba .
Matar mutum bata zama ta wanin sa , washegari da misalin ƙarfe goma na safe taron jama'ar da suka cika suka tumbatsa suka shaida ɗaurin auren Hamza Mustapha Dilmari tare da Amina Muhammad Kalama .
Bayan ɗaurin Aure walima ta biyo baya , abokan Doctor Hamza da suka tasamma su ishirin sun sanya shi a tsakiya gami da sauran dangi , bayan fara'a babu abunda yake kamar ba shi bane ya sha ɓacin-rai da jin labarin auren ,
Shi da kansa bai san takamaimai me yake bashi nishaɗi ba illa yasan wani ɗan tsiron farin-ciki ne daga can saƙon zuciyar sa da ya zata ya mutu tun-tuni yake sabunta kan sa a yau .
Ɗan gefe guda Suleiman ya jaa shi bayan ya gama tsokanar sa yadda ransa ke so a ƙarshe yace masa ya kamata Amarya ta fito su gaisa saboda su anjima kaɗan zasu juya .
Baya so ko kaɗan Suleiman ya fahimci akwai wani abu marar daɗi a tsakanin sa da ita saboda ko babu kome ita a yanzu wata ɓangare ce ta rayuwar sa ba zai so ya zubda mata da ƙima a wajen wasu nasa ba dan haka yace ," Abokina mu je daga sashi na a ƙira ta ta gaishe ka kai kaɗai amma sauran sa haɗu watarana kawai .
" Ayi haka kuwa abokina ? Doctor Suleiman yace da ɗan shakku , hannun sa Doctor Hamza ya jaa tare da cewa "ai anyi ma , suka fara tafiya zuwa sashin sa yana ƙiran Amnee a waya , bayan ta ɗaga yake sanar da ita buƙatar sa na son a turo Yakaka sashin sa zasu gaisa ita da Suleiman .
Cike da murnar da tunda aka ɗaura auren lafiya yake mamaye ta , Amnee ta miƙe daga bakin gadon ta da take suke zaune ita da wasu ƴan'uwanta suna tattaunawa ta nufi ɗakin da ta bari a ɗazu Hajje Nadiya tana shirya Amaren a ciki ,
A haukace Sofiya ta warce hannun ta daga cikin na Momy kori , da ƙaraji a muryar ta tace ,
" ki bar ni Momy , nace ki bar ni wayyo Allah na na shiga uku Doctor meyasa za ka min haka duk irin kula da son da nake nuna maka irin sakayyar da za ka min kenan ?
Wani mummunan tsaki Momy kori ta jaa a fusaace tace , " to kar ki tashi dan uban ubanki ki zauna kina kuka anan , kina sambatun wofi akan wani lusarin yaron da bashi da zaɓin kan sa , shegiya mahaukaciya zauna anan nace ,
Daga haka ta fice a fusace , wasu daga cikin dangi da suke 'yan kanzagin ta suka rufa mata baya , wasu kuma duuu suka yi kan sofiya wacce take ta rafsa ihu kamar wacce uwar ta da ubanta suka mutu a haÉ—arin mota .
Yakaka wacce duk haukar da Sofiya take yi tana kallon ta , a hankali ta fara jaan ƙafafun ta tana yin baya-baya zuciyar ta kuwa cike da tsoron kar Sofiya ta gan ta ,
Ai kuwa bata yi nasara ba domin kamar ancewa Sofiya É—ago kan ki karaf ta sauke idanunta akan Yakaka ,
Wata irin zabura tayi ta miƙe har tana ture matan da suka taru suna rarrashin ta dayawa daga cikin su rayukan su a ɓace yake da irin cin zarafin da suke ganin an yiwa 'yar uwar su , yi mata kishiya ba tare da an sanar da ita ba , sai a wajen bikin ta samu labari babu shakka a wajen mata wannan shine iyakar cin zarafin da ɗa Namiji zai iya yi musu .
