Sashe 256
Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Muryar ta na rawa ta furta "Allah ya kiyaye mu ku hanya ya kai ku lafiya Amin .
Da sauri kamar ba ita ce ke ɗauke da wannan tirtsetsen cikin ba ta ƙarasa barin wajen idanun ta a rufe da ruwan hawaye .
Youssouf da yake tsaye ji yake kamar ya bita ya riƙe ta ya hana ta tafiya amma ya san idan yayi hakan zai ɓata goma ne ɗaya bata gyaru ba .
Lokacin da ta ɓacewa ganin sa dan kansa ya shiga motar direba ya jaa suka ɗau hanyar barin-gidan suka kama hanya ɗoɗar zuwa Birnin Tahoua inda yake aiki .
Lokacin da Falmata ta koma sashin ta abu na farko da ta fara yi bayan ta ci kuka har ta bawa aku lada ta ji idanun ta sun fara raurawa suna mata alamun ciwo '
Lallaɓawa tayi ta ɗau wayar ta wacce take ji tana ta ɗaukar kiɗa da ko bata duba ba ta san Biyamuradi Youssouf ne ke kira
A hankali ta shafa wayar ta kashe tana zunɓuro baki kamar yana ganin ta tace "Na fasa yin Appel vidéo ɗin da kai .
****
Duk da cewa tafiyar bata yiwa Siyama armashin da ta so ba amma hakan bai guntule mata jin daɗi da ɗokin ta ba sai hira take yi masa wani ya amsa wani kuwa yayi shiru yana shafe-shafen waya da sarai ta lura da wacce yake faman ƙira Fatima ce .
Ko da suka isa jahar Tahoua da gefen Azahar a share a tsaftace suka tarar da gidan dan haka aikin da tayi ba mai yawa bane ba illa kayayyakin su da tayi musu ma'ajiya a muhallin da ya dace ta sake yin wasu 'yan gyararraki da ba'a rasa ba.
Kafin ta gama wani Soja da yake hidima da gidan ya zo da cefene dan haka kai tsaye ta shiga kitchen duk da cewa ba sabon ta bane yin girki amma bata gagara iyawa ba dai-dai gwargwado ta zage-damtse dan farantawa Mijin ta tayi girki mai kyau da daɗi Yumna na taya ta da ɓarna .
Youssouf kuwa tunda suka zo da aka sauƙe su shi wucewa direba yayi da shi can babban ofishin su inda zasu yi wata ganawa shi da abokan aikin sa .
Ba shi ya samu damar komawa gidan ba sai bayan isha'i lokacin da ya shiga gidan tsit babu motsin kome sai na na'urori.
bai tarar da Siyama a falon ba sai fa wani daddaɗan ƙamshi da ya shaƙa wanda take ya tado masa da tunanin Fatiman sa domin kuwa ƙamshin irin nata ne a duk inda tayi bigire nan yake jin irin ƙamshin kewar ta mai yawa ya ji tana bin jikin sa , tunda suka taho yake son ya ji lafiyar ta amma taƙi ɗaukar wayar a ƙarshe ma ta kashe ta baki ɗaya kuma tunda ta kashe bata kunna ba .
Zama yayi akan kujerar falon yana sunce igiyoyin takalman sa , bai ji tahowar ta ba sai sauƙar kyakkyawan hannun ta da yasha adon ƙunshi ya gani ta ajiye akan hannun sa ta karɓe kunce takalmin da ya fara .
Sakar mata yayi yana bin jikin ta da kallo da ta sha ado da wata bugaggiyar shadda Boo ɗinkin bubu tayi ɗaurin ɗankwali mai ban sha'awa jelunan kitson ta da ta haɗa ta tufke ta haɗe cikin ƙaton ribbon ya taimaka wajen ɗago da ɗaurin daga ƙasa sai ya zauna ɗas a kan ta kamar hula .
"Siyama ma'abociyar kwalliya ce , daga can ƙasan ran sa ya aiyana haka .
Yana kallon ta har ta gama ta É—ago fuskar ta da bata cika fente-fente ba tana masa murmushi ta ce "Bienvenue mon amour et comment va le travail? Sannu.
Fuskar sa a sake da taƙaitatcen murmushi yace "ke za'a wa Sannu Maman Yumna da hidmar gida da kaɗaici , ɗakin taro mun ka hige sai yanzou munka kai ga hittowa.
bata amsa ba ta miƙe da ɗan murmushi a fuskar ta ta wuce ɗaki daga can ta haɗa masa ruwan wanka .
