← Book details Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 265 OF 269

Sashe 265

Mafari Hargitsin Rayuwa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Dole tasa ya sanar da Biyamuradi Youssouf da bai kai ga sanin Matar sa na asibiti ba saboda a da so suka yi sai ta haihu kawai sai a sanar masa amma a yanzu da lamari ya yi gardama dole aka sanar masa sannan kuma aka shiga addu'a fiye da wacce ake a baya sannan aka ɗaura tukwane domin yin abinci a bayar sadaƙha duk dan Allah ya sauƙi Gimbiya Falmata Matar Yarima Youssouf lafiya .

Ganin lokaci zai tafi tare da shiga hatsarin rasa Baby ko uwar yasa likitoci suka nemi da wani makusanci ya sa hannu a shiga da Falmata É—akin fiÉ—a .

Maimartaba sarki Abdoul-azizou shine da kansa ya zo har asibitin ya sa hannu aka shiga da Falmata É—akin fiÉ—a.

Anyi aiki cikin nasara an fitar da ƙatuwar jaririyar da ba'a ce ɗiyar fari bace saboda girma zabgegiya da ita jajir mai tarin suma akai kamar an kifa mata hular gashi dan har sai da likitan da ya ciro ta ya sanya almakashi ya yanke mata gashin ta gaban kan ta sannan ta iya buɗe ido .

Babu wanda yasan da tahowar Youssoufa kawai sai ganin sa aka yi a asibitin lokacin har an gama aikin an tura Falmata recovery room.

Duk suna tsaye suna jiran a fito da ita zuwa É—akin da zasu Iya shiga su gan ta É—aya daga cikin manyan malaman jinyan ya fito ya nemi son yayi magana da Youssoufa .

Nan yake shaida masa Falmata ta farka amma kuma sai surutai take tana kuka tana ƙiran sunan wata .

Ana buƙatar idan zai yiwu waccan ɗin ta zo ko kuma a ƙira ta a waya a haɗa ta da Falmata suyi magana dan kar kuma wata matsalar ta ɓullo .

Tare suka koma cikin É—akin da take abunda ya bashi Mamaki bai wuce nunawa da Falmata tayi ita ba shi take son gani ba Yakaka yayar ta take nema .

Shi ba shi da layin wayar Yakaka amma yana da ta Baba Prof , Amnee da Mamar su da yake ƙira akai-akai yana gaishe su da baya zaton ma kawo yanzu sun san Falmatan ta haihu 

Dan haka kawai sai ya ƙira Amne Bayan sun gaisa a gurguje ya sanar da su halin da ake ciki na haihuwar Falmata bayan an mata fiɗa da kuma halin da take ciki a yanzu na neman Yakaka .

Yanayi biyu ne ya chakuÉ—uwa Amnee na farko farin-cikin haihuwar Falmata tare kuma da fargabar halin da aka ce Falmatan na ciki bayan fiÉ—a da aka mata aka cire mata 'yar .

Nan take ta tura masa number Yakaka da bai jinkirta ba ya fara ƙiran layin sai dai sau biyar yana ƙira ba'a ɗauka hankalin sa duk ya daɗa tashi ganin yadda har lokacin Falmata bata bar kuka ba .

Dan haka ya sake ƙiran Amne lokacin da ta ɗauka ma suna tsakiya da tattauna da khaalty Rahima kan haihuwar da kuma halin da aka ce tana ciki hankalin su duk bai wani kwanta ba. dan haka sai ta haɗa su da khaalty Rahima tayi masa barka ta kuma sake tambayar jikin Falmatan ?

Nan yace har yanzu tana kuka kuma Yakaka take nema sannan ita kuma bata É—aukar wayar .

Jin yadda hankalin sa ke tashe sannan ita ma tana iya jiyo kukan Falmatan da take surutai sai ta ce to bari ta tura masa layin Mijin Yakaka ya ƙira shi wataƙila suna tare amma bari a fara sanar da shi

Lokacin da ta ƙira Doctor Hamza dawowar su kenan daga Asibitin da yaga ƙiran Amnee ya ɗauka har labarin abunda ya faru ne ya je musu dan haka yayi hanzarin ɗaukar wayar sai dai bayan sun gama gaisawa sai ya ji Amnee ta ɗaura masa da wani batu kan Falmata da ta haihu da kuma halin da take ciki na kuka da neman Yakaka.'

Yana jin haka ya fahimci cewa Falmata tana da sani kan abunda ya faru da hakan ne yasa ta firgicin da take ciki a halin yanzu .

Amnee ta cigaba da faɗa masa cewa " idan har yana tare da Yakaka to Mijin Falmatan zai ƙira yanzu sai ya haɗa su suyi magana .

"To
Ya amsa kafin yayi wani yunƙuri Amnee ta katse wayar ta.'

Bai rufa mintoci biyu ba sai ga ƙira daga ƙasar Niger.

Ɗan jimm yayi kafin ya ɗaga ƙiran saboda sanin da yayi ƙiran daga Biyamuradi Youssouf ne Baban Mama .

Lokacin da ya É—aga ga mamakin sa ba kamar yadda yayi zato ba sai ya ji muryar Youssouf É—in faran-faran kamar ya san shi haka ya gaisa da shi dan haka shi ma sai ya daure zuciyar sa suka gaisa har ya masa barka .

Daga nan sai Youssouf ya nemi da ya haÉ—a shi da Yakaka , Falmata ce ke son magana da ita.

Cikin nutsuwa Doctor Hamza yace "ka kai mata wayar idan ka bata sai na haɗa su  .

"D'accord .

