Sashe 225
Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
" Ni kaÉ—ai nake zance na Yaa Falta .
Yakaka ta furta hakan tana miƙewa ita ma ta tafi ɗauro Alwalar ta .
Washegari tun asuba masu aiki suka shiga hidimar abincin Baƙi Amnee da Khaalty Rahima basu zauna ba suna tsaye a kan su suna sa hannu a inda ya dace suna kuma gwada musu .
Kafin ƙarfe takwas illahirin harabar gidan har maƙota ya ɗau ƙamshin girki da sumfurin ƙamshi iri-iri na daga sunadaran ƙamsasa girki na mutan N'Djamena .
Mutan Niger sun ci sun gyatse sun kuma yaba sun zuba santi ba kaɗan ba domin kuwa Ɗan Malikin Maraɗi Mai ruwan kuɗi lokacin da ya gama ƙurbe shayin da aka cika masa 'yar butar shayi ( kettle ) cewa yayi " shi kuma wannan ruwan me sunan sa ? 🤔 ga shi dai yana wani zaƙi-zaƙi kamar tattaciyar zuma farar saƙa , ga kuma wani tsami-tsami da yake yi kamar matsatsen ruwan ɗan itaciyar inabi , ga kuma wani garɗi-garɗi da yake kamar ruwan zam-zam , ƙamshin da yake tashi a cikin sa ai mai samar da nutsuwa ne irin wannan idan kana shan sa kullum ai ka tsufa da ƙarƙon ka 😂
Amnee bata zauna ba ita ta shiga gyara Falmata ta sake goge mata jiki da sauran kayan gyaran jikin Amare da ya rage , kasantuwar bata iya zanen fulawa ba hakan bai hana bayan ta gama murjewa Falmata jiki ta kama kwaɓa lalle da turarurrukan ƙunshi irin nasu bayan ta jiƙa ganyen 'yar itaciyar "Sofan " ta ɗiga ruwan sa da yayi jawur a ƙwabin lallen ta ɗan ajiye shi ya jiƙu kaɗan ta kama ƙafafun Falmata ta rangaɗa mata lallen gargajiya a tafin ƙafar da kan yatsu .
Sha ɗayan rana Hajja ta iso da daman tun jiya Amnee ta ƙira ta a waya take sanar da ita batun zuwan dangin Mijin Falmata da zancen komawar su .
Da gama wayar su Hajja ta hau shiri ran ta cike da farin-cikin jin cewa Uwarɗakin zata koma ɗakin ta , daman bikin ya ƙare dan haka yau tun safe ta bi dangi ta yiwa kowa Sallama .
Prof ya nemi ganawa da Amnee tare da Khaalty Rahima bayan sun amsa ƙiran su ya tambaye su kan me da me ake buƙata da Falmata zata tafi da shi ?
Amnee tace " Baa Alaji ai lokaci ya ƙure na yin wani babban shiri sai dai kawai za'a ɗiba mata su turaren wuta a cikin na 'yar uwar ta ..
"Meyasa ita baza'a mata nata ba kada a taɓawa 'yar uwar ta kayan ta .
Prof ya katse ta , cikin kwantar da murya Amnee tace " to ai lokaci ne ya ƙure yau ne fa kawai ? Idan aka ɗibar mata kaɗan na Amfani idan ya so bayan sun tafi sai nayi waya can N'Djamena ayi mata nata a kuma ƙarowa Takwarata nata a tsanake idan Allah ya sauƙe ta lafiya sai mu tafi mata da kayayyakin ko kuwa ?
Ta tambayi khaalty Rahima . "Hakane Ukhtee ,
Prof ya ce to kayan É—aki fa da na Amfanin gida ba za'a sauya mata wasu ba ?
"duk su ma idan ta haihu sai a mata sabbi tunda yanzu tafiyar ba ta shiri bace .
"Hakane to Allah ya kai mu kafin lokacin duk za'a tanadi kome ko ke da kan ki sai ki tafi Dubai yi mata sayayya .
Godiya mai yawa Khaalty Rahima ta yi masa bai amsa ba sai cigaba yayi da cewa a cikin ku biyun waccece zata raka ta ?
'Yar Dariya Amnee tayi kafin tace " da wai ni cewa nayi ko Zainab ma tunda ita take kusa anan sai ta kawo yaran idan Mijinta ya yarda sai su tafi tare tunda ga Hajja da daman tare suke , idan ta haihu mu sai mu je .
