← Book details Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 171 OF 269

Sashe 171

Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

" Yau ina ganin taɓara maigida da kukan tsarki , mene haka wata shaɓatartar da ke kin wani ɗaɗɗane ɗan mutane ƙin kalmashe shi ? O ni hauwa'u inda ranka ka sha kallo , ikon Allah 'ya'yan zamani , mu lokacin mu ina muke iya ɗaga ido mu dubi miji a gaban mutane ?

Cike da 'yar kunya doctor Hamza ya miƙe bayan ya ture Sofi daga jikin sa ,  yace ,

" Rahima bata nan ko Hajja ? A É—an sama mana abinda zamu ci please ina tare da yunwa ,

" Rahima bata nan likita , bata ƙaraso ba daga Makaranta , to babu laifi yanzu kuwa za'a samar da abinci ,sannun ku da hanya ,

Wani banzan Kallo Sofi ta jefawa Hajja tana bin bayan mijinta , cikin ranta cike da haushin kalaman Hajja , cikin ran ta tana cewa ,

"ji min tsohuwar nan da kinibibi ? Ko ina ruwanta da ni ," ? Idan har ta ce zata shiga harka ta kafin na bar gidan nan sai na ratsa mata tarbiyya ,'

" Mts
  Hajja ta saki tsaki bayan barin su falon
, "abun haushi Nama na jan kare ,  me ake da mace marar kunya da kamun kai ? Kunya ai ado ce .

Murnar labarin da Falmata ta bata na samun warakar ta ya taso yayi awon gaba da takaicin da sofi ta bata ,

*****

Washegari bayan Doctor Hamza ya shirya kai tsaye ya nufi yin abunda ya kawo shi garin .

Bayan ya je sun gaisa da Prof shi da Sofi , daga bakin mashigar sashin Prof ya dakatar da ita daga binsa ,

" Sofi ki koma ciki , ni fita zan yi sai na   dawo ,

Zunɓur-ɓur ta turo baki ,
   Cikin salon da koyaushe take amfani dashi idan tana gaban shi na ƙoƙarin ta nuna masa ƙuruciyar ta da a zahiri ta riga ta yi mata adabo ,
        A shagwaɓe tace

"Haba mana Doctor please zan bika mu tafi tare naga gari , ka ga fa irin yanayin gidan shiru ba...

"please Sofi kar ki ɓata min lokaci a banza ai kin san yanayin gidan babu abokin hira kika dage sai kin biyo ni , kuma ni wajen aiki zan tafi ba yawo a gari ba ,

  Juyawa yayi ya ƙarasa ga motar sa ya shige ciki bai ko sake waigowa ta kan ta ba ya tada motar yayi tafiyar sa ,

" jagale ! Tayi a tsaye ranta cike da ƙuna ,
    "so take ta san meye Doctor yake ƙullawa a garin da yake ta zirga-zirga a tsakanin Maiduguri da Abuja ,

Cikin wata guda wannan ne zuwan sa na uku , ita fa duk wani abu da zai sha gaban ta , ya mata katanga kome ƙanƙantar sa da Doctor Hamza yaƙi take yi da koma menene ,

Ko aikin sa dan bata da ikon hana shi ne amma da tuni ta shata layi tsakanin su , so take koyaushe ya zama bashi da uzuri sai nata ,

A fusace ta juya ciki ,

****

Kai tsaye gidan Amne ya nufa , ya taddata tana karin kumallo da Fankaso da miyar gandar ƙafar sa ,

Ya gaishe ta cike da ladabi , ta amsa tana mai farin-cikin ganin sa ,

Tambayar sa tayi ya safiyya ?

Ya shaida mata ai tare suka zo garin .

"Shine kuma baka kawo min ita mun gaisa ba ?

Ta furta haka lokacin da take zuba masa miya akan fankason da ta zuba masa ,

"Amnee fita zamu yi tare zuwa wani waje ,

Ya furta haka lokacin da yake kai lomar farko bakin sa.

" ina kuma zamu ? Allah yasa dai Lafiya .

"lafiya lau Amne sai Alheri ,

cikin nutsuwa ya gama cin abincin sa ,

Bayan ya wanke hannu , yace

"Amne zamu iya tafiya yanzu ko kina da wani uzurin da zaki yi ?

"ba abunda zan yi , amma tukun wai ina zaka kai ni ? Kaƙi sanar da ni .

"kiyi haƙuri Amnee mu je ki gani ,

"to bari na yafa mayafi na ,

Tare suka fito shi da ita ya buÉ—e mata gidan baya na mota ta shiga ya rufe , gami da zagayawa ya shiga ya tada motar yana barin unguwar ,

Ya riga ya gama tsara hanyoyin da zai bi domin ganin ya dai-daita lamarin iyayensa , wanda daman burin sa ne tun ma kafin bayyanuwar Khaalty Rahima a gare shi ,

Bayyanar ta ya sauƙaƙa masa lamarin , ya kuma ji daɗi domin yasan dawowar ta a dai-dai lokacin matakin nasarar gyaruwar kome ne wanda hargitsewar kome yake da nasaba da ita ,

Bayan duk lallamin da yayi mata akan  ya mayar da ita gida , amma taƙi amincewa ,

Cikin dogon nazarin da yayi ya yanke shawarar haÉ—a su kitsumun , ba tare da sanin kowaccen su ba .

Dan haka a yanzu da ya É—au Amnee kai tsaye ya nufi gidan da Khalty Rahima take ba tare da ya sanar da kowaccen su game da 'yar uwarta ba .

