← Book details Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 40 OF 269

Sashe 40

Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

shikenan dan ta ni kam baku da matsala koh cewa kika yi kar na nuna na san falmata  bazan nuna ba ,  me ma kika ce sabon sunan ta ??
    Kachallah
    Kachallah , ta maimaita
Suka haÉ—a ido gami da kwashewa da dariya , ga alama zuciyar yakaka ta samu Æ´ar nutsuwa a karon farko tun bayan barowar su garin su .

          Niamey Niger

Yau kwanakin su siyama da gnala goma sha huɗu wanda kuma a gobe ne suke da niyyar komawa maraɗi saboda hutun da ta ɗauka a wurin aikin ta gobe yake ƙarewa ,

Zaune suke a ɗakin ubboh wacce ta kama kan siyamar tana kitsewa kamar yadda ta saba yi mata tun siyamar tana ƙanƙanuwa ,har ɗan tasawar ta kafin a aurar da ubboh ,"

      Ho addah ke kouwa yaushe ne zaki bar mini kitson hittoɓe ? Haba mana adda baki ganin na girma da wannan kitson ??
     Ɗan murmushi ubboh tayi tana me kallon fuskar siyama da ta shagwaɓe fuskar ta ta jikin mudubi ,"
      Kauna ta kin kouwa san yadda kitson hittoɓe yake fidda kyauwou tare da cikar surar ki ?? Na kou jima ina faɗi miki babu kitson da ke haska ki yaa shi ina mai tabbatar miki akwai wani sirri cikin kitson ga ki riƙe shi da kyawou har gidan amren ki,"

Shiru siyama tayi domin ubboh ta fama mata ciwon da ke nuƙurƙusar ta cikin rayi ," da nazarin sauyin da ya bayyana akan fuskar ta ubboh ta tsaida kitson da ta fara yi ,"

     Ban san yauhe ne munka fara ƴar haka da ke ba kaunata ,?? Yauhe ne kin ka fara boye mini damuwar da ke a zuciyar ki ? Yanzu duniya da gaskiya siyama kina da ƴar uwa da ta fice ni ?? Tuno da kusancin da ya wanzu tsakanin mu tun tsawon lokacci shin kou kuowa dai matsayi na ya sauyu gare ki ?

  Juyowa siyama tayi ta fuskanci ubboh , fuskar ta da alamun rashin jin daɗin maganganun ubboh ,"

Kou kussa adda matsayin ki gareni wallah basshi sauyuowa , ke kou me zai sanya ki wagga irin tounani adda amm ??

   Shafar fuskar ta ubbo tayi ," cikin ranta ƙaunar siyama na sake linkuwa,

Tun zouwar ki nan wurina na fahimci kina tare da damuwa amma juyin duniya nayi da ke ki faɗi min me ke ad damun ki kin ki faɗi mini toh ƙaƙa kike so in yi da rayi na ? Shin kou kuwa dai a chan gida an ka bata miki rayi ??

     Ajiyar zuciya siyama tayi domin ta ga wannan ce damar da zata yi amfani da ita wurin fidda abun da ke boye cikin ran ta , sake marairaice fuska tare da shagwaɓe ta tayi bayan ta karya wuya ,"

    Adda amm ni kam ban san dalili guda wadda ya sa hamma youssouf ya ƙi jini na ba , tun tasowa ta nake hangen ƙiyayyar da ke mini cikin idanouwan sa
 
    Da sauri ubboh ta kai hannu ta ɗan make bakin siyamar , tare da maɗaukakin bacin rai akan fuskar ta tace ,"
    Wanne irin kalami kike haka ga ɗan ouwan ki siyama ? Shi youssouf ɗin ne basshi ƙamnar ki ? Ƙaƙa kin kai ga fahimtar hakan ,?  Ƙou kouwa shi da baki nay ya furta hakan gare ki ? yi samri ki sanar da ni ƙaƙa anka yi wagga mummunan tounani ya kai ga ɗarsuwa cikin rayin ki ?

  Hawayen da daman suna kurkusa sune suka samu dalilin ballowa da gudu akan kumatun siyama ," cikin ranta tana faɗin "ayi a ƙare yafi a bari sai gobe ,"

    Hamma youssouf bai ɗaouke ni matsayin kauna gare shi ba , har ya gaza boye hakan a gare shi Shi ɗai , sai da ta kai ya bayyana ga bayun masarauta agades , inda ya danganta ni da baƙuwa garai a gaba gare su ,"sun ka maishe ni marar muhimmanci ga har ta kai bayun sun nemi taka ni ,'

   Cikin takaicin jin abun da youssouf ɗin ya aikata ga ƴar lelen ta ubboh tace ,"
     Yi shirun ki kaunata ki kuma daina wagga mummuna tounani , youssouf yana dawouwa ya iske ni nan cikin gida na zan kuma yi masa magana , yo a rabe magirbin yakuwa ne da na rama ?? Bar ni da shi ,"
    Cikin sanyin murya da cikin ran ta ba haka ta so ba , tace
    Adda kar ki masa faɗa bissa dilili na bani son ko ƙaƙa ran sa ya baci a sanadiyya ta , bacin ran sa ba zaya dadaɗa mini ba ,"