Cike da Amincewa Prof yace
"wannan shawara ce mai kyau bari zan ƙira shi Maigidan Zainab sai na nemi iznin sa da kaina , Allah ya kai mu .
" Amin Amin , Amnee ta amsa cike da jin daÉ—i
Bayan fitowar su daga sashin Prof a harabar gidan suka ci karo da Yakaka sai kai-kawo take a mamakance Khaalty Rahima tace " ke kuma me kike yi anan ?
Da sauri ta matso tana riƙo hannun Amnee ta ɗan rangwaɗa kai sannan tace " Amnee Dan Allah zan raka Falmata Niger ɗin ? Bana son ta tafi ita kaɗai nasan duk takura zata yi a tsakanin su tunda basu wani saba ba .
Kallon kin cika sakarci Khaalty Rahima ta mata kafin tace " Da iznin wa za ki tafi ? Kin san dai da Auren ki idan kuma gaban kan ki za kiyi to ,
Mayar da ganin ta tayi kan Amnee ta cigaba da cewa
" Ukhtee mai sunan ki dai sai kina yi kina taro ta sam bata da wayo .
Daga haka ta shige ciki ta bar su a tsaye , Amnee ta dubi Yakaka fuskar ta cike da murmushi tace ," takwara kema ai Amarya ce duk yaushe aka yi bikin ki ,? Ki bari idan ta haihu sai mu tafi tare .
" Amnee kawai raka ta zan yi fa Wallahi tausayin ta nake ji ace ta sake tafiya ita É—aya , sai Hajja .
" Zainab ma zata raka ta .
Ta katse ta .
Zata sake yin wata maganar Amnee tace " ki tambayi iznin Mijin ki idan ya bar ki sai ku tafi tare .
"Ɗan tsallen Murna Yakaka tayi ta ƙanƙame hannun Amnee da yake cikin nata tana cewa "Nagode , nagode Amnee naa .
A hankali Amnee ta zare hannun ta ta wuce ciki tana dariyar rashin wayon Yakaka , ita yanzu idan an bar ta sai ta sake kwasar ƙafa ta bi Falmata ita bata tunanin gina nata gidan auren da har yanzu bata da takamaimai matsugunni a cikin sa ? Ita kenan kome na rayuwar ta zai biyo bayan uzurin Falmata ne .
Jinjina kai tayi cikin ran ta ta kasa ƙiyasto iya adadin girman ƙaunar da Yakaka take yiwa Falmata , can sashi guda na ranta dariya take dan tasan ko kusa Hamza ba zai Amince da tafiyar Yakaka Niger ba bare kuma Prof .
Bayan wucewar Amnee Yakaka tsumu tayi a tsaye , ita sai yanzu da aka ce ta ƙira Doctor Hamza ne ma ta tuna ko number sa bata da ita a wayar ta , gaskiya tana son raka Falmata Niger ɗin nan saboda ko a hanya wannan ƙatuwar matar zata nemi ɓata mata rai ta tare mata .
Zama tayi akan dan dandamalin da aka yi shukar furanni ta cikin sa tana tunanin ina zata samu layin Doctor hamza , ita dai ba zata iya tambayar Amnee ba kunya take ji , ba kuma ta son ta tambayi Rahima ko da a waya ne tasan sai ta sille ta ta mata tsiya .
Wayar Mamar su ta faɗo mata a rai tasan babu tantama akwai number sa a kai , to ko zata ɗauka ta ƙira shi kawai ma ta wayar ta ta ƙila yafi ɗagawa da wuri fiye da idan ta layin ta ta ƙira da bai san layin ba .
Da sauri ta miƙe ta shiga ciki , ta hau sama ɗakin Khaalty Rahima da sa'ar ta babu kowa a ɗakin , daga gefen gado ta hango wayar , da sauri ta ɗauka ta shiga neman sunan sa cikin jerin sunayen dake kan wayar bata sha wahala ba ta samu sunan tare da number sa .
Shiru tayi ta gagara danna ƙiran , tana son tattaro kalmomin da zata yi amfani da su wajen yi masa magana ,
Idon ta ta kai kan agogon wayar ta ga sha biyu saura tasan dai duk tsiya yanzu ya tashi a bacci duk kuwa da cewa yau lahadi ce ba aiki .
