Sashe 138
Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Babu inda zaki dunga goyon ta kina tafiya da ita anan waje na zaki dunga barin ta idan ya so kafin ki dawo na sauya ta , ko kuwa na gudu da ita, kina nufin baza ki maida hankali kan karatun naki bane ? Zaki dunga ɗaukar ta kina zuwa da ita makaranta ki ɓige da raino memakon karatu ni ke meyasa ana nuna miki hanya kina daɗa bauɗewa ne ??
Æata rai tayi ta É—auke kai
Murmushi youssouf yayi , shi dai rigimar hajja da falmata na ba shi dariyaÂ
Duba fatima ki bar mama a wajen hajja har ki tai école ki dawo Kin ji kou ? Ba'a tafiya da yara école.
Shiru tayi idanun ta na kawo ƙwalla ita dai bata ƙaunar abunda zai raba ta da mama ko na ƴan mintoci ne bare fa makaranta da awanni zata yi a can , kai anya zata iya , ?
To hajja mu dunga zuwa tare da ke mana makarantar ? Sai ki dunga riƙe min mama nayi karatun na fito ?
Ke raba ni da wannan gudun birin , gotai gotai da ni zani makarantar ? Yaushe rabon duniya da ayyaraye ? Babu inda za ni ke kaɗai zaki tafi makarantar ki ki dawo ki same ni ina nan , ilmin ai shine Babban gatan ki falmata kin ji ko ?
Naji hajja
Yauwa mutuniyar ai shiyasa nake son ki akwai ki da saurin fahimta ,
Sallama suka yi da youssouf yana sake yiwa hajja godiya me tarin yawa tare da ɗanka mata ƴan kuɗaɗe wanda da kyar hajjan ta yadda ta karɓa sai da yayi ta roƙon ta da Allah .
Daga nan Dosso yayiwa tsinke bai jin marmarin zuwa maraɗi duk da cewa fiye da kaso talatin na ɓacin ran sa game da sha'anin sa da gimbiya maimouna ya kau , domin har sun yi waya ma cikin kwanaki biyun .
 Â
Assalamu Alaikum kowa da kowa !
Da fatan kuna lafiya ?
Ina neman afuwar ku bisa jinkirin zuwan wannan shafin , hakan ya faru ne sakamakon tafiya da ni zuwa gida , ban samu zama ba ziyarar dangi da sauran Al'amuran yau da kullum .
Da fatan zaku cigaba da haƙuri da tsaikon da ake samu cikin ajizanci irin na ɗan Adam ?
Nagode
 Â
[9/3, 10:14 PM] +234 806 122 1116: Fikrah writers association
MAFARI
( Hargitsin Rayuwa )
Umm'muaz
32
Bayan Shekaru Biyar
Lokaci baya jira sai dai a jira shi , ba'a masa shamaƙi a yayin wucewar sa , Lokaci gudu ne da shi fiye da saurin bugun zuciyar ɗan adam ,
Lokaci yayi juyi ya juya ya zo da sauyi ta mabanbantan fuskoki a rayuwar mutane a cikin tsawon shakaru biyar .
Yakaka tana ɗaya daga cikin mutanen da suka samu sauyi ta fuska me kyau tare da tarin nasarori daki-daki cikin rayuwar ta , wanda a yau ta kawo matakin kammala makarantar ta secondry wacce ta rayu tsawon shekaru biyar tana faɗi tashin neman ilmi a cikin ta , da jajircewar ta tare da nuna ƙwazo ya sa aka ɗaga ta aka mata tsallaken aji na shekara guda daga jss3 zuwa ss2.
Da hakan ya kawo kammaluwar karatun nata cikin shekaru biyar kachal .
Ta fito da sakamako mafi kyau da ya sanyata farin ciki ita da duk wasu makusantan ta musamma malama maryam da lubna waÉ—anda da jajircewar su cikin taimakon yakaka a harkar ilmin ta har ta kawo wannan matsayin .