Kukan kura tayi ta kaiwa Yakaka cafka , da gudu Yakaka ta kewaya ta bayan kujeru tayi ɗakin Amnee dai-dai da murɗo ƙofar da Doctor Hamza yayi ya fito daga ɗakin ,
Tana zuwa ta shige jikin sa ta ƙanƙame shi , a bazata ya ji shigar sa jikin sa , dan haka ya ɗago kai a firgice dai-dai tahowar Sofiya , a cikin ƙanƙanin lokaci ƙwaƙwalwar sa ta fahimci abunda ke faruwa dan haka ya juya baya da sauri , dukan da Sofiya ta kawo gami da chafkar da taso yiwa maƙogoron Yakaka ya sauƙa a bayan sa ,
Tun ƙarfinta ta shiga dukan bayan sa da ya yiwa Yakaka rumfa da shi , tana ɗura ashar tare da shan alwashin a kan sai ta kashe Yakaka ,
Da kyar ya ɓanɓare Yakaka daga jikin sa wacce ta shige masa jiki ta runtse ido gam zuciyar ta bayan bugu ba abinda take yi , addu'o'i iri-iri bata gama wata take kama wata .
Ƙofar ɗakin Amnee ta murɗo ta leƙo , lokacin da yake zare Yakaka daga jikin sa ,
" Menene kuma hakan ?
Amnee ta tambaya a tsawace , Yakaka tana jin muryar ta ta juya da gudu ta kutsa ta bayan ta ta tsaya tana kallon Sofiya , tsintar kan ta tayi da kwashewa da irin dariyar nan ta na tsira , da kuma ƙarin ganin yadda Makeup ɗin da Sofi tayi duk ya mata muzu-muzu a fuska ya kwaɓe mata , kamar wata dodo .
Ganin Amnee bai sa Sofiya ta bar zage-zagen da take yi ba , sai ma daɗa zabura da take yi tana son kamo Yakaka , wacce har lokacin dariya take yi da gajerun fararen haƙoran ta ,
Dariyar ta ta shagaltar da Doctor Hamza wanda yake ta faman rirriƙe Sofiya kamar wata tunkiyar da take rawar turke , fuskar sa da ɓoyayyen murmushin da ya barranta da yanayin da yake ciki a zahiri a sace yake kallon Yakaka , yaƙi matsawa daga wajen kamar wanda aka dasa shi banda kokawa babu abunda yake da sofiya .
Muryar Amnee ce ta dawo da shi cikin hankalin sa , inda take cewa ,
" ka jaa ta ku bar nan wajen nace bana son hauka da rashin kunya kana jina ko ?
Da ƙarfi ya murɗa hannun sofiya , muryarsa cike da gargaɗi yace " ki nutsu Sofiya meye kike ne haka ? Ki zo mu tafi .
Ta tsakanin Mata da yaran da suke tsaye carko-carko suka wuce yana riƙe da tsintsiyar hannun ta
Sun zo kusa da sashin sa ta warce hannun ta da ƙarfi , muryar ta tana rawar kuka tace
" Ka daina jana Hamza , ina wai za ka kaini ? so nake kawai ka faÉ—a min gaskiya , dan ni har yanzu ban yadda da abunda yake shirin faruwa ba .
Matsowa yayi daf da ita yana satar kallon tsirarun mutanen da suke sabgogin su a harabar gidan yace " Sofiya kiyi haƙuri dan Allah muje ki nutsu na miki bayani..
Da ƙarin ƙarfin kukan da ta take yi tace " Bayani ? Bayanin me za ka min ? Doctor meye bana yi maka a zaman mu na aure da za ka min kishiya da wannan ƙazamar kuchakar Yarinyar ? Kuma ma wai har ka ɓoye min Doctor ka ƙi sanar da ni tun wuri da na yiwa tufka hanci .
Kwantar da murya yayi yace " Sofiya wallahi ba ni nace zan aure ta ba Baa da Amnee ne suka haÉ—a lamarin nan , ki bari zan miki bayani sosai idan mun zauna, yanzu ki bar kukan da kike muje cikin É—akina ki wanke fuskar ki , kin ga magariba ta gabato bana so na rasa jam'i ,
Juyawa tayi maimakon ta É—au hanyar cikin gidan sai ta kama hanyar sashin Prof , a tsorace ya sha gaban ta wannan karon fuskar sa babu alamun wasa yace " Ina za ki ?