Fargaba bai rabu da ita ba ta danna ƙiran layin bayan ta kai wayar kunne ta runtse ido gam tana jin wani yanayi mai ƙarfi na shigar ta , daga can ƙasan ran ta addu'ar samun nutsuwa ta fara yi .
Wural ta buɗe idanun ta lokacin da ta ji sautin muryar computer na bata tabbacin babu kuɗin da zai isa ƙira a wayar .
Dariya tayi da ƙaramin sauti , kafin tace " kai Maman mu sai a bar ta ko meyasa take barin waya ba kuɗi ? Ita kamar ma bata wani damu da wayar ba .
Numbers ɗin ta kwafa a wayar ta , sai da ta zauna a bakin gado sannan ta danna ƙiran .
ABUJA
Daga can Sofiya ce a É—akin Doctor Hamza tana gyara gadon da basu wani jima da tashi a kai ba Doctor Hamza ya shiga wanka .
Tana gyara bargon su lokacin da wayar sa dake gefen gado ta ɗau kiɗa alamun shigowar ƙira .
Ba tare da ta dau wayar ba ta leƙa fuskar ta ga lambobi ne reras ba suna , ɗan yamutsa fuska tayi ta gatsina guntun hancin ta kafin tace "yau Sunday ma ba za ku bar mutum ya huta ba shi kenan cikin jigila tsakanin asibiti da gida yau kam rana ta ce sai na more lokutana da aka cinye na sauran kwanaki tsawon sati .
Har wayar ta gama ƙara bata ɗaga ba .
Daga can Yakaka tayi jim da waya a hannun ta , cike da tsoron kar ta dame shi ta daure ta sake danna ƙiran a karo na biyu ,
Wannan karon har Sofiya zata fice a ɗakin sai ta dawo baya , ta ɗau wayar kai tsaye ta ɗaga ƙiran tana kara wayar a kunne tace " Hello who's on the line ?
" Mukut
Yakaka ta haÉ—iye yawun firgici , jim tayi kafin tace " amm ni ce Yakaka ina kwana ? bata tsaya ba ta zarce da cigaba da cewa "ki kaiwa Yaya doctor wayar .
Ba domin Sofiya tana shakkar kar Doctor Hamza da tasan kunnen sa yana iya jiyo ta ba da ba abunda zai hana ta É—uÉ—É—urawa Yakaka zagi .
Yakaka ta furta hakan tana miƙewa ita ma ta tafi ɗauro Alwalar ta .
Washegari tun asuba masu aiki suka shiga hidimar abincin Baƙi Amnee da Khaalty Rahima basu zauna ba suna tsaye a kan su suna sa hannu a inda ya dace suna kuma gwada musu .
Kafin ƙarfe takwas illahirin harabar gidan har maƙota ya ɗau ƙamshin girki da sumfurin ƙamshi iri-iri na daga sunadaran ƙamsasa girki na mutan N'Djamena .
Mutan Niger sun ci sun gyatse sun kuma yaba sun zuba santi ba kaɗan ba domin kuwa Ɗan Malikin Maraɗi Mai ruwan kuɗi lokacin da ya gama ƙurbe shayin da aka cika masa 'yar butar shayi ( kettle ) cewa yayi " shi kuma wannan ruwan me sunan sa ? 🤔 ga shi dai yana wani zaƙi-zaƙi kamar tattaciyar zuma farar saƙa , ga kuma wani tsami-tsami da yake yi kamar matsatsen ruwan ɗan itaciyar inabi , ga kuma wani garɗi-garɗi da yake kamar ruwan zam-zam , ƙamshin da yake tashi a cikin sa ai mai samar da nutsuwa ne irin wannan idan kana shan sa kullum ai ka tsufa da ƙarƙon ka 😂
Amnee bata zauna ba ita ta shiga gyara Falmata ta sake goge mata jiki da sauran kayan gyaran jikin Amare da ya rage , kasantuwar bata iya zanen fulawa ba hakan bai hana bayan ta gama murjewa Falmata jiki ta kama kwaɓa lalle da turarurrukan ƙunshi irin nasu bayan ta jiƙa ganyen 'yar itaciyar "Sofan " ta ɗiga ruwan sa da yayi jawur a ƙwabin lallen ta ɗan ajiye shi ya jiƙu kaɗan ta kama ƙafafun Falmata ta rangaɗa mata lallen gargajiya a tafin ƙafar da kan yatsu .
Sha ɗayan rana Hajja ta iso da daman tun jiya Amnee ta ƙira ta a waya take sanar da ita batun zuwan dangin Mijin Falmata da zancen komawar su .
