Sashe 249
Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shiru yayi har lokacin da Sofia ta ƙaraso wajen ta zauna fuskar ta wasai kamar an mata bishara .
"Wafaa ya ƙira Yakaka da tsauri a muryar sa .
A hankali ta É—ago kan ta.
"Babu kare a gidan nan .
Hawayen da bata san yaushe suka taru ba su ne suka silalo mata .
"A karo na ƙarshe ina faɗa miki ba kare a gidan nan ya kamata ki kwantar da hankalin ki ki daina wannan firgice-firgicen da kike yi ko kina son ƙwaƙwalwar ki ta samu matsala ne ?
"Docto wai daman akan haukar .....
"Sofia idan ina magana ki daina saka min baki please behave yourself.
Yace yana mata wani mummunan kallo gaba ɗaya daga ƙasan ran sa yana zargin Sofia da bai san dalilin hakan ba shi dai zuciyar sa bata aminta da ita ba akan wannan matsalar da tayi sammakon shigowa rayuwar auren sa da Yakaka da ko kaɗan abun bai masa daɗi ganin ta koyaushe a firgice tana guje-guje da safure-safure yana ƙona masa rai tare da sauƙar masa da gajiya .
"Wafaa ya ƙira ta a tausashe , ta ɗago kan ta da idanun ta da suke narke take kallon sa .
"Zan yi shirin Masallaci idan na dawo daga Sallah zamu je mu ci abincin kar ki shiga kitchen yanzu dare yayi .
Langaɓe kan ta tayi kawai bata amsa ba ko kaɗan bata son ya matsa ya bar wani sarari tsakanin ta da Sofi .
Mayar da kallon sa kan sofia yayi wacce take ta faman hura hanci tana kokawa da zuciyar ta da take jin har wani toroƙo take kamar za ta fashe
"Sofi anjima ina so nayi magana da ku baki É—aya .
Bai jira amsar ta ba ya miƙe , Yakaka ma cikam! Ta miƙe tana riga shi wucewa ta yi hanyar ɗakin su .
Da kallo ya bi bayan ta kayan da ta sa a jikin ta ya masa kyau matuƙa sai ya gan ta kamar irin kyawawan matan nan da ake tallan sutura da su .( model's ) a hankali ya taka ya bi bayan ta
Sofia wacce take zaune É—im!akan kujera ta kaiwa kujerar wani irin duka da hannu kafin ta toshe bakin ta da hannu wani irin kuka take yi ciki-ciki , irin kishin da take ji a ran ta akan Yakaka muddin bata É—au mataki ba za ta iya haÉ—iyar zuciya ta mutu.
Lokacin da Doctor Hamza ya idar da sallar Magarib yayi niyyar komawa gida amma yunwar da yake ji da kuma sanin da yayi a gidan ma shi suke jira tunda ya hana ayi girkin sai kawai da ya shigo gidan ya É—au motar sa ya sake fita ba tare da ya shiga cikin gidan ba .
Sofia da ta ji ƙugin tashin motar sa da sauri ta leƙa ta window ta ga fitar sa , tana ganin ya bar gidan a guje ta sauƙa ƙasa kai tsaye ɗakin Yakaka ta tasamma .
Tana murɗa ƙofar ta ji a kulle , ɗan kwankwasawa tayi cikin salon da Doctor Hamza yake yi .
Yakaka wacce take zaune ta miƙe a hankali ta ƙarasa jikin ƙofar .
Haka kawai ta ji zuciyar ta ta doka da ƙarfi dan haka ta dakata ta fasa bude kofar cikin siririyar murya tace "Waye ?
Shiru Sofi tayi tana fatan ta buɗe su gamu , sake dukan ƙofar tayi da karfi da hakan ya sa nan take Yakaka ta fahimci wace ce a wajen dan haka a sarari ta furta "Auzu Billah minash Shaytanir Rajeem, baya ta koma ta zauna a inda ta ta shi.
"Ya kamata na samarwa kaina da mafita ni Yakaka lamarin Matar nan ya fara wuce iyakata ta musulunci , ta furta hakan a sarari kawo yanzu ta haƙaƙe da gasken gaske sofi ta ɗaura ɗamarar yaƙar ta dalili kawai;sun hada Miji daya.
"Ina Mafita?