Ya shiga yayi bayan ya gama ya sako ƙananun kaya da basu cika nawi ba a jikin sa ya fito
Daga nan abinci ta kawo suka ci tare bayan sun gama ta tattara wajen ta dawo ta zauna daga gefen sa suna kallon TV tare duk da dai ita ba wani jin daÉ—in kallon take ba saboda tashar labarai ne shi yake ganin kayan sa .
Lokacin da ta ga ya ɗau waya sa sai da zuciyar ta ta doka tana satar kallon sa ta ga ya fara ƙira bugu ɗaya biyu , daga can ta ji computer na sanar da shi wayar a kashe take chajin wayar sa ya duba ya ga saura kadan ta mutu dan haka kawai sai ya kashe wayar ya sa a chaji
yana jin duk babu daÉ—i "meyasa Fatima za ta masa wannan horon ?
"Biyamuradi
Ta ƙira sunan shi
Da ido ya amsa mata yana kallon ta .
Murmushin yaƙe tayi kafin ta ce "tunda muka zo nayi ta neman wayar ƙamnata a kashe wayar....
Kafin ta ƙarasa Youssouf ya amsa mata fuskar sa na bayyana damuwa "nima itta nake ta ƙira amma ta kar wayar ko mai yassa tayi hakan ?
"Watakila batta so ta tsare ma aiki ne , Siyama ta amsa masa tana É—an nazarin sa ta É—ora da cewa
"Amma ko za ka gouda kiran Hajja ne saboda a san halin da ta yini ciki.
"Hakka ya kamata, Amma itta telephoné na babu wutta cikin ta.
"Bari na ƙira ta da telephoné na sai ta sada mu da itta
Bugu É—aya Hajja ta É—au wayar ta tana É—an gigin bacci tace "hallo waye anan ?
Daga can Siyama ta amsa mata tana jin muryar ta ta watsake suka gaisa faran-faran ta ɗora da faɗa mata dalilin ƙiran nan take Hajja ta yunƙura ta fita daga ɗakin ta ta nufi ɗakin Falmata cewa take "kada ma ki katse ƙiran ai yanzu zan kai mata idon ta biyu dan ban jima ba ma da barin ɗakin nata bayan mun gama hira .
"Hello Maman Yumna da fatan kun isa lafiya ? daga can Falmata da ta karbi wayar ta furta
Shiru ta ji anyi "Hello ta sake cewa.
Daga can ɓangaren da tunda ta ɗaga wayar Siyama ta miƙawa Youssoufa
"Fatima .
Sautin sa ya doki dodon kunnen ta da yasa ta runtse Ido tana jin yadda gangar jikin ta ke sauyawa daga jin amon sa .
"Fatima me yassa kin ka kashe min waya unn ?
Shiru ta sake yi tana jin sa ya cigaba da cewa "kin sa na shigga damouwa , kar ki sake min ya hakka kin ji kou ?
"Fatima
"Mon bébé kina ji na ?
Sautin kukan ta ya ba shi tabbacin tana jin sa runtse ido yayi yana jin ciwon kukan nata ya fahimci Fatima tana da zafin kishi sosai da sosai da shi a ganin sa ba kome ya kawo hakan ba illa tsananin son da take masa.
Ajiyar zuciya yayi daga ƙasan ran sa ya fara harhaɗo kalaman da zai rarrashe zuciyar ta take cike da ƙaunar sa.
****
Bayan Awa ÆŠaya da Rabi:
Rarrashi ya rikiɗe ya koma hira mai cike da raha da ƙaunar juna daga ƙarshe ma suka koma video call kamar ba sa rabu ba kafin daga ƙarshe ya sake wani rarrashin kafin su yi Sallama da alƙawarin gobe za ta gan shi a vidieo call a dai-dai wannan lokacin
Zuciyoyin Su cike da nishaÉ—i da begen juna suka yi Sallama bayan sun aikawa da juna Sumba ta iska .
Sai bayan da ya sauƙe wayar ya lura da yadda dare ya shiga wajen shaɗaya da rabi na dare.
Yawo yayi da idanun sa a falon sai dai ko alamun wacce yake dubawa bai gani ba , haka kawai ya ji wani irin yanayi na bin jikin sa yana ganin rashin kyautawa kan abunda yayi musamman da ya tuno da cewa da fa wayar ta su ka sha hira shi da Fatima , "anya kana adalci ? Zuciyar sa ta ƙwanƙwashe shi.