Suna 'yar hira shi da Amnee har suka iso ƙofar gidan , ya fita a motar ya nemi iznin shiga gidan daga maigadi inda ya amince nan take har ma yake sake jaddada masa , ai kuwa Mamar Bulama tana ,

Tare da Amnee suka shiga wacce take cike da mamakin ina Hamza ya kawo ta ? Gurin wa suka zo ? Allah dai ya sa lafiya ,

Shi ya fara shiga sashin da Khaalty Rahima take , daga bakin ƙofa ya dogare ,  yana fuskantar Cikin gidan

daga inda yake yana hango Khaalty Rahima wacce ta duƙufa yin wanki daga gefe ,

Babu Alamun ta san da tsayuwar sa a wajen ,

"Bissmillah Amnee shigo ,

" Assalamu Alaikum ,

Amne ta ce lokacin da ta shigo filin gidan ,

Dai-dai da É—agowar Khaalty Rahima wacce sautin Hamza ya ankarar da ita tsayuwar shi a wajen ,

Zuciyoyin su suka buga da wani irin yanayi mai girma , daga ƙasa har sama Amnee take kallon ta ,

Kowanne irin jirkituwar halitta ce ta samu Rahima ƙanwar ta , ba zai sa ta gaza gane ta ba ,

"Rahma,  Rahmatullah ,

Ta ƙira ta da wani ɗan guntun sauti ,

"Rahmatullah hal hdha haqiqiun lak 'Yaa ukhtee ? ( shin dagaske ke ce 'Yar uwata ? )

A hankali ta saki rigar hannun ta da take wankewa  ,

Da hannu biyu Amnee ta rufe fuskar ta lokacin da hawayen farin-ciki ya fara zarya akan fuskar ta ,

Bata jira ƙarasowar Rahima ba wacce take tahowa da sassarfa , ta taka da sauri ta tadda ta ,

Rungume juna suka yi hawayen murnar ganin junan su na sauƙa ,

Khaalty Rahima bata san haka take cikin maricin tare da kewar 'yar uwar ta , yayar ta , madadin uwa agare ta ba sai yanzu da ta gan ta tsaye a gaban ta bayan tsawon shekaru fiye da ashirin da suka kwashe basa tare .

Hannu biyu Amnee ta sa ta riƙe fuskar Rahima ,

"ke ce wannan Rahimatullah ? Meyasa kika tafi kika barni ? Kina garin nan Rahimatullah duk tsawon shekarun nan bakya nema na ? Meye na miki mai girma haka Rahimatullah  ?

"Rahimatullah wacce irin Rayuwa kike yi tunda kika barni ? Nan ne gidan ki ? Kin yi aure ne ? Ina maigidanki ? ki min magana mana ƙanwata

Muryar Doctor Hamza ta ratsa tsakani , shi da kansa ƙwalla ta taru masa a ido , irin ƙaunar da yake hangowa a fuskar kowaccen su ga 'yar uwar ta , ta masa yanayi da na yaran nan biyu 'yan gudun hijira .

"Amnee ki kwantar da hankalin ki , Khaalty Rahima ta gamu da larura tana jin magana amma bata iya mayarwa ,

Sabon Kuka Amnee ta fashe da shi ,

"Rahimatullah ce ta kurunce ? Meye haka ya faru da ke Rahimatullah ?

Cikin ruÉ—ani ta waiga ga Hamza

" mu tafi asibiti a duba min ita yanzu Rahimatullah Amana ce a wajena ,

Da sigar rarrashi khaalty Rahima ta jijjiga hannun Amnee da yake cikin nata ,

Waigowa tayi tana kallon ta ,

Murmushi tayi mata , ta kai hannu ta goge mata hawaye tana girgiza mata kai ,

ƙoƙarin taro ta Amnee take lokacin da ta ga tana ƙoƙarin tsugunnawa ,

tare suka durƙusa ,

Khaalty Rahima ta rubuta mata a ƙasa cikin yaren su ,

"ki daina kuka , murna yakamata muyi da sake ganin junan mu Yaa Amina .

Bayan Awanni biyu

Doctor Hamza , tare da Amnee da Khaalty Rahima da Bulama suka kama hanyar komawa gidan Amnee.

Ga mamakin Hamza Khaalty Rahima bata yiwa 'yar uwarta irin tirjiyar da tayi masa kan komawa gida ba ,

Ko daman dan bata ga 'yar uwar tata bane a gaban ta ?

abunda ya ɗan riƙe su a gidan shine batun tafiya da Rahima da ɗan ta da suka yi wanda da farko matar da khaalty Rahimar take yiwa aiki bata Amince ba .

sai da suka bata gamsassun bayanai tare da ƙwararan hujjoji ta kuma ga shaida tare da Amincewar ita kanta Khaalty Rahimar tukun ta yarda ta sallami Rahima tare da yi mata fatan Alheri .

Da shigar su gida Amnee ta shiga hidimar Khaalty Rahima , kama daga shirya mata wajen zama na musamman har zuwa gyara mata shimfiÉ—ar da zasu kwana ita da É—an ta.

Abunda ya sake bawa Hamza tausayi shine duk inda Amnee ta gusa , Khaalty Rahima zata matsa kusa da ita tana yunƙurin karɓe aikin da take yi , Amnee taƙi sakar mata ,

banda murmushi mai cike da tarin ƙauna da tausayi babu abunda suke yiwa junan su .

Sai da Amnee ta gama gyara musu waje tsaf sannan ta dawo ta zauna kusa da Rahima , ta riƙo hannun ta tace ,

"Rahimatullah ina son jin labarin yadda kika yi rayuwa bayan barin ki gida , amma babu dama a yanzu , inshaAllah daga gobe zaki fara ganin likita ,

Gyaran murya Doctor Hamza yayi ,

"Amne

Ya ƙira sunan ta , a hankali ta waigo gare shi ,
Chapter 171 · 0% Book details