Da gama wayar su Hajja ta hau shiri ran ta cike da farin-cikin jin cewa Uwarɗakin zata koma ɗakin ta , daman bikin ya ƙare dan haka yau tun safe ta bi dangi ta yiwa kowa Sallama .
Prof ya nemi ganawa da Amnee tare da Khaalty Rahima bayan sun amsa ƙiran su ya tambaye su kan me da me ake buƙata da Falmata zata tafi da shi ?
Amnee tace " Baa Alaji ai lokaci ya ƙure na yin wani babban shiri sai dai kawai za'a ɗiba mata su turaren wuta a cikin na 'yar uwar ta ..
"Meyasa ita baza'a mata nata ba kada a taɓawa 'yar uwar ta kayan ta .
Prof ya katse ta , cikin kwantar da murya Amnee tace " to ai lokaci ne ya ƙure yau ne fa kawai ? Idan aka ɗibar mata kaɗan na Amfani idan ya so bayan sun tafi sai nayi waya can N'Djamena ayi mata nata a kuma ƙarowa Takwarata nata a tsanake idan Allah ya sauƙe ta lafiya sai mu tafi mata da kayayyakin ko kuwa ?
Ta tambayi khaalty Rahima . "Hakane Ukhtee ,
Prof ya ce to kayan É—aki fa da na Amfanin gida ba za'a sauya mata wasu ba ?
"duk su ma idan ta haihu sai a mata sabbi tunda yanzu tafiyar ba ta shiri bace .
"Hakane to Allah ya kai mu kafin lokacin duk za'a tanadi kome ko ke da kan ki sai ki tafi Dubai yi mata sayayya .
Godiya mai yawa Khaalty Rahima ta yi masa bai amsa ba sai cigaba yayi da cewa a cikin ku biyun waccece zata raka ta ?
'Yar Dariya Amnee tayi kafin tace " da wai ni cewa nayi ko Zainab ma tunda ita take kusa anan sai ta kawo yaran idan Mijinta ya yarda sai su tafi tare tunda ga Hajja da daman tare suke , idan ta haihu mu sai mu je .
Cike da Amincewa Prof yace
"wannan shawara ce mai kyau bari zan ƙira shi Maigidan Zainab sai na nemi iznin sa da kaina , Allah ya kai mu .
" Amin Amin , Amnee ta amsa cike da jin daÉ—i
Bayan fitowar su daga sashin Prof a harabar gidan suka ci karo da Yakaka sai kai-kawo take a mamakance Khaalty Rahima tace " ke kuma me kike yi anan ?
Da sauri ta matso tana riƙo hannun Amnee ta ɗan rangwaɗa kai sannan tace " Amnee Dan Allah zan raka Falmata Niger ɗin ? Bana son ta tafi ita kaɗai nasan duk takura zata yi a tsakanin su tunda basu wani saba ba .
Kallon kin cika sakarci Khaalty Rahima ta mata kafin tace " Da iznin wa za ki tafi ? Kin san dai da Auren ki idan kuma gaban kan ki za kiyi to ,
Mayar da ganin ta tayi kan Amnee ta cigaba da cewa
" Ukhtee mai sunan ki dai sai kina yi kina taro ta sam bata da wayo .
Daga haka ta shige ciki ta bar su a tsaye , Amnee ta dubi Yakaka fuskar ta cike da murmushi tace ," takwara kema ai Amarya ce duk yaushe aka yi bikin ki ,? Ki bari idan ta haihu sai mu tafi tare .
" Amnee kawai raka ta zan yi fa Wallahi tausayin ta nake ji ace ta sake tafiya ita É—aya , sai Hajja .
" Zainab ma zata raka ta .
Ta katse ta .
Zata sake yin wata maganar Amnee tace " ki tambayi iznin Mijin ki idan ya bar ki sai ku tafi tare .
"Ɗan tsallen Murna Yakaka tayi ta ƙanƙame hannun Amnee da yake cikin nata tana cewa "Nagode , nagode Amnee naa .
A hankali Amnee ta zare hannun ta ta wuce ciki tana dariyar rashin wayon Yakaka , ita yanzu idan an bar ta sai ta sake kwasar ƙafa ta bi Falmata ita bata tunanin gina nata gidan auren da har yanzu bata da takamaimai matsugunni a cikin sa ? Ita kenan kome na rayuwar ta zai biyo bayan uzurin Falmata ne .
