Sashe 255
Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yana murmushin da yake bayyana farin-cikin da yake ciki ya dubi Falmata wacce itan ma shi take kallo tana jiran ya zubo mata abincin da jin ƙamshin sa kaɗai duk ya bi yasa yawun ta ya tsinke wata bijirarrar yunwa kuma ta fara sasuƙar ta da yasa ta tuno da rabon ta da abinci tun tattaciyar madarar da ta sha da safe bata ci wani abin kirki ba ga shi yanzu gefen azahar .
"Fatima kin zama 'yar gatan Umma kullum cikin kwasar gara kike bayan saƙonni gaisuwa da girmamawa da suke isko ki a kullum anya kouwa baki haye min ƙaraga ta ga wajjen ta ba ?
Dariya tayi har gajerun haƙoran ta na bayyana kafin ta ce " ai kada kayi kokonto Biyamuradi yanzu ni ce ke da Umma .
Yunƙurawa tayi zata miƙe da sauri ya taso ya kama ta suka tako tare zuwa gaban abincin bayan ta zauna ya jingina mata pillow daga bayan ta tana ɗan sake bajewa .
Da hannu take gwada masa waɗanda take so yana zuba mata , lokacin da ya gama wani cokalin daban ya ɗauka zai bata a baki fahimtar hakan da tayi yasa ta karɓe plate ɗin daga hannun sa da sauri '
ba zata iya jurar yunwar da take ji ba , bare har ta iya jira a ciyar da ita bayan tayi Bismillah cikin nutsuwa ta sanya hannu ta ta fara ci .
Daɗin abincin na ratsa ta yana dasa mata ƙaunar uwar Mijin ta da ta fahimci tunda abun nan ya faru ya wuce baki ɗaya ta sauya duk wata rashin kulawa da rashin ƙaunar da take gwada mata sun juye sun rikiɗe sun koma tsantsar kulawa da nuna ƙauna a fili .
Tun faruwar lamarin da rashin lafiyar da tayi har ta samu sauƙi cikin sati guda kuma ta tare a sabon sashin ta da ta zo ta tarar da shi a shirye tsaf cike da kayan alatu irin na saraki da Biyamuradi ya tabbatar mata da cewa Maimartaba ne ya mata kome har sai da tayi hawaye cikin ran ta kuwa ta dunga miƙa godiyar ta ga Allah da idan ba shi ba babu mai ɗora misuƙa miskiniya irin ta a matsayin da take a yau babu shakka Allah shine abun godiya .
Bayan Hajja da take taya ta zama an haɗa ta da bayu mata biyar masu hidima kaɗai a sashin ta duk da cewa ba girki suke mata ba sai fa aiyukan shara da goge-goge ,wanke-wanke da sauran ƙananun aiyuka .
Abincin ta daga Sashin Hajiya Umma yake tahowa ita ta hana ta cin kowanne abinci sai fa na sashin ta har zuwa lokacin da zata haihu sannan ta sauwaƙe mata zuwa gaida ta kullum ta ce ta dunga sanya kwana ɗaya a tsakani saboda tayi nawi kuma da 'yar tazara a tsakanin su Hajja ita ke zuwa kai gaisuwa kullum.
Tana tunanin zuci bata san ta cinye abincin ba sai da ta laluba ta ji ba kome sai 'yan tsirarun shinkafa.
Ta ɗago kan ta a hankali ta dubi Fuskar Youssouf wanda ya rafka tagumi da hannu biyu yana mata kallo mai ruwa biyu , zallar ƙaunar ta da kuma tausayin halin da take ciki .
A kunyace ta ɗan yi murmushi kafin tayi magana ya riga ta da cewa "kin ƙoshi ? Bai jira amsar ta ba ya kai hannun sa ya goge mata gefen bakin ta da miya ta ɗan sauƙa.
"Mon Bébé kin ƙoshi ?
Ya sake tambayar ta
" Na ƙoshi Baban Mama ta furta tana ƙoƙarin tashi shi ya taimaka mata ta wanke hannun ta .
Tare suka zauna yana maƙale da ita ko yaya ta motsa yana mata sannu tare da gwada mata So.
ƙiran Sallah da akayi shi yasa shi sallama da ita bayan ya fita kai tsaye sai da ya shiga sashin Siyama da tun asuba rabon shi da ita saboda girkin Falmata ne
A zaune ya same ta an yi mata zanen ƙunshi a fararen ƙafafun ta tana jiran ya bushe ta wanke .