Ita ma da wata irin faffaɗar murya tace " wajen sa zan je naji dalilin da zai sa ya mun haka , sannan kuma na roƙe shi dan Allah ya warware wannan mummunan ƙullin da yake son yiwa rayuwata ,
Muryar sa a dake da bayyanuwar ɓacin rai yace " Sofiya ki nutsu ki shiga hankalin ki , iyayena fa ba abun wasan ki bane , naga duk irin haukar da kika yi a gaban Amnee dan na miki uzuri dalilin cewa ke ma an miki kuskure ba hakan ne zai sa ki dunga yin duk abunda kika ga dama ba akan su , ki nutsu nan gaba zan iya ɗaukar mummunan mataki akan ki muddin kika nemi cin zarafin iyayena ,
Daga haka ya wuce ya bar ta a wajen , wajen famfon dake zubar ruwa ya nufa yana daura alwala ,
Da saurin da ya wuce ƙima Sofiya ta tasamma ƙofar gidan ta fita tamkar zata kifa ,
Zuciyar sa babu daɗi ya bita da kallo , wannan tashin hankalin yake gudu daga gareta yasa tun farko ya kasa sanar da ita , sam shi ba mutum bane mai ƙaunar hayaniya .
Yana kammala Alwala ya shiga motar sa ya tayar aka buɗe masa ƙofa , yana fita kafin ya dai-daita kan motar a bisa titi ya hango motocin su Doctor Suleiman tare da na wasu abokan sa su huɗu , motoci biyar kenan , a sarari yayi tsaki kafin yace " wannan kuma Uban 'yan didimar sai da ya min gayyar da na ce bana so .
Hannu kawai ya É—aga musu tare da matsa ham , ya bi bayan sofiya wacce ya hango har ta kusa titi .
Da kyar ta yadda ta shiga motar ya miƙa ta gidan su , sai dai ko ficewa a layin gidan nasu bai yi ba ita ma ta sake fitowa a cikin motar Momy kori da gudun gaske ta ɗau hanyar gidan gogaggen Malamin ta da ta yadda da shi ɗari cikin ɗari aikin sa na ci , aifa zama bai gan ta ba .
Matar mutum bata zama ta wanin sa , washegari da misalin ƙarfe goma na safe taron jama'ar da suka cika suka tumbatsa suka shaida ɗaurin auren Hamza Mustapha Dilmari tare da Amina Muhammad Kalama .
Bayan ɗaurin Aure walima ta biyo baya , abokan Doctor Hamza da suka tasamma su ishirin sun sanya shi a tsakiya gami da sauran dangi , bayan fara'a babu abunda yake kamar ba shi bane ya sha ɓacin-rai da jin labarin auren ,
Shi da kansa bai san takamaimai me yake bashi nishaɗi ba illa yasan wani ɗan tsiron farin-ciki ne daga can saƙon zuciyar sa da ya zata ya mutu tun-tuni yake sabunta kan sa a yau .
Ɗan gefe guda Suleiman ya jaa shi bayan ya gama tsokanar sa yadda ransa ke so a ƙarshe yace masa ya kamata Amarya ta fito su gaisa saboda su anjima kaɗan zasu juya .
Baya so ko kaɗan Suleiman ya fahimci akwai wani abu marar daɗi a tsakanin sa da ita saboda ko babu kome ita a yanzu wata ɓangare ce ta rayuwar sa ba zai so ya zubda mata da ƙima a wajen wasu nasa ba dan haka yace ," Abokina mu je daga sashi na a ƙira ta ta gaishe ka kai kaɗai amma sauran sa haɗu watarana kawai .
" Ayi haka kuwa abokina ? Doctor Suleiman yace da ɗan shakku , hannun sa Doctor Hamza ya jaa tare da cewa "ai anyi ma , suka fara tafiya zuwa sashin sa yana ƙiran Amnee a waya , bayan ta ɗaga yake sanar da ita buƙatar sa na son a turo Yakaka sashin sa zasu gaisa ita da Suleiman .
Cike da murnar da tunda aka ɗaura auren lafiya yake mamaye ta , Amnee ta miƙe daga bakin gadon ta da take suke zaune ita da wasu ƴan'uwanta suna tattaunawa ta nufi ɗakin da ta bari a ɗazu Hajje Nadiya tana shirya Amaren a ciki ,