Haka Sofia ta gaji da bugun ƙofar tana surutai , jin shigowar motar Doctor Hamza ya sa tayi saurin barin wajen ta koma ɗakin ta kai tsaye banɗaki ta shiga ta sakarwa kan ta ruwan sanyi .
Kusan mintuna goma sha biyar suka kwashe suna jiran sofia ta zo su ci abinci amma shiru ba alamun ta sau uku yana ƙiran layin ta wayar tana ƙara bata ɗauka ,
Ran sa ya fara ɓaci da salon rainin da yake hango take-taken sa daga Sofia wanda kuma ba zai ɗauka ba .
"Wafaa hau sama ki ƙira Sofia .
Kamar bata fahimci abunda yake cewa ba haka Yakaka take jahiltar sa da ido .
Ganin yadda tayi da fuska ya sa shi miƙewa da kan sa ya nufi saman .
Yakaka wacce ta bi shi da kallo da tuno da abunda ya faru jiya daga zuwa ƙiran Sofi ya sa ta miƙewa tsaye da sauri .
"yaya Dakta .
Ta ƙira sunan sa ,
a hankali ya waigo.
"zan bika .
tace tana yin narai-narai da ido .
Bai amsa ba sai hannun sa da ya miƙo mata alamar ta taho da sauri ta isa gare shi tana jefa hannun ta cikin na shi , ya riƙe ta suka hau saman tare .
Sofia wacce take tsaye a maɓoyar ta tana ganin duk abunda ya faru kafin su ƙaraso ta fito da sauri kamar daga ɗaki ta fito ,
Wani irin kallo ta watsa musu kafin ta gyara fuskar ta tana cewa " Yaks manya ke dai ko ina kina liƙe da Miji ɗa Namiji daɗi ko ai kin saba .
"Sofi sau nawa zan faÉ—a miki ki daina min yawo a gida tsirara-tsirara ?
Doctor Hamza ya katse ta ba tare da ya bari zancen da tayi yayi tasirin da zai hana shi sukuni ba duk da cewa kalmomin ta sun taɓa ran sa .
Buɗe baki Sofi tayi cike da mamaki kafin ta mayar da ganin ta kan Yakaka wacce ta sunkuyar da kan ta a tun kallon farko da tayiwa Sofi da take sanye da wasu bodycon sleeve rigar duk bata karasa kugun ta ba wandon kuwa iyakar shi ƙourin ta rashin kaurin da kayan ke da Su ya ya taimaka wajen fiddo da halittun jikin ta .
Narke murya tayi cike da kissa tana ƙoƙarin haɗiye fushin ta tace "Doctor kai ne fa kake cewa kafi son kana gani na a haka Kana jin daɗi tare da samun gamsuwar ido sobada ganin ko ina nawa a ciccike ko ka manta ne ? Kai ne fa kake cewa siririyar mace ramammiya haushi take ba....
A hankali Yakaka ta zame hannun ta tayi baya tana barin wajen saboda fahimta da tayi gaba kaÉ—an Sofi zata ce wani abu da zai fi haka ji mata ciwo .
"Duk ban tambaye ki wannan zancen ba dan na lura bakya jin kunyar ƙarya Sofi da girman ki amma ina so ki sani a yanzu ba mu kaɗai ne a gidan dan haka bana so na sake ganin ki haka kina min yawo a gida .
"Riga da wondo ne fa Doctor na ? Ta furta hakan a shagwaɓe zuciyar ta sol ganin Yakaka ta ɓace a wajen .
"Eh amma na 'yan iska ba ? Ko Wafaa ma ai riga da wondo ta saka amma na mutunci da zata iya fitowa a gaban ki kuma sun mata kyau sun burge ni .
"Ki koma ki sauya kaya ni ba zan iya cigaba da jiran ki cin abinci ba zamu fara ci dan yunwa nake ji .
Daga haka ya juya yana barin wajen , Sofi ta bi jikin ta da kallo kalmomin sa na dawo mata a kai "Doctor yana daf da kufce min na shiga uku ni Safiya ni ce yau yake cewa na dunga rufe masa jikin da a baya yafi kaunar ganin sa fiye da television?
Bayan sun gama cin abincin da Yakaka take jin sa ba wani daÉ—i sosai hakan kuwa bai rasa nasaba da yadda duk suka haÉ—a ido da Sofi sai ta galla mata harara .
Dan haka tana gama ci ta miƙe zata yi tafiyar ta Doctor Hamza da duk yake kallon motsin su ya dakatar da ita ta dawo ta zauna har ya gama cin abincin sa .