Cikin rashin kuzari ya miƙe bayan ya kashe kayan kallon ya rufe ko'ina ya nufi ɗakin baccin su '
A hankali ya turo ƙofar cike da son kiyayewa kada ya tada su a baccin da yake hasashen suna tsaka da yin sa .
Da shigar sa yayi turus kafin ya ɗan yi duru-duru saboda ido huɗu da suka yi shi da Siyama wacce take zaune daga ƙasa ta tasa laptop a gaba da alama karatu take yi .
Murmushin da ta jefe shi da shi lokacin da take zare gilashin idanun ta bai taimaka ba ko kaÉ—an wajen rage masa yanayin da yake ji a dai-dai lokacin da shi kan sa ya gaza fahimtar ainashin wanne irin yanayi ne ? .
"Ya Fatima da Bébé ? Duk suna lahia kou.?
"Suna lafiya , ya amsa mata kafin ya zauna daga kan kujera ɗaya tal da take ɗakin yana ɗan sosa ƙeya .
"Siyama .
Ya ƙira sunan ta yana kallon ta .
Cikin nutsuwa ta É—ago kan ta ba tare da ta amsa ba
Da taimakon hasken ɗakin ya iya hango yadda launin idanun ta suka sauya su ka yi jaa kaɗan .
"Ba kiyi bacci ba har yanzou ?
Ya tambaye ta .
Wani irin murmushi mai ciwo tayi tana kawar da kan ta , muryar ta babu ƙarfi sosai ta ce " Ban yi bacci ba Biyamuradi ina jiran ka shiggo muyi Sallama.
"Siyama
Ya sake ƙiran sunan ta bai jira amsawar ta ba yace .
"Duk lokacin da kin ka ji bacci kiyi ko da ina gidan ko bana nan ba sai kin jira mun yi sallama ba...''
"Saboda me ? Ta katse shi da wata irin muryar da take tsakanin harshe da wuyan ta
Kallon sa tayi ta ga yadda ya ke duban ta da rauni a cikin idanun sa , kafin ta É—ora da cewa .
"Saboda baka sona ? Baka ƙamna ta ? Baka amre ni domin so ba ? Ni matar cushe ce gare ka ?
"Siya...
Da sauri ta katse shi lokacin da ruwan hawayen ta ke sauƙa yana ɗiga ta cigaba da cewa
Da sauri kamar ba ita ce ke ɗauke da wannan tirtsetsen cikin ba ta ƙarasa barin wajen idanun ta a rufe da ruwan hawaye .
Youssouf da yake tsaye ji yake kamar ya bita ya riƙe ta ya hana ta tafiya amma ya san idan yayi hakan zai ɓata goma ne ɗaya bata gyaru ba .
Lokacin da ta ɓacewa ganin sa dan kansa ya shiga motar direba ya jaa suka ɗau hanyar barin-gidan suka kama hanya ɗoɗar zuwa Birnin Tahoua inda yake aiki .
Lokacin da Falmata ta koma sashin ta abu na farko da ta fara yi bayan ta ci kuka har ta bawa aku lada ta ji idanun ta sun fara raurawa suna mata alamun ciwo '
Lallaɓawa tayi ta ɗau wayar ta wacce take ji tana ta ɗaukar kiɗa da ko bata duba ba ta san Biyamuradi Youssouf ne ke kira
A hankali ta shafa wayar ta kashe tana zunɓuro baki kamar yana ganin ta tace "Na fasa yin Appel vidéo ɗin da kai .
****
Duk da cewa tafiyar bata yiwa Siyama armashin da ta so ba amma hakan bai guntule mata jin daɗi da ɗokin ta ba sai hira take yi masa wani ya amsa wani kuwa yayi shiru yana shafe-shafen waya da sarai ta lura da wacce yake faman ƙira Fatima ce .
Ko da suka isa jahar Tahoua da gefen Azahar a share a tsaftace suka tarar da gidan dan haka aikin da tayi ba mai yawa bane ba illa kayayyakin su da tayi musu ma'ajiya a muhallin da ya dace ta sake yin wasu 'yan gyararraki da ba'a rasa ba.
Kafin ta gama wani Soja da yake hidima da gidan ya zo da cefene dan haka kai tsaye ta shiga kitchen duk da cewa ba sabon ta bane yin girki amma bata gagara iyawa ba dai-dai gwargwado ta zage-damtse dan farantawa Mijin ta tayi girki mai kyau da daɗi Yumna na taya ta da ɓarna .