Daga inda yake yana iya hangen jelar ƙananun kitson da aka mata da suka kwanta har a kafaɗun ta 'yar doguwar fuskar ta ta sake fitowa sai ƙyallin gyaran jikin da ta samu take yi .
Ba tare da ya zauna ba yake amsa gaisuwar da Siyamar ke yi masa bayan sun gama gaisawar ya ɗan yi murmushi kafin ya ce "wannan ƙwalliyar du ta tafiyar ce ? Ko kouwa tawa ce ?
Ɗan wara idanun ta tayi sai kuma tayi dariya cike da jin daɗi da ɗoki ta ce "ƙwalliya taka ce Baban Yumna kamar yadda tafiyar ma take taka domin kai .
Ɗaga mata gira yayi yana juyawa akan ƙafafun sa yace "idan hakka ne ayi shiri da kyau a kouma gama bisa kan lokaci doumin kamar yadda na faɗi gobbe kafin hantsi ya ɗagga zamu tai da yardar Allah .
"To Insha Allah ba zan makara ba.
Ta furta hakan tana bin bayan sa da kallo wani irin farin-ciki na ratsa ta sanin da tayi gobe iwar haka daga ita sai shi a wani yanki .
Daren ranar kusan raba shi suka yi Youssoufa yana aikin rarrashin Falmata da shima kawai daurewa yake yi amma har cikin ran sa yake jin rabuwar da zasu yi.
Dan dai babu yadda zai yi ne a cikin halin da take ciki ba zai yiwu ya ɗauke ta su tafi bariki ba can wata jahar da babu kowa nasu ko shi da kansa ba zai so hakan ba bare ma kuma Hajiya Umma da Maimartaba sun riga sun gama magana akan ya bar ta anan gida har ta haihu abunda ta haifa yayi ƙwari kafin ta fara bin sa jahar da yake aiki .
****
Washegari.
Duk yadda Falmata ta so ta ɓoyewa Siyama damuwar ta lokacin da ta shiga sashin ta domin yi mata Sallama kasawa tayi .
Idanun ta suka tara ruwan hawayen muryar ta na ɗan rawa tace "Maman Yumna zan yi kewar ku ke da Yumna sosai dan Allah ki dunga ƙirana Appel vidéo .
Riƙe hannun ta Siyama tayi cikin ran ta tana yabawa ƙwarai da juriyar da ta gwada na ɓoye mata ainahin dalilin damuwar ta , cike da rarrashi tace "ma petite soeur mu ma za muyi kewar ki amma kar ki damu kullum za mu dunga yin waya dan Allah kar kisa damuwa a ran kin san ba'a so ki zauna cikin damuwa a halin da kike ciki ko ?
"A hankali ta gyaÉ—a kai tana jin yadda zuciyar ta ke matsewa kamar zata fashe .
Murmushi Siyama tayi mata tana É—an jaan hannun ta tace " to tashi ki zo ki mana rakiya le chauffeur ya zo za mu tai yanzu .
ÆŠan jimm tayi tana jin wani yanayi marar daÉ—i na ratsa ta tayi zaton Youssoufa zai sake shigowa suyi wata Sallamar bayan Sallama bayan da Sallamomin da suka dunga yi tun daga jiya har wayewar garin yau da safe kafin ya shirya ya fita daga Sashin nata inda ya kwana .
"Maman yumna bari na É—auko Mayafi na.
Tace tana zame hannun ta daga nata ta nufi É—aya daga cikin É—akunan ta '
Bayan shigar ta ɗakin bata jima ba ta fito hannun ta riƙe da wata Paper-bag.
Bayan ta ƙaraso sai ta miƙawa Siyama ,muryar ta da rauni ta ce "Maman Yumna ga tsaraba ta nan kiyi amfani da kayan ciki.
Murmushi Siyama tayi kafin ta sanya hannu ta karɓa tana ɗan leƙen cikin jakar ta ce "ma petite soeur kyauta ce hakka anka min ? Na kouwa gode miki ƙamna ta Allah shi bar ƙauna a tsakani.
"Amin .
Falmata ta amsa tana Murmushin yaƙe .
A bakin mota suka tarar da Biyamuradi Youssouf yana riƙe da hannun Yumna yayi shirin sa tsaf cikin kakin sa na soji da yake matuƙar amsar jikin sa .