Sannan ya fara yi musu nasiha cikin nutsuwa da fiye da rabin ta yafi karkata akan tunasar da su kan gujewa ɗaukar hakkin juna/cutar da juna sannan ya kwaɗaitar da su daɗin da za su ji su kuma jiyar da shi muddin suka zauna lafiya da juna a matsayin 'yan uwa ba abokan hamayya ba sannan ya tunasar da su shi aure bangare ne na ibada da ake samun ɗimbin lada a gurin Ubangiji Allah ta dalilin sa , dan haka yake jaan hankalin su da suyi ƙoƙari wajen ganin sun yi bautar su yadda ya dace. sai ya rufe da cewa
"Muddin kuka haÉ—a kai ku ka min rumfa ku ka bani kariya , ku ka bani kulawar da ta dace da ta samar min da nutsuwa ai ba za ku bar wata damar da wata za ta sake ratso tsakanin mu ba ku biyun nan kun isheni rayuwa ta duniya Safiya da Amina bayan ku duk sauran mata ba zan gan su har su burge ni ba
Da murmushi Yakaka take kallon sa kalmomin sa sun mata daÉ—i sosai kafin a hankali tace "Yaya Dakta da yardar Allah ba zamu zama sanadin tashin hankalin ka ba kai ma ka dunga mana addu'a Allah ya haÉ—a kan mu ya kori shaiÉ—an a tsakanin mu .
"Ameen Wafaa tun kafin yanzu ina muku addu'a zan kuma cigaba da yi muku insha Allah .
"Sofi baki ce kome ba ?
Ya furta hakan yana É—ora ganin sa akan ta wacce ta tattara hankalin ta duk akan fuskar wayat ta kamar bata wajen '
Sake yi tayi kamar bata jin sa duk kuwa da cewa sarai tana jin nasa shi ma kuma ya san tana ji dan haka ya É—auke ganin sa daga kan ta ya mayar ga Yakaka yana cigaba da cewa
"Sai batun kwanakin girkin ku bayan kin gama kwanakin ki bakwai na amarci kamar yadda addini ya tanadar da yau kike da kwanaki biyu a gidan nan dan haka yau mun samu kwana biyu ko Wafaa ?
"Wafaa ya ƙira Yakaka da tsauri a muryar sa .
A hankali ta É—ago kan ta.
"Babu kare a gidan nan .
Hawayen da bata san yaushe suka taru ba su ne suka silalo mata .
"A karo na ƙarshe ina faɗa miki ba kare a gidan nan ya kamata ki kwantar da hankalin ki ki daina wannan firgice-firgicen da kike yi ko kina son ƙwaƙwalwar ki ta samu matsala ne ?
"Docto wai daman akan haukar .....
"Sofia idan ina magana ki daina saka min baki please behave yourself.
Yace yana mata wani mummunan kallo gaba ɗaya daga ƙasan ran sa yana zargin Sofia da bai san dalilin hakan ba shi dai zuciyar sa bata aminta da ita ba akan wannan matsalar da tayi sammakon shigowa rayuwar auren sa da Yakaka da ko kaɗan abun bai masa daɗi ganin ta koyaushe a firgice tana guje-guje da safure-safure yana ƙona masa rai tare da sauƙar masa da gajiya .
"Wafaa ya ƙira ta a tausashe , ta ɗago kan ta da idanun ta da suke narke take kallon sa .
"Zan yi shirin Masallaci idan na dawo daga Sallah zamu je mu ci abincin kar ki shiga kitchen yanzu dare yayi .
Langaɓe kan ta tayi kawai bata amsa ba ko kaɗan bata son ya matsa ya bar wani sarari tsakanin ta da Sofi .
Mayar da kallon sa kan sofia yayi wacce take ta faman hura hanci tana kokawa da zuciyar ta da take jin har wani toroƙo take kamar za ta fashe
"Sofi anjima ina so nayi magana da ku baki É—aya .
Bai jira amsar ta ba ya miƙe , Yakaka ma cikam! Ta miƙe tana riga shi wucewa ta yi hanyar ɗakin su .
