← Book details Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 239 OF 269

Sashe 239

Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Shiru Fadar ta ɗauka kafin cikin abunda yake ƙasa da mintuna biyu wani daga cikin manyan bayun gidan ya taho a sukwane ya yi gurfano yana kai gaisuwa kafin ya ɗora da cewa "Ran Sarki ya dade yau da alamun ɓacin-rai mai girma ga Yarima Biyamuradi domin kuwa ga shi can riƙe da bindiga a tsirarar ta ya nufi shiya......

Miƙewar da Maimartaba yayi babu shiri ita ta sa sauran 'yan Fada suka miƙe tsaye su ma su na cewa "Allah ya huci zuciyar ka jagoran Al'umma Yaa Sarkin mu mai Adalci .

Cikin É—ago taku Sarki Abdoul-azizou ya wuce gaba bayan yace "mu tai ka min jagora zuwa inda yake .

Hajiya Mama da Biyamuradi Youssouf ƙiris ya rage su ci karo a tsakanin hanyar sashin Hajiya Uwa ,

ita tana fitowa shi kuma yana ƙoƙarin shiga da sauri ta jaa baya idanun ta a waje take bin sa da kallo .

Shi ma tsare ta yayi da ido yana bin ta da wani irin kallo mai kaifi da yasa nan take laɓɓan ta suka ɗauki rawa kamar wacce take gaban alƙali .

"Kai..kai kuma la..lafiya ? Ina..ina za ka tai ?

Bai amsa mata ba ya wani irin kewaye ta ya wuce , wani mummunan bugu zuciyar ta ta hau yi ganin inda ya nufa kai tsaye ƙofar falon Hajiya Uwa .

Taƙi barin fargabar da take bin duk lakkar jikin ta tana kassarawa tayi nasarar duƙusar da hanzarin ta , ta bi shi da ɗaga takun da ta ƙara da gudu ta sha gaban sa lokacin da yake ƙarasawa gaban ƙofar ta shiga tsakani sa da ƙofar ta raba hannuwan ta cikin wata irin buɗaɗɗiyar murya tace

" Ba zaka shiga ba ka koma inda ka fito nan ba hurumin ka bane , nace ka koma.

Idanun sa da suka yi jawur ya É—ago yana kallon ta da wani irin yanayi da ya fara fita a saiti na hankalin sa ya sanya hannun sa É—aya ya ture ta gefe tayi taga-taga zata faÉ—i amma ta tokare.

Sai dai me ? Ture ta da yayi da ƙarar ɓalla ƙofar da yayiwa duka ɗaya da kafar sa ya shiga falon basu ruguza mata zuciya kamar taron mutanen da ta hango sun yi ɗango suna tahowa ba wanda halin ɗimuwar da take ciki bai hana ta gane Maimartaba , Hajiya Umma tare da kakaf 'ya'yan su da suke gida a dai-dai lokacin zuwa manyan bayu da ma ƙanana da suke danno musu baya ba .

Jin ƙarar kamar Youssoufa yana karya wata ƙofar ya sa ta runtumawa da gudu ta faɗa falon ba tare da ta damu da taron mutanen da suke iya hango duk abunda yake faruwa ba , hankalin ta a dai-dai lokacin ya kasa yarda da abunda ke shirin faruwa da ita .

Tana shiga ta riƙo rigar Youssoufa ta baya tamau ta cukuikuye shi ta hana shi shiga ɗakin da ya riga ya karya ƙofar kawai sai ta saki wani irin ihu dai-dai da shigowar Maimartaba .

"Maimartaba ka hana shi ka hana shi nace wayyo Allah na , nace ka hana shi kar ya min lahani ga rayuwa ta.

Wata irin fincika da Youssouf ya yiwa rigar sa sai da ya kai Hajiya Mama ƙasa da sauri Hajiya Umma ta tare ta cikin ɓacin rai tace

"Kai Youssoufa mene ne kake yunƙurin yi hakka ? Hala bakka cikin hayyacin ka ?