      Cikin son fahimtar abun da ta hango tattare da siyamar ,"ubboh" tace
     Ke ko ƙauna ta faɗi min gaskiya ƙou kouwa dai son hamman naki kike ?? Kou amren dangin kike so ?

    sunkui da kan ta tayi a lokaci guda tana wani ɗan kyakkyawan murmushin da tun zowar ta ubboh take son ganin irin sa a fuskar ta , kamo haɓar ta tayi ta ɗago fuskar ta ,tana dariya tace
     "ni ƴar uwa nake gare ki bai kyautu ba ki boye min kome idan Allah ya yarda youssouf sai ya zama miji gare ki , ina bayan ameren ku ɗari cikin ɗari , ai ba domin lamurran sa da wagga ɗiyar buzouwa ya kankama ba ai da ba'a bawa dawa ba gida ba ta ƙoshi ba ," ki kauda wagga mummunan tounani naki , youssouf ɗan ouwan ki ne kuma zai zamto miji gare ki bisa yarda Allah , ki samu kusanci da shi , kin ji kou ? Ni zan yi maganar ku da hajiya umma ,"
     Cikin matsanancin farin cikin da siyama ta gaza boye shi ta miƙe bisa kan guiwar ta tare da rungume ubboh wacce ke zaune bisa bakin gadon ta na alfarma ," zuciyar ta cike da farin cikin da ta daɗe rabon ta da jin irin sa tamkar dai ubboh ta riga ta ɗaura mata aure ne da biyamuradi youssouf ɗin ,"
         Nagode nagode nagode , kawai ita ce kalmar da take fitowa bakin ta saboda ta gaza doguwar magana

Cikin sanÉ—a saÉ—af-saÉ—af gnala ta koma da baya wacce ta taho domin kawo wa siyama lamurjen da ta sanya ta haÉ—a mata , ta zo bakin kofar ta tsinkayi tattaunawar su da ta jaa hankalin ta har ta tsaya daga bakin kofar ta ji kome ,"
     Sai dai kan ta ya ƙulle ashe daman siyama ba ƙanwa take ba ga biyamuradi youssouf ??ashe kishiya take ga uwargijiyar ta ? To amma ya aka yi gimbiya maimouna bata kai ga sanin hakan ba ??
   Jikin ta har rawa yake lokacin da ta mayar da lamurjen ɗakin girki tare da komawa cikin ɗakin da aka yi mata masauki ta murza ɗan makulli , cikin ujila ta fiddo wayar ta tare da danna kiran uwargijiyar ta tana me zumuɗin sanar da ita wannan labarin , domin tun zuwan su sau uku gimbiya maimouna na kiran ta a waya tana tambayar ta ko akwai wani labari koh sun koma maraɗi ??ita kuma Tana shaida mata har yanzu suna niamey ɗin kuma bata ci karo da wani abun da ke bukatar fashin ɓaki ba ,"sai tsantsar ƙaunar da ta fahimci tana tsakanin ƴa da ƙanwar, wanda gimbiya maimouna ta gwatsale ta tare da cewa bata tambaye ta wannan ba ta kuma sake gargaɗin ta tare da jaan kunne akan ta kula da abun da ya kai ta kaɗai ,!

Sai dai har wayar ta gama karaÉ—in ta daga chan wurin gimbiyar bata É—aga ba , "tana kuma jin tsoron sake kiran ta kar tayi laifi , dan haka ta maida wayar tare da dasa zaman jiran kira daga gimbiyar ,!

        Maraɗi

Lokaci yayi  kusa da zaki iddasa aykin da kin ka faro shi saratu , koh kin manta cikin watan ga mai kamawa youssouf yake cika shekarun sa talatin cif ne ? Kou kouwa dai kin manta da abun da zai faru a ranar zagayowar haihuwar sa na cikon shekarun sa talatin ,

    Ban manta ba hajiya uwa ba kuma zan manta ba tou ƙaƙa ma za'a yi na mance wannan lokaci ?bayan shi zai zamto shiri na na karshe akan tarwatsa rayuwar safiyyah tare da duk wasu masu ƙaunar ta ??

Ke dai Allah shi kai mu karfe 23:59h na ranar goma ga wattan biyu ,"

Ni ma nace Allah ya bani ikon É—orawa !
     Kar ku manta da nunan ƙauna !

#umm'muaz
#comment
#vote
#share
[6/24, 10:58 AM] +234 701 013 7848: *©Fikrah Writers Association*

*MAFARI*
(hargitsin rayuwa)

*Umm"muaz*

*17*
Chapter 40 · 0% Book details