Tun da Falmata ta samu lafiyar idanun ta yau ce rana ta farko da ta gan shi sanye da kakin soji sai ta shagala wajen kallon sa yadda yayi mata kyau ji take kamar ta ruga da gudu ta rungume shi a ƙarshe kuma ta hana shi tafiya ya zauna a gaban ta tayi ta kallon sa haka tana miƙa godiyar ta ga Ubangiji Youssoufa Namiji ne da kowacce mace zata so ta mallaki irin sa a fagen kyaun suffa da cikar zati irin na cikakken ɗa Namiji yayi zarra .
Shi ɗin ma ita ya zubawa ido a tun fitowar su yana nazarin damuwar da take danƙare a fuskar ta wanda a take ya ji tana kassara masa gaɓɓai da a zahiri ma dan haka ne ya ƙi shiga sashin nata yayi mata bankwana saboda yana tsoron abunda ka iya biyo bayan hakan wataƙila ma ya fasa tafiyar .
Gyaran muryar da Siyama tayi yasa Falmata tayi saurin ɗauke ganin ta daga kan sa tana yin ɗan baya kaɗan ta riƙo hannun Yumna wacce ta baro Baban ta ta dawo wajen Mamar ta .
"Yumna zan yi kewar ki sosai , ta furta hakan tana shafa kan ta .
Mayar da ganin ta tayi sashin da Siyama take tsaye "to Maman Yumna Allah ya kiyaye muku hanya dan Allah idan kun isa ki sanar min .
"Nima zan yi ƙewar ki ƙamnata Amin nagode sosai dan Allah ki kula muna da kan ki da bébé mu .
Gyaɗa kai Falmata tayi tana mayar da ƙwallar da take ji tana cika mata ido taƙi yarda ta sake kallon Sashin da Biyamuradi yake tsaye duk da cewa tana jin idanun sa na yawo a kan ta.
chauffeur ya buɗe ƙofar motar Siyama da Yumna suka shiga ganin haka yasa a hankali ta juya tana ɗaga takun ta dan barin wajen.
" Fatima .
ya ƙira sunan ta .
Chak ta tsaya ba tare da ta jiyo ba , ɗan taku yayi ya matso kusa da ƙofar motar cikin amon sa mai ƙarfi yace "je t'aime tellement Et tu me manqueras.
Har cikin ran ta ta ji kalmomin sa a hankali ta runtse idanun ta hawayen da suka cika gurbin idon suka gangaro kan ƙuncin ta .
"Fatima kin zama 'yar gatan Umma kullum cikin kwasar gara kike bayan saƙonni gaisuwa da girmamawa da suke isko ki a kullum anya kouwa baki haye min ƙaraga ta ga wajjen ta ba ?
Dariya tayi har gajerun haƙoran ta na bayyana kafin ta ce " ai kada kayi kokonto Biyamuradi yanzu ni ce ke da Umma .
Yunƙurawa tayi zata miƙe da sauri ya taso ya kama ta suka tako tare zuwa gaban abincin bayan ta zauna ya jingina mata pillow daga bayan ta tana ɗan sake bajewa .
Da hannu take gwada masa waɗanda take so yana zuba mata , lokacin da ya gama wani cokalin daban ya ɗauka zai bata a baki fahimtar hakan da tayi yasa ta karɓe plate ɗin daga hannun sa da sauri '
ba zata iya jurar yunwar da take ji ba , bare har ta iya jira a ciyar da ita bayan tayi Bismillah cikin nutsuwa ta sanya hannu ta ta fara ci .
Daɗin abincin na ratsa ta yana dasa mata ƙaunar uwar Mijin ta da ta fahimci tunda abun nan ya faru ya wuce baki ɗaya ta sauya duk wata rashin kulawa da rashin ƙaunar da take gwada mata sun juye sun rikiɗe sun koma tsantsar kulawa da nuna ƙauna a fili .
Tun faruwar lamarin da rashin lafiyar da tayi har ta samu sauƙi cikin sati guda kuma ta tare a sabon sashin ta da ta zo ta tarar da shi a shirye tsaf cike da kayan alatu irin na saraki da Biyamuradi ya tabbatar mata da cewa Maimartaba ne ya mata kome har sai da tayi hawaye cikin ran ta kuwa ta dunga miƙa godiyar ta ga Allah da idan ba shi ba babu mai ɗora misuƙa miskiniya irin ta a matsayin da take a yau babu shakka Allah shine abun godiya .