Bai saurari kowa ba sabod idanun sa daga na zuci har na zahiri a makance suke.a lokacin ƙudirin da yake gaban sa kawai yake son cimmawa .

Yana danna kai a ɗakin ya shiga yin fatali da duk abunda ya tarar a cikin ɗakin da bai wuce wasu itatuwa da wasu ƙwarrai da babu kome a cikin su ba.

Dube-dube ya shiga yi har idanun sa suka sauƙa kan wardrobe irin ta jikin gina na shekaru aru-aru .

Duk da ƙarfin da yake da shi da jarumta irin na sojin ƙwarai da kyar ya iya buɗe ta ya shiga yawo da idanun sa a ciki lokacin da Hajiya Mama ta sake yin kukan kura ta kufce daga Hannun Hajiya Umma ta faɗa ɗakin .

Idanun sa suna sauƙa akan wata ƙatuwar ƙwarya da take ajiye daɓas da duwawun ta bata wani tangaɗi ba'a ce ƙwarya bace lokacin kuma Hajiya Mama ta sake riƙo rigar sa ta baya cikin wata irin murya mai firgitarwa tace

" Kar ka taɓa , wallashi ina kashe ka idan ka taɓa .

Kalmomin ta suka sauƙa a kunnuwan Maimartaba da Hajiya Umma da suke shigowa ɗakin sauran mutane na biye da su domin kowa ya shiga ɗimuwa tare da ƙaguwa kan son fahimtar wai me yake shirin faruwa ?

Hannun sa biyu ya sa ya cicciɓi ƙwaryar yana juyowa Hajiya Mama ta jawo rigar sa da iyakar ƙarfin ta da har sai da ta ɓarke .

Ƙwaryar kuma tayi tangal-tangal a hannun sa lokaci ɗaya ya sake ta ta tafi baki ɗaya ta kwaranye a rabin jikin Hajiya Mama kafin ta kai ƙasa ta tarwatse .

Wani fitinanne wari marar daÉ—i da yake tada hankali ya cika É—akin da yasa sai da kowa ya toshe hancin sa wasu suka yi baya da sauri .

Maimartaba da yake tsaye ƙiƙam da idanu ya bi wasu kwaɗi biyu da suka fito daga cikin ruwan mugunyar sai tsalle suke suna neman wajen ɓuya .

Kafin yayi wani yunƙuri Liman da shi ma hankalin sa ya kai kan su nan take ya fara addu'a .

Chak suka tsaya suka bar tsallen yayin da warin da ya cika wajen kuma ya fara raguwa sai tsamin giyar burkutu da ya maye gurbin warin gum kai kace a tsakiyar gidan Madam Saly -fara ake .

Umarni yayiwa wasu bayi biyu da su ɗauke su su fita da su su riƙe .

Jin haka yasa Hajiya Mama da tayi suman tsaye tun lokacin da ƙwaryar ta fashe cikin wani irin sauti mai faɗi fashe da matsanancin kuka tana duban jikin ta cikin tashin hankali da wasu zuƙa-zuƙan tsutsotsi da suke yama-yama a cikin ruwan suka hau jikin ta .

Ihu ta sake kurmawa lokaci guda ta fara cewa "ku bani ruwa dan Allah kar su shige min cikin jiki wayyo Allah na shiga uku , Youssoufa Allah shi tsine maka É—an bala'i .

Jikin sa yana mazari ya taho gaban ta ya tsaya yana gyara riƙon bindigar sa yace

"ina Mata ta ?

"Ina kin ka kai min Mata ta ?

"Ina Mata ta nake tambayar ki ?

Bangaje shi Hajiya Mama tayi cikin yanayin da yake nuna ta daina fahimtar kome da gudu ta nufi hanyar fita mutane suka dare a tsorace suka buÉ—a mata hanya ta fita a guje .