Youssouf ya amsa yana mai takawa ya matsa gaban gadon da Falmata ke kwance a hankali ya kara mata wayar a kunne cikin taushin murya yana shafa kan ta yace "Mon Bébé ga Yayar ki nan kuyi magana kiji sai hankalin ki ya kwanta ta ki daina kuka .

"Hello Yakaka na tace tana shiƙar kuka..

Jin muryar ta yasa Doctor Hamza karawa Yakaka wayar a kunnen ta wacce duk abunda yake faÉ—a tana jin sa amma bata san da wa yake maganar ba .

Jin sautin Falmata tana kuka yasa ita ma kukan ya zo mata sai suka dunga yi tare cikin kukan Falmata ke tambayar ta "Yakaka baki mutu ba ko ? Sofi bata kashe ki ba ? Ashe Sofi haka take muguwa azzaluma  ? Yakaka ki koma gidan Baa kawai idan Sofi ba zata bari ki rayu a gidan ba kin ji Yakaka Dan Allah ki koma Maiduguri kar watarana Sofi ta kashe min ke Yakaka idan ta kashe ki ni kuma ya zan yi.?

Doctor Hamza shi ya fara ƙoƙarin hana kukan Yakaka muryar sa a ƙasa yace " Wafaa ki daina mata kuka ta haihu ana so jinin ta ne ya dai-daita a halin da take ciki kwantar da hankali take buƙata ki rarrashe ta .

Kallon sa take yi kafin a hankali ta buÉ—i baki tace "Falmata kin haihu da gaske.? Me kika haifa muna ?

Falmata tana goge hawayen ta da bayan hannu Youssouf na taya ta tace "eh Na haihu Yakaka amma ni ban san ma me na haifa ba ban gani ba ma Ya..

Da sauri Yakaka ta katse ta tana cewa "ina abunda kika haifa ? Ki sa a kawo miki ki ɗauki abinki ki riƙe a hannun ki ki rungume ki shayar da shi arziƙi ne babba yau Allah ya miki Falmata kin zama uwa a yau Dan Allah kar ki bari abunda ki ka haifa yayi kuka a domin rashin ki a kusa da shi sa a kawo shi Alhamdulillah Alhamdulillah .

Wata irin nutsuwa kalaman Yakaka suka zo mata da shi cikin sanyi murya ta ce "To Yakaka zan sa a bani abunda na haifa yanzu amma Yakaka kina lafiya ko ? Sofi bata yi miki ciwo ba .

"Lafiya ta ƙalau Falmata , ki sa a kawo Baby nan ki sa min naji sautin numfashin abunda kika haifa Falmata .

"Ina Baby na ?
Falmata ta cewa Youssouf haka , É—an murmushi yayi yana jin daÉ—in yadda ta fara dawowa hankalin ta.

"Riƙe telephoné na amsa miki ɗiyar mu ki ganta Fatima '

Fita yayi sai ga shi ya dawo rungume da jaririyar a hannun sa da shi ma sai yanzu ya ɗauke ta a shirye take tsaf ta sha kayan  sanyi irin na alfarma tayi kyau matuƙar gaya .

ÆŠora mata ita yayi a jikin ta bayan ya É—an É—ago mata gadon sai ya zauna tana jingina da jikin sa daga shi har ita tsurawa jaririyar ido su kayi suna ganin tsananin kamannin ta da Mama kamar lokacin da aka haife ta , marabar su kawai wannan tana da girma kuma tafi Mama gashi bayan hakan za'a ce Mama ce kawai Allah ya dawo musu da ita .

A hankali ta É—ago ta sumbanci kumatun ta dama da hagu da yasa ta motsawa a hankali tana É—an yamutsa fuska irin na jarirai.

"Yakaka na É—auke ta ,Yarinya ce mace Mai tsananin kama da Mama , Allah ya dawo mana da Mama Yakaka.

Daga can murmushi mai sauti Yakaka tayi tana jin ƙaunar 'yar da bata kai ga ɗora idanu akan ta ba na samun wajen zama na musamman a cikin ran ta a lokacin ji take kamar tayi tsuntsu ta je ta gan ta ta ɗauke ta ta riƙe a hannun ta ta rungume ta a ƙirjin ta ta gwada mata ƙauna a matsayin ta na uwa a gare ta ba wai Yayar uwa ba kawai ɗiyar Falmata ɗiyar ta ce halak malaƙ .

"Allah ya raya ta Falmata , Allah ya mata Albarka , Yaa Allah yasa ta amfanar da Al'ummar musulmai ajiye wayar ki ɗaga ta ki shayar da ita anjima zan sake ƙiran ki .

"Amin Yakaka .

Daga haka Doctor Hamza ya zare wayar daga kunnen ta ya kashe kafin ya jaa ta cikin jikin sa ya rungume ta tsam suna musayar jin ciwon rashin nasu gudan jinin da suka yi .

Sumbatar goshin ta da Youssouf yayi bai sa ta janye idanun ta daga kallon fuskar 'yar ta ba da take jin wani abun da ya zarce a ƙira shi da So sannan kuma ya wuce ƙauna tasiri yana bin duk wani sarari na ran ta yana dasa wani al'amari mai girma ji take kamar ta tsaga ƙirjin ta ta sa ta .

Wai yau ita Falmata ce take riƙe da 'yar ta ta cikin ta babu shakka Allah shine mafi girman Abun Godiya "Alhamdulillahi Yaa Allah .

Ta furta hakan a sarari tana jin wata ƙwallar farin-ciki na cika mata gurbin ido .

A hankali Youssoufa ya kai hannu yana ɗauke 'yar daga jikin ta bata yi wani yunƙuri ba illa bin su da tayi da ido cikin ran ta bata mamakin yadda ya iya ɗaukar jariri saboda tun akan Mama ta san ya ƙware .
Chapter 265 · 0% Book details