← Book details Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 257 OF 269

Sashe 257

Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Laifi zuciya ta tayi a doumin ta so ka ? Ko kouwa ni nayi laifi da na kassa jumriya akan ƙamnar ka har dai nayi kafiya kan Amren ka ? Da ka ke gwadan rashin ƙamna a fili kake watsi da sha'anin da duk ya shafe ni ?

Tasowa yayi ya dawo gaban ta ya zauna yana jin girman laifin sa na masa lulluɓi tunda ya kai girman da har ta kai yau Siyama ta ɗaga Muryar ta .

Hannuwan ta da suka ɗau sanyi ya riƙe yana lalubo kalmomin da ya musu ajiya mai nisa da basa taso da kan su sai fa akan wacce aka yi ajiyar su a domin ta yau so yake ya ƙalato su ya yiwa Siyama kyautar su wataƙila sa wanke mata zuciya su samar mata da nutsuwa a cikin hakan babu laifi domin ita ma ta cancanta.

"viens chérie yaya ki ke faɗin hakka ? Me yassa za ki ce bani ƙamnar ki ? Bani ƙamnar ki na amre ki har mun ka haihu ? Ina son ki mana Siyama...

Zame hannun ta tayi tana girgiza kai lokaci guda tayi wani murmushi mai ciwo muryar ta da 'yar dariyar baƙin-ciki tace .

"Kar ka jefe ni da kalmomin aro domin shi kayan aro ai basshi rufe katarar mai su , wannan kalmar ta so ba tawa ce ba ban taɓa samun ta ba ga gurin ka kai tsaye sai ko dan alfarma bani son jin ta domin ba'a halicce ta a zuciyar ka a domin ni ba .

Saƙare yayi yana kallon ta wata irin kunyar ta ya ji a lokacin tana tasowa tana danne shi har yana jin kamar bai iya numfashi mai kyau .

Ganin yayi shiru ya sa ta miƙewa bayan ta kashe laptop ɗin ta ta tura gefe , wani irin ciwo zuciyar ta ke yi so take ta samu waje tayi kuka yadda ya kamata .

Sai dai kafin ta ɗaga ƙafa ta bar gurin ya jawo hannun ta da ƙarfi ta taho gaba ɗaya ta faɗa masa yayi mata kyakkyawar runguma a ƙirjin sa .

Kukan da yake cin ta a rai shi ta samu damar yi ta shiga rairawa har jikin ta na tsuma .

Biyamuradi Youssoufa ya kasa cewa kome illa rungume ta da yayi tsam yana jin yadda kukan ta ke ratsa jijiyoyin jikin sa suna tsinka masa gudun jini tare da É—arsa masa wani irin yanayi mai kama da tsoro-tsoro a cikin ran sa "tsoro yake ji na É—aukar hakkin ta , tsoro yake kar Allah ya kama shi da laifin rashin adalci a tsakanin Matayen sa .

Sai da tayi kukan ya ishe ta har ta fara lafawa dan kan ta sannan ya kai hannu a hankali ya riƙo hannun ta ya ɗora shi a saitin ƙirjin sa muryar sa can a ƙasan maƙoshi yace .

"Kin ga nan , kin ji yadda zuciyata ke tsanan ta bugu a halin yanzu ? Akan ki ne Siyama tuhuma ta take yi meyasa na ɓata miki Siyama ? Zuciyata na ganin GIRMAN ki ke ABAR GIRMAMAWA kike a gareni , ina jin Kunya idan na ga na ɓata miki Siyama a nan duniya cikin 'ya'ya mata wace ta samu ƙima da girman matsayi kwatankwacin naki a gurina Siyama ? Amsar ita ce babu.'

" Yakanar ki ta sayo miki mafi É—aukakuwar daraja a gurina shin ba za kiyi alfahari da hakan ba ?

A hankali ta ɗago kan ta daga cikin ƙirjin sa tana jin yadda ruwan hawayen ta ke ƙafewa zuciyar ta ke tsantsamewa kunnuwan ta ke buɗewa .

Kallon da take masa kallo ne na irin " sake faÉ—a na ji ? Da gaske kake ?

Da hannunwan sa biyu ya riƙo fuskar ta yana jin yanayin da yake ji a game da ita na sake ninkuwa har yana neman fin ƙarfin sa so yake kawai ta yarda da abunda yake faɗa mata .

"Siyama zuciya ta na girmamaki gangar jikina kuma na buƙatar ki ke ɗaya ce ke da wannan matsayin a guri na da alƙawari na miki watta ba zata samu gurbi ya irin na ki ba , watta ba zata ɗau wannan matsayin ba ki yarda da ni .

Ɗan bakin ta da ya faɗaɗa da murmushi yake motsawa da son cewa wani abu shi ya rufe domin a lokacin baya buƙatar tace wani abu .

"So , ƙauna , haƙuri , Yakana da kawaicin da ta kwashi shekaru tana gwada masa sun riga sun masa gamsarwar da bai buƙatar ta sake furta kowacce kalma a gare shi a domin wai ta maida masa martanin kalmomin sa lokaci ne yanzu yayi da ita ma zai kyautata mata gwargawdon girman da zuciyar sa ke bata .

"Ta gaza tantance a halin da take ciki tsawon lokaci ji take kamar mafarki take za ta farka , kalmar girma ta mata nawi wajen ɗauka kamar yadda zuciyar ta ta gaza wajen jurar irin farin-cikin da take ciki wanda da ɗai a rayuwa bata taɓa samun makamancin sa ba dan haka ta dunga maida masa martanin Soyayyar da yake gwada mata cikin nishaɗi da basu taɓa samun makamancin sa ba a duk zaman auren su .