Youssouf kuwa tunda suka zo da aka sauƙe su shi wucewa direba yayi da shi can babban ofishin su inda zasu yi wata ganawa shi da abokan aikin sa .
Ba shi ya samu damar komawa gidan ba sai bayan isha'i lokacin da ya shiga gidan tsit babu motsin kome sai na na'urori.
bai tarar da Siyama a falon ba sai fa wani daddaɗan ƙamshi da ya shaƙa wanda take ya tado masa da tunanin Fatiman sa domin kuwa ƙamshin irin nata ne a duk inda tayi bigire nan yake jin irin ƙamshin kewar ta mai yawa ya ji tana bin jikin sa , tunda suka taho yake son ya ji lafiyar ta amma taƙi ɗaukar wayar a ƙarshe ma ta kashe ta baki ɗaya kuma tunda ta kashe bata kunna ba .
Zama yayi akan kujerar falon yana sunce igiyoyin takalman sa , bai ji tahowar ta ba sai sauƙar kyakkyawan hannun ta da yasha adon ƙunshi ya gani ta ajiye akan hannun sa ta karɓe kunce takalmin da ya fara .
Sakar mata yayi yana bin jikin ta da kallo da ta sha ado da wata bugaggiyar shadda Boo ɗinkin bubu tayi ɗaurin ɗankwali mai ban sha'awa jelunan kitson ta da ta haɗa ta tufke ta haɗe cikin ƙaton ribbon ya taimaka wajen ɗago da ɗaurin daga ƙasa sai ya zauna ɗas a kan ta kamar hula .
"Siyama ma'abociyar kwalliya ce , daga can ƙasan ran sa ya aiyana haka .
Yana kallon ta har ta gama ta É—ago fuskar ta da bata cika fente-fente ba tana masa murmushi ta ce "Bienvenue mon amour et comment va le travail? Sannu.
Fuskar sa a sake da taƙaitatcen murmushi yace "ke za'a wa Sannu Maman Yumna da hidmar gida da kaɗaici , ɗakin taro mun ka hige sai yanzou munka kai ga hittowa.
bata amsa ba ta miƙe da ɗan murmushi a fuskar ta ta wuce ɗaki daga can ta haɗa masa ruwan wanka .
Ya shiga yayi bayan ya gama ya sako ƙananun kaya da basu cika nawi ba a jikin sa ya fito
Daga nan abinci ta kawo suka ci tare bayan sun gama ta tattara wajen ta dawo ta zauna daga gefen sa suna kallon TV tare duk da dai ita ba wani jin daÉ—in kallon take ba saboda tashar labarai ne shi yake ganin kayan sa .
Lokacin da ta ga ya ɗau waya sa sai da zuciyar ta ta doka tana satar kallon sa ta ga ya fara ƙira bugu ɗaya biyu , daga can ta ji computer na sanar da shi wayar a kashe take chajin wayar sa ya duba ya ga saura kadan ta mutu dan haka kawai sai ya kashe wayar ya sa a chaji
yana jin duk babu daÉ—i "meyasa Fatima za ta masa wannan horon ?
"Biyamuradi
Ta ƙira sunan shi
Da ido ya amsa mata yana kallon ta .
Murmushin yaƙe tayi kafin ta ce "tunda muka zo nayi ta neman wayar ƙamnata a kashe wayar....
Kafin ta ƙarasa Youssouf ya amsa mata fuskar sa na bayyana damuwa "nima itta nake ta ƙira amma ta kar wayar ko mai yassa tayi hakan ?
"Watakila batta so ta tsare ma aiki ne , Siyama ta amsa masa tana É—an nazarin sa ta É—ora da cewa
"Amma ko za ka gouda kiran Hajja ne saboda a san halin da ta yini ciki.
"Hakka ya kamata, Amma itta telephoné na babu wutta cikin ta.
"Bari na ƙira ta da telephoné na sai ta sada mu da itta
Bugu É—aya Hajja ta É—au wayar ta tana É—an gigin bacci tace "hallo waye anan ?
Daga can Siyama ta amsa mata tana jin muryar ta ta watsake suka gaisa faran-faran ta ɗora da faɗa mata dalilin ƙiran nan take Hajja ta yunƙura ta fita daga ɗakin ta ta nufi ɗakin Falmata cewa take "kada ma ki katse ƙiran ai yanzu zan kai mata idon ta biyu dan ban jima ba ma da barin ɗakin nata bayan mun gama hira .