Jinjina kai tayi cikin ran ta ta kasa ƙiyasto iya adadin girman ƙaunar da Yakaka take yiwa Falmata , can sashi guda na ranta dariya take dan tasan ko kusa Hamza ba zai Amince da tafiyar Yakaka Niger ba bare kuma Prof .
Bayan wucewar Amnee Yakaka tsumu tayi a tsaye , ita sai yanzu da aka ce ta ƙira Doctor Hamza ne ma ta tuna ko number sa bata da ita a wayar ta , gaskiya tana son raka Falmata Niger ɗin nan saboda ko a hanya wannan ƙatuwar matar zata nemi ɓata mata rai ta tare mata .
Zama tayi akan dan dandamalin da aka yi shukar furanni ta cikin sa tana tunanin ina zata samu layin Doctor hamza , ita dai ba zata iya tambayar Amnee ba kunya take ji , ba kuma ta son ta tambayi Rahima ko da a waya ne tasan sai ta sille ta ta mata tsiya .
Wayar Mamar su ta faɗo mata a rai tasan babu tantama akwai number sa a kai , to ko zata ɗauka ta ƙira shi kawai ma ta wayar ta ta ƙila yafi ɗagawa da wuri fiye da idan ta layin ta ta ƙira da bai san layin ba .
Da sauri ta miƙe ta shiga ciki , ta hau sama ɗakin Khaalty Rahima da sa'ar ta babu kowa a ɗakin , daga gefen gado ta hango wayar , da sauri ta ɗauka ta shiga neman sunan sa cikin jerin sunayen dake kan wayar bata sha wahala ba ta samu sunan tare da number sa .
Shiru tayi ta gagara danna ƙiran , tana son tattaro kalmomin da zata yi amfani da su wajen yi masa magana ,
Idon ta ta kai kan agogon wayar ta ga sha biyu saura tasan dai duk tsiya yanzu ya tashi a bacci duk kuwa da cewa yau lahadi ce ba aiki .
Fargaba bai rabu da ita ba ta danna ƙiran layin bayan ta kai wayar kunne ta runtse ido gam tana jin wani yanayi mai ƙarfi na shigar ta , daga can ƙasan ran ta addu'ar samun nutsuwa ta fara yi .
Wural ta buɗe idanun ta lokacin da ta ji sautin muryar computer na bata tabbacin babu kuɗin da zai isa ƙira a wayar .
Dariya tayi da ƙaramin sauti , kafin tace " kai Maman mu sai a bar ta ko meyasa take barin waya ba kuɗi ? Ita kamar ma bata wani damu da wayar ba .
Numbers ɗin ta kwafa a wayar ta , sai da ta zauna a bakin gado sannan ta danna ƙiran .
ABUJA
Daga can Sofiya ce a É—akin Doctor Hamza tana gyara gadon da basu wani jima da tashi a kai ba Doctor Hamza ya shiga wanka .
Tana gyara bargon su lokacin da wayar sa dake gefen gado ta ɗau kiɗa alamun shigowar ƙira .
Ba tare da ta dau wayar ba ta leƙa fuskar ta ga lambobi ne reras ba suna , ɗan yamutsa fuska tayi ta gatsina guntun hancin ta kafin tace "yau Sunday ma ba za ku bar mutum ya huta ba shi kenan cikin jigila tsakanin asibiti da gida yau kam rana ta ce sai na more lokutana da aka cinye na sauran kwanaki tsawon sati .
Har wayar ta gama ƙara bata ɗaga ba .
Daga can Yakaka tayi jim da waya a hannun ta , cike da tsoron kar ta dame shi ta daure ta sake danna ƙiran a karo na biyu ,
Wannan karon har Sofiya zata fice a ɗakin sai ta dawo baya , ta ɗau wayar kai tsaye ta ɗaga ƙiran tana kara wayar a kunne tace " Hello who's on the line ?
" Mukut
Yakaka ta haÉ—iye yawun firgici , jim tayi kafin tace " amm ni ce Yakaka ina kwana ? bata tsaya ba ta zarce da cigaba da cewa "ki kaiwa Yaya doctor wayar .
Ba domin Sofiya tana shakkar kar Doctor Hamza da tasan kunnen sa yana iya jiyo ta ba da ba abunda zai hana ta É—uÉ—É—urawa Yakaka zagi .