Bayan Hajja da take taya ta zama an haɗa ta da bayu mata biyar masu hidima kaɗai a sashin ta duk da cewa ba girki suke mata ba sai fa aiyukan shara da goge-goge ,wanke-wanke da sauran ƙananun aiyuka .
Abincin ta daga Sashin Hajiya Umma yake tahowa ita ta hana ta cin kowanne abinci sai fa na sashin ta har zuwa lokacin da zata haihu sannan ta sauwaƙe mata zuwa gaida ta kullum ta ce ta dunga sanya kwana ɗaya a tsakani saboda tayi nawi kuma da 'yar tazara a tsakanin su Hajja ita ke zuwa kai gaisuwa kullum.
Tana tunanin zuci bata san ta cinye abincin ba sai da ta laluba ta ji ba kome sai 'yan tsirarun shinkafa.
Ta ɗago kan ta a hankali ta dubi Fuskar Youssouf wanda ya rafka tagumi da hannu biyu yana mata kallo mai ruwa biyu , zallar ƙaunar ta da kuma tausayin halin da take ciki .
A kunyace ta ɗan yi murmushi kafin tayi magana ya riga ta da cewa "kin ƙoshi ? Bai jira amsar ta ba ya kai hannun sa ya goge mata gefen bakin ta da miya ta ɗan sauƙa.
"Mon Bébé kin ƙoshi ?
Ya sake tambayar ta
" Na ƙoshi Baban Mama ta furta tana ƙoƙarin tashi shi ya taimaka mata ta wanke hannun ta .
Tare suka zauna yana maƙale da ita ko yaya ta motsa yana mata sannu tare da gwada mata So.
ƙiran Sallah da akayi shi yasa shi sallama da ita bayan ya fita kai tsaye sai da ya shiga sashin Siyama da tun asuba rabon shi da ita saboda girkin Falmata ne
A zaune ya same ta an yi mata zanen ƙunshi a fararen ƙafafun ta tana jiran ya bushe ta wanke .
Daga inda yake yana iya hangen jelar ƙananun kitson da aka mata da suka kwanta har a kafaɗun ta 'yar doguwar fuskar ta ta sake fitowa sai ƙyallin gyaran jikin da ta samu take yi .
Ba tare da ya zauna ba yake amsa gaisuwar da Siyamar ke yi masa bayan sun gama gaisawar ya ɗan yi murmushi kafin ya ce "wannan ƙwalliyar du ta tafiyar ce ? Ko kouwa tawa ce ?
Ɗan wara idanun ta tayi sai kuma tayi dariya cike da jin daɗi da ɗoki ta ce "ƙwalliya taka ce Baban Yumna kamar yadda tafiyar ma take taka domin kai .
Ɗaga mata gira yayi yana juyawa akan ƙafafun sa yace "idan hakka ne ayi shiri da kyau a kouma gama bisa kan lokaci doumin kamar yadda na faɗi gobbe kafin hantsi ya ɗagga zamu tai da yardar Allah .
"To Insha Allah ba zan makara ba.
Ta furta hakan tana bin bayan sa da kallo wani irin farin-ciki na ratsa ta sanin da tayi gobe iwar haka daga ita sai shi a wani yanki .
Daren ranar kusan raba shi suka yi Youssoufa yana aikin rarrashin Falmata da shima kawai daurewa yake yi amma har cikin ran sa yake jin rabuwar da zasu yi.
Dan dai babu yadda zai yi ne a cikin halin da take ciki ba zai yiwu ya ɗauke ta su tafi bariki ba can wata jahar da babu kowa nasu ko shi da kansa ba zai so hakan ba bare ma kuma Hajiya Umma da Maimartaba sun riga sun gama magana akan ya bar ta anan gida har ta haihu abunda ta haifa yayi ƙwari kafin ta fara bin sa jahar da yake aiki .
****
Washegari.
Duk yadda Falmata ta so ta ɓoyewa Siyama damuwar ta lokacin da ta shiga sashin ta domin yi mata Sallama kasawa tayi .
Idanun ta suka tara ruwan hawayen muryar ta na ɗan rawa tace "Maman Yumna zan yi kewar ku ke da Yumna sosai dan Allah ki dunga ƙirana Appel vidéo .