Wani irin duka Youssouf ya shiga kaiwa bango da hannun sa yana wani irin huci gaba ɗaya jijiyoyin jikin sa sun miƙe yana wani irin tsuma da duk ya tsorata mutanen wajen .

Nan take hawaye ya fara sauƙa a fuskar Hajiya Umma .

Maimartaba ne ya tako a hankali ya dafa kafaɗun sa kafin ya zarce da riƙe hannun sa da har ya fara fitar da jini .

"Innalillahi wa inna ilahi raji'oon ,Lahaula wala kuwata illah billah huwal aliel azim ya fara maimaita masa cikin nutsuwa kafin ya kai hannu ya zare bindigar da yake riƙe da ita a ɗayan hannun sa .

Wani irin kuka ya fashe da shi yana damƙe hannun Maimartaba da yake cikin nasa yace " Baba me na mata ? Meyasa ta min hakka ? Itta ta ɓata min rayuwa ta tayi sanadin da suna na ya ɓaci ƙima ta ta zubbe , iyayena sun ka yi fushi da ni , Baba me na mata ?

" Ka ƙira ta ta dawo ta faɗi inda ta kai Mata ta , Ita tayi enlevé na Fatima

" Me Fatima ta mata zata badda ta ? Ina ta kai Fatima ?

Ya ƙara cewa haka da wata irin buɗaɗɗiyar muryar da tayi amsa kuwwa a baki ɗayan sashin .

Falmata da take tsakiya da yin kuka cikin tsoron ko Hajiya Mama ta turo mata Aljannu ne su kashe ta kamar yadda ta faÉ—a mata a yanzu? domin da ta shigo ta ji tana karatun Alkur'ani .

Shine ta mammake Mata baki ta ɗora da tsorata ta da cewa zata mata turen ifiritai su zuƙe jinin ta muddin ta sake karatun kur'ani .

Jin tashin muryar Youssouf yana ƙiran sunan ta ya sa ta zabura ta miƙe zafin da ya ratsa ƙafar ta ya sa ta saurin komawa ta zauna wasu sabbin hawaye na sake zubo mata .

Da rarrafe ta ƙarasa bakin ƙofar ɗakin ta soma bubbugawa da ƙarfi tana ƙiran sunan Youssouf .

Da gudu Youssouf É—in ya fito saboda shirun da wajen ya É—auka ya bashi damar jin muryar ta a kusa .

Duka ɗaya ya yiwa ƙofar ta karye da ƙiris ya rage bai faɗa mata akai ba .

Yana shiga ɗakin ya zube guiwowin sa a ƙasa ya ɗago ta "Fatima-Zahra Est-ce que ça va? Alhamdulillah , Alhamdulillah '

Wani irin kuka ta fashe da shi tana ƙan-ƙame shi kamar zata koma jikin sa cikin kuka ta fara cewa " Dan Allah ka fitar da ni anan ka mayar da ni gida wajen Mamana, waccan matar ita ce ta kawo ni nan ta kulle ni yau kwana huɗu tace min zata kashe ni ,idan na yarda nayi magana , kai ma ita ta yi ma asiri kai da Yakaka ita tayi , ita tayi muguwa ce bata da kirki ....

Jijjiga ta yayi da sigar rarrashi yace "va bien mon amour Votre protégé en toute sécurité maintenant babu abunda zatta sake iya yi miki kin ji Fatima ki nutsu ki daina kuka ? Tayi miki ciwo ? Ina yake miki ciwo ?

Ya furta hakan yana ɗaga kallon sa zuwa kan Maimartaba da Hajiya Umma waɗan da suke ganin kome kamar a shirin film wai Hajiya Saratu da suke rayuwa da ita shekara da shekaru ita ce ta yiwa ɗan su duk wannan mugun ƙullin ?.
Chapter 239 · 0% Book details