"Hello Maman Yumna da fatan kun isa lafiya ? daga can Falmata da ta karbi wayar ta furta
Shiru ta ji anyi "Hello ta sake cewa.
Daga can ɓangaren da tunda ta ɗaga wayar Siyama ta miƙawa Youssoufa
"Fatima .
Sautin sa ya doki dodon kunnen ta da yasa ta runtse Ido tana jin yadda gangar jikin ta ke sauyawa daga jin amon sa .
"Fatima me yassa kin ka kashe min waya unn ?
Shiru ta sake yi tana jin sa ya cigaba da cewa "kin sa na shigga damouwa , kar ki sake min ya hakka kin ji kou ?
"Fatima
"Mon bébé kina ji na ?
Sautin kukan ta ya ba shi tabbacin tana jin sa runtse ido yayi yana jin ciwon kukan nata ya fahimci Fatima tana da zafin kishi sosai da sosai da shi a ganin sa ba kome ya kawo hakan ba illa tsananin son da take masa.
Ajiyar zuciya yayi daga ƙasan ran sa ya fara harhaɗo kalaman da zai rarrashe zuciyar ta take cike da ƙaunar sa.
****
Bayan Awa ÆŠaya da Rabi:
Rarrashi ya rikiɗe ya koma hira mai cike da raha da ƙaunar juna daga ƙarshe ma suka koma video call kamar ba sa rabu ba kafin daga ƙarshe ya sake wani rarrashin kafin su yi Sallama da alƙawarin gobe za ta gan shi a vidieo call a dai-dai wannan lokacin
Zuciyoyin Su cike da nishaÉ—i da begen juna suka yi Sallama bayan sun aikawa da juna Sumba ta iska .
Sai bayan da ya sauƙe wayar ya lura da yadda dare ya shiga wajen shaɗaya da rabi na dare.
Yawo yayi da idanun sa a falon sai dai ko alamun wacce yake dubawa bai gani ba , haka kawai ya ji wani irin yanayi na bin jikin sa yana ganin rashin kyautawa kan abunda yayi musamman da ya tuno da cewa da fa wayar ta su ka sha hira shi da Fatima , "anya kana adalci ? Zuciyar sa ta ƙwanƙwashe shi.
Cikin rashin kuzari ya miƙe bayan ya kashe kayan kallon ya rufe ko'ina ya nufi ɗakin baccin su '
A hankali ya turo ƙofar cike da son kiyayewa kada ya tada su a baccin da yake hasashen suna tsaka da yin sa .
Da shigar sa yayi turus kafin ya ɗan yi duru-duru saboda ido huɗu da suka yi shi da Siyama wacce take zaune daga ƙasa ta tasa laptop a gaba da alama karatu take yi .
Murmushin da ta jefe shi da shi lokacin da take zare gilashin idanun ta bai taimaka ba ko kaÉ—an wajen rage masa yanayin da yake ji a dai-dai lokacin da shi kan sa ya gaza fahimtar ainashin wanne irin yanayi ne ? .
"Ya Fatima da Bébé ? Duk suna lahia kou.?
"Suna lafiya , ya amsa mata kafin ya zauna daga kan kujera ɗaya tal da take ɗakin yana ɗan sosa ƙeya .
"Siyama .
Ya ƙira sunan ta yana kallon ta .
Cikin nutsuwa ta É—ago kan ta ba tare da ta amsa ba
Da taimakon hasken ɗakin ya iya hango yadda launin idanun ta suka sauya su ka yi jaa kaɗan .
"Ba kiyi bacci ba har yanzou ?
Ya tambaye ta .
Wani irin murmushi mai ciwo tayi tana kawar da kan ta , muryar ta babu ƙarfi sosai ta ce " Ban yi bacci ba Biyamuradi ina jiran ka shiggo muyi Sallama.
"Siyama
Ya sake ƙiran sunan ta bai jira amsawar ta ba yace .
"Duk lokacin da kin ka ji bacci kiyi ko da ina gidan ko bana nan ba sai kin jira mun yi sallama ba...''
"Saboda me ? Ta katse shi da wata irin muryar da take tsakanin harshe da wuyan ta
Kallon sa tayi ta ga yadda ya ke duban ta da rauni a cikin idanun sa , kafin ta É—ora da cewa .
"Saboda baka sona ? Baka ƙamna ta ? Baka amre ni domin so ba ? Ni matar cushe ce gare ka ?
"Siya...
Da sauri ta katse shi lokacin da ruwan hawayen ta ke sauƙa yana ɗiga ta cigaba da cewa