Riƙe hannun ta Siyama tayi cikin ran ta tana yabawa ƙwarai da juriyar da ta gwada na ɓoye mata ainahin dalilin damuwar ta , cike da rarrashi tace "ma petite soeur mu ma za muyi kewar ki amma kar ki damu kullum za mu dunga yin waya dan Allah kar kisa damuwa a ran kin san ba'a so ki zauna cikin damuwa a halin da kike ciki ko ?
"A hankali ta gyaÉ—a kai tana jin yadda zuciyar ta ke matsewa kamar zata fashe .
Murmushi Siyama tayi mata tana É—an jaan hannun ta tace " to tashi ki zo ki mana rakiya le chauffeur ya zo za mu tai yanzu .
ÆŠan jimm tayi tana jin wani yanayi marar daÉ—i na ratsa ta tayi zaton Youssoufa zai sake shigowa suyi wata Sallamar bayan Sallama bayan da Sallamomin da suka dunga yi tun daga jiya har wayewar garin yau da safe kafin ya shirya ya fita daga Sashin nata inda ya kwana .
"Maman yumna bari na É—auko Mayafi na.
Tace tana zame hannun ta daga nata ta nufi É—aya daga cikin É—akunan ta '
Bayan shigar ta ɗakin bata jima ba ta fito hannun ta riƙe da wata Paper-bag.
Bayan ta ƙaraso sai ta miƙawa Siyama ,muryar ta da rauni ta ce "Maman Yumna ga tsaraba ta nan kiyi amfani da kayan ciki.
Murmushi Siyama tayi kafin ta sanya hannu ta karɓa tana ɗan leƙen cikin jakar ta ce "ma petite soeur kyauta ce hakka anka min ? Na kouwa gode miki ƙamna ta Allah shi bar ƙauna a tsakani.
"Amin .
Falmata ta amsa tana Murmushin yaƙe .
A bakin mota suka tarar da Biyamuradi Youssouf yana riƙe da hannun Yumna yayi shirin sa tsaf cikin kakin sa na soji da yake matuƙar amsar jikin sa .
Tun da Falmata ta samu lafiyar idanun ta yau ce rana ta farko da ta gan shi sanye da kakin soji sai ta shagala wajen kallon sa yadda yayi mata kyau ji take kamar ta ruga da gudu ta rungume shi a ƙarshe kuma ta hana shi tafiya ya zauna a gaban ta tayi ta kallon sa haka tana miƙa godiyar ta ga Ubangiji Youssoufa Namiji ne da kowacce mace zata so ta mallaki irin sa a fagen kyaun suffa da cikar zati irin na cikakken ɗa Namiji yayi zarra .
Shi ɗin ma ita ya zubawa ido a tun fitowar su yana nazarin damuwar da take danƙare a fuskar ta wanda a take ya ji tana kassara masa gaɓɓai da a zahiri ma dan haka ne ya ƙi shiga sashin nata yayi mata bankwana saboda yana tsoron abunda ka iya biyo bayan hakan wataƙila ma ya fasa tafiyar .
Gyaran muryar da Siyama tayi yasa Falmata tayi saurin ɗauke ganin ta daga kan sa tana yin ɗan baya kaɗan ta riƙo hannun Yumna wacce ta baro Baban ta ta dawo wajen Mamar ta .
"Yumna zan yi kewar ki sosai , ta furta hakan tana shafa kan ta .
Mayar da ganin ta tayi sashin da Siyama take tsaye "to Maman Yumna Allah ya kiyaye muku hanya dan Allah idan kun isa ki sanar min .
"Nima zan yi ƙewar ki ƙamnata Amin nagode sosai dan Allah ki kula muna da kan ki da bébé mu .
Gyaɗa kai Falmata tayi tana mayar da ƙwallar da take ji tana cika mata ido taƙi yarda ta sake kallon Sashin da Biyamuradi yake tsaye duk da cewa tana jin idanun sa na yawo a kan ta.
chauffeur ya buɗe ƙofar motar Siyama da Yumna suka shiga ganin haka yasa a hankali ta juya tana ɗaga takun ta dan barin wajen.
" Fatima .
ya ƙira sunan ta .
Chak ta tsaya ba tare da ta jiyo ba , ɗan taku yayi ya matso kusa da ƙofar motar cikin amon sa mai ƙarfi yace "je t'aime tellement Et tu me manqueras.
Har cikin ran ta ta ji kalmomin sa a hankali ta runtse idanun ta hawayen da suka cika gurbin idon suka gangaro kan ƙuncin ta .