Da kallo ya bi bayan ta kayan da ta sa a jikin ta ya masa kyau matuƙa sai ya gan ta kamar irin kyawawan matan nan da ake tallan sutura da su .( model's ) a hankali ya taka ya bi bayan ta
Sofia wacce take zaune É—im!akan kujera ta kaiwa kujerar wani irin duka da hannu kafin ta toshe bakin ta da hannu wani irin kuka take yi ciki-ciki , irin kishin da take ji a ran ta akan Yakaka muddin bata É—au mataki ba za ta iya haÉ—iyar zuciya ta mutu.
Lokacin da Doctor Hamza ya idar da sallar Magarib yayi niyyar komawa gida amma yunwar da yake ji da kuma sanin da yayi a gidan ma shi suke jira tunda ya hana ayi girkin sai kawai da ya shigo gidan ya É—au motar sa ya sake fita ba tare da ya shiga cikin gidan ba .
Sofia da ta ji ƙugin tashin motar sa da sauri ta leƙa ta window ta ga fitar sa , tana ganin ya bar gidan a guje ta sauƙa ƙasa kai tsaye ɗakin Yakaka ta tasamma .
Tana murɗa ƙofar ta ji a kulle , ɗan kwankwasawa tayi cikin salon da Doctor Hamza yake yi .
Yakaka wacce take zaune ta miƙe a hankali ta ƙarasa jikin ƙofar .
Haka kawai ta ji zuciyar ta ta doka da ƙarfi dan haka ta dakata ta fasa bude kofar cikin siririyar murya tace "Waye ?
Shiru Sofi tayi tana fatan ta buɗe su gamu , sake dukan ƙofar tayi da karfi da hakan ya sa nan take Yakaka ta fahimci wace ce a wajen dan haka a sarari ta furta "Auzu Billah minash Shaytanir Rajeem, baya ta koma ta zauna a inda ta ta shi.
"Ya kamata na samarwa kaina da mafita ni Yakaka lamarin Matar nan ya fara wuce iyakata ta musulunci , ta furta hakan a sarari kawo yanzu ta haƙaƙe da gasken gaske sofi ta ɗaura ɗamarar yaƙar ta dalili kawai;sun hada Miji daya.
"Ina Mafita?
Haka Sofia ta gaji da bugun ƙofar tana surutai , jin shigowar motar Doctor Hamza ya sa tayi saurin barin wajen ta koma ɗakin ta kai tsaye banɗaki ta shiga ta sakarwa kan ta ruwan sanyi .
Kusan mintuna goma sha biyar suka kwashe suna jiran sofia ta zo su ci abinci amma shiru ba alamun ta sau uku yana ƙiran layin ta wayar tana ƙara bata ɗauka ,
Ran sa ya fara ɓaci da salon rainin da yake hango take-taken sa daga Sofia wanda kuma ba zai ɗauka ba .
"Wafaa hau sama ki ƙira Sofia .
Kamar bata fahimci abunda yake cewa ba haka Yakaka take jahiltar sa da ido .
Ganin yadda tayi da fuska ya sa shi miƙewa da kan sa ya nufi saman .
Yakaka wacce ta bi shi da kallo da tuno da abunda ya faru jiya daga zuwa ƙiran Sofi ya sa ta miƙewa tsaye da sauri .
"yaya Dakta .
Ta ƙira sunan sa ,
a hankali ya waigo.
"zan bika .
tace tana yin narai-narai da ido .
Bai amsa ba sai hannun sa da ya miƙo mata alamar ta taho da sauri ta isa gare shi tana jefa hannun ta cikin na shi , ya riƙe ta suka hau saman tare .
Sofia wacce take tsaye a maɓoyar ta tana ganin duk abunda ya faru kafin su ƙaraso ta fito da sauri kamar daga ɗaki ta fito ,
Wani irin kallo ta watsa musu kafin ta gyara fuskar ta tana cewa " Yaks manya ke dai ko ina kina liƙe da Miji ɗa Namiji daɗi ko ai kin saba .
"Sofi sau nawa zan faÉ—a miki ki daina min yawo a gida tsirara-tsirara ?
Doctor Hamza ya katse ta ba tare da ya bari zancen da tayi yayi tasirin da zai hana shi sukuni ba duk da cewa kalmomin ta sun taɓa ran sa .
Buɗe baki Sofi tayi cike da mamaki kafin ta mayar da ganin ta kan Yakaka wacce ta sunkuyar da kan ta a tun kallon farko da tayiwa Sofi da take sanye da wasu bodycon sleeve rigar duk bata karasa kugun ta ba wandon kuwa iyakar shi ƙourin ta rashin kaurin da kayan ke da Su ya ya taimaka wajen fiddo da halittun jikin ta .