"Shin me ya kai hakan martaba a ce Mijin ka wanda Allah ya umarta da ka girmama shi , da bakin sa yace shi ke girmama ka ?

"Ashe ba soyayya ce kaÉ—ai abun nema a wajen Miji ba akwai abunda yafi soyayyar girma da martaba .

"Babu shakka daga yau za ta iya tutiya da matsayin da Mijinta ya ɗora ta akai matsayin da bata taɓa tarayya da wata akan sa ba nata ne mallakin ta ita kaɗai .

"Ina ma da mata zasu fahimci hakan a duk lokacin da hagu ta ƙi su a gurin Miji suyi amfani da Dama su samarwa da kan su ramin kan su ba tare da sun nace da suyi kafaɗa da kishiya ta fanni ɗaya ba.? Da kuwa gidaje da yawa an zauna lafiya a tsakanin kishiyoyi .

Siyama ke ayyana hakan a cikin ran ta bayan bacci ya É—auke Biyamuradi Youssouf da ita kuma zallar farin cikin da take ciki a yau shi ya hana ta bacci .

A karo na biyu ta É—aga kan ta duk da cewa da duhu a É—akin so take ta sake ganin hasken fuskar sa ko da sau É—aya ne kafin bacci ya É—auke ta .

A daren yau son da take masa ya sake ninkuwa ne akan na daa har tana jin kamar ba zata iya É—auka ba .

Cikin bacci ya mayar da kan ta jikin sa ya kwantar tare da sumbatar goshin ta kafin ya cigaba da baccin sa cikin nutsuwa .

Ɗan murmushi tayi ta sumbanci ƙirjin sa kafin ta rufe ido baccin da yafi daɗi da kan sa daɗi ya ɗauke ta.

****

Abuja

Cikin satika ukun da suka biyo bayan barin Sofi Gidan Doctor Hamza wata irin Soyayya mai daɗi da shaƙuwa mai girma ne ya ƙullu tsakanin ma'auratan biyu Doctor Hamza da Yakaka .

Musamman da ya kasance daman 'yan uwan juna ne dan haka sai aka yi dace wasu daga cikin halayen su suka zo ɗaya kamar yanayin buƙatuwar halittar su da matsananciyar tsaftar su , yawan ibadar su , da rashin son hayaniyar su dan a wasu lokutan ma shiru gidan yake ɗauka suna gudanar da soyayyar su a aikace ko kaɗan basa gajiya da junan su kusan koyaushe cikin ƙoƙarin farantawa juna suke muddin dai suna tare .

A satika ukun har wata 'yar sirantatciyar ƙiba Yakaka tayi ta sake fari tayi fes da ita  , yawan gyaran da take yiwa fatar ta kamar yadda Amnee ta koya mata bayan ta haɗo ta da kayan gyaran yasa kullum jikin ta kamar bayan ƙwai luwai-luwai .

Ga ƙamshi na musamman da ya zauna mata saboda turara da take yi gaba ɗayan jikin ta da hakan shi yafi kome sa Doctor Hamza ya liƙe mata kasantuwar sa ma'abocin son kamshi.

Ga girki da kullum take yi musu masu gamsarwa da ƙara lafiyar jiki saboda har ajin koyan girki ta shiga a whtsapp na musamman da shahararriyar ƙwararriyar mai koyar da girke-girken nan kuma Marubuciya Maryam Talba ta bude take kuma jagorar azuzuwan musamman domin koyar da mata girke-girke masu gamsar da Maigida,

Tare da goyon bayan Doctor Hamza da shi ma yake jin daɗin girkin ta dan haka ya amince ta faɗa ajin Koyan girki Na chef  Maryam Talba

(wacce duk take da ra'ayin shiga ajin girkin Chef Maryam Talba duba da cewa Azumi ya gabato Uwargida kina bukatar sabbin darasi kan girke-girke domin gamsar da Maigida da iyalan ki , to kar ki ji kome yi maza ki min direct message insha Allah zan sada ki da Chef din da na san sai kin min godiya a gaba sannan babban abun farin-cikin da za ki tadda shine a kudi mai rahusa za ki fada ajin 👌sai kun zo👍)

*****

Yau ta wayi gari cike da burin gwada wani daddaɗan girkin da a jiya Chef Maryam ta gwada musu da yayi matuƙar burge ta .

Kamar yadda Chef Maryam ta kware a girke-girken mu na nan gida Nigeria har da na ƙetere ma ba'a bar ta a baya ba ta ƙware a girkin larabawa dan haka yau Yakaka tayi aniyar gwada dafuwar Maqluba wadda dafuwar shinkafa ce da kaza, dankali, ganyayyaki haɗi da sauran sinadaran girki .

Maqluba girki ne na mutanan gabas ta tsakiya wanda yake da matuƙar daɗi .

Cike da nishaɗi take aikin ta tana yi tana bin ƙira'ar Alkur'ani da ta sa a wayar ta.

Kafin ya bayyana ƙamshin sa ya sanar mata da wanzuwar sa a gurin zuwa lokacin da ya shigo kitchen ɗin ta ɗago kan ta a hankali tana jifan sa da wani tsadaddan murmushi .

"Habibi barka da tashi , gaskiya ka sha bacci.

Ta furta hakan ba tare da ta janye murmushin ta ba

Ƙarasowa yayi ya rungume ta ta baya yana ɗora kan sa a kafaɗar ta yace .

"Wafaa kin saɓa doka ta meyasa ?

Wara ido tayi tana ƙoƙarin juyowa ya hana ta a hankali ta ce

"Kayi haƙuri cikin rashin sani ne.
Chapter 257 · 0% Book details