Narke murya tayi cike da kissa tana ƙoƙarin haɗiye fushin ta tace "Doctor kai ne fa kake cewa kafi son kana gani na a haka Kana jin daɗi tare da samun gamsuwar ido sobada ganin ko ina nawa a ciccike ko ka manta ne ? Kai ne fa kake cewa siririyar mace ramammiya haushi take ba....
A hankali Yakaka ta zame hannun ta tayi baya tana barin wajen saboda fahimta da tayi gaba kaÉ—an Sofi zata ce wani abu da zai fi haka ji mata ciwo .
"Duk ban tambaye ki wannan zancen ba dan na lura bakya jin kunyar ƙarya Sofi da girman ki amma ina so ki sani a yanzu ba mu kaɗai ne a gidan dan haka bana so na sake ganin ki haka kina min yawo a gida .
"Riga da wondo ne fa Doctor na ? Ta furta hakan a shagwaɓe zuciyar ta sol ganin Yakaka ta ɓace a wajen .
"Eh amma na 'yan iska ba ? Ko Wafaa ma ai riga da wondo ta saka amma na mutunci da zata iya fitowa a gaban ki kuma sun mata kyau sun burge ni .
"Ki koma ki sauya kaya ni ba zan iya cigaba da jiran ki cin abinci ba zamu fara ci dan yunwa nake ji .
Daga haka ya juya yana barin wajen , Sofi ta bi jikin ta da kallo kalmomin sa na dawo mata a kai "Doctor yana daf da kufce min na shiga uku ni Safiya ni ce yau yake cewa na dunga rufe masa jikin da a baya yafi kaunar ganin sa fiye da television?
Bayan sun gama cin abincin da Yakaka take jin sa ba wani daÉ—i sosai hakan kuwa bai rasa nasaba da yadda duk suka haÉ—a ido da Sofi sai ta galla mata harara .
Dan haka tana gama ci ta miƙe zata yi tafiyar ta Doctor Hamza da duk yake kallon motsin su ya dakatar da ita ta dawo ta zauna har ya gama cin abincin sa .
Sannan ya fara yi musu nasiha cikin nutsuwa da fiye da rabin ta yafi karkata akan tunasar da su kan gujewa ɗaukar hakkin juna/cutar da juna sannan ya kwaɗaitar da su daɗin da za su ji su kuma jiyar da shi muddin suka zauna lafiya da juna a matsayin 'yan uwa ba abokan hamayya ba sannan ya tunasar da su shi aure bangare ne na ibada da ake samun ɗimbin lada a gurin Ubangiji Allah ta dalilin sa , dan haka yake jaan hankalin su da suyi ƙoƙari wajen ganin sun yi bautar su yadda ya dace. sai ya rufe da cewa
"Muddin kuka haÉ—a kai ku ka min rumfa ku ka bani kariya , ku ka bani kulawar da ta dace da ta samar min da nutsuwa ai ba za ku bar wata damar da wata za ta sake ratso tsakanin mu ba ku biyun nan kun isheni rayuwa ta duniya Safiya da Amina bayan ku duk sauran mata ba zan gan su har su burge ni ba
Da murmushi Yakaka take kallon sa kalmomin sa sun mata daÉ—i sosai kafin a hankali tace "Yaya Dakta da yardar Allah ba zamu zama sanadin tashin hankalin ka ba kai ma ka dunga mana addu'a Allah ya haÉ—a kan mu ya kori shaiÉ—an a tsakanin mu .
"Ameen Wafaa tun kafin yanzu ina muku addu'a zan kuma cigaba da yi muku insha Allah .
"Sofi baki ce kome ba ?
Ya furta hakan yana É—ora ganin sa akan ta wacce ta tattara hankalin ta duk akan fuskar wayat ta kamar bata wajen '
Sake yi tayi kamar bata jin sa duk kuwa da cewa sarai tana jin nasa shi ma kuma ya san tana ji dan haka ya É—auke ganin sa daga kan ta ya mayar ga Yakaka yana cigaba da cewa
"Sai batun kwanakin girkin ku bayan kin gama kwanakin ki bakwai na amarci kamar yadda addini ya tanadar da yau kike da kwanaki biyu a gidan nan dan haka yau mun samu kwana biyu ko Wafaa ?