Samy baby ma wacce ta tashi daga matsayin samy baby ta koma ,Hajiya samira ," ita ma ta taya yakaka farin cikin kammala karatun ta wanda duk wasu kuɗaɗen hidindimun karatun daga farkon sa har ƙarshen sa ya fito ne daga aljihun Alhaji Gali da har kawo yau suke liƙe a naniƙe da juna , bata da wata maraba da matar sa , kai har ma ta zarta matar sa ta aure iko da shi tare da samun kuɗaɗen hannun sa , Alhalin kuwa har yau da suke samun wajen shekaru takwas tare sun gaza yin aure ."illar bariki kenan ,!
Karo na uku yakaka ta ajiye ƴar madaidaiciyar taɓaryar hannun ta da take dakan fura da ita , ta murza tafin hannun ta da suka yi ruwan hoda hoda saboda dakan da basu saba yin irin sa ba ,
  Ta ɗago fuskar ta tana yamutsa ta ,
Ummi wallahi nagaji da dakan nan É—an Allah ummi a min sassauci ki yadda na tafi ko'ina ne cikin garin nan na nemo furar nan nayi sadakar nan da ita , Allah bazan iya yin fura da hannu na ba ,
Malama maryam wacce take zaune daga gefe akan kujerar tsakar gida tana karatun littafin Al'mauduat Al'kubra , ta É—an janye littafin daga fuskar ta
  Fuskar ta babu alamun wasa ta ce ,
  Sai fa kin daka furar nan yakaka kiyi sadaka da abunda kika sha wahala wajen samun sa yafi ɗaukaka darajar sadakar ki a wajen ubangiji , tsawon shekaru biyar kina faɗi tashin neman ilmin nan , a yanzu kin samu kin kai wata gaɓa me kauri ashe baza ki iya dakan fura kaɗai kiyi sadaka domin nuna godiya ga ubangijin ki ba ??
Jikin yakaka a sanyaye ta amsa
  Zan iya ummi ,
To maza kiyi sauri ki gama dan shabiyu ta kusa , kar har a sauƙo daga juma'ah baki gama ba kin ga kamata yayi a ce ki rabar da ita ga mabaratan da suke bakin masallacin juma'ar unguwar nan kin ji ko ?
 To ummi tace tana saɓar taɓaryar ta fara daka ,
  Lubna wacce take zaune a gefe kusa da ita kan ƴar darduma tana yankar ƙumba , ta ɗago kan ta fuskar ta da murmushi ta sanya hannu cikin faffaɗan kwanon silver da aka ajiye guntun dafaffiyar furar da ba'a kai ga daka ta ba , ta gutsuro wata ƙatuwa ta sake jefawa cikin turmin da yakaka ke daka ,
  Yauwa ƴar ummi yi maza ki daka, na ɗebo madara na fara damu ni ce ta farkon sanya Albarka a result ɗin nan kin sani ko ?
  Ummi kina ganin ta fa ? Tana ƙara min wata bayan na kusa gama dakan
 Lubna maza ajiye nails clipper nan ki karɓi dakan nan ki taya ta ,
  Ta furta hakan tana gyara zama gilashin idanun tana cigaba da karatun ta .
 Ummiii , dan Allah ni lokacin da nayi nawa dakan futar gama makarantar ta taya ni Haba ummi dan Allah,Â
 Wallahi na taya ki kin manta ranar ....
  Yanzu aikin samun ladan kuke yiwa haka ?
  To shikenan duk ku bari ni zan zo na ƙarba nayi tunda da alamu ku lada yayi muku yawan da ya sa har kuka fara gudun sa ,
 Da sauri lubna ta zaburo tana ƙoƙarin karɓe taɓaryar hannun yakaka ita kuma yakakar ta riƙe gam ta hana ta ,
 Dan Allah ki bar ni na taya ki kin ji sahiba ta.
  Tare da marairaice murya
 Naƙi ɗin , nima zan daka kaya na duk na mulmula na ɗau abuna a kai naje na rabar , kin ji sahiba ta .
Wayar lubna da ta É—au kiÉ—a ita ta raba musu gardama
  Cikin sauri lubna ta ɗau wayar ta ta yi hanyar falo tana satar kallon ummi wacce bata nuna alamun ta san duk abunda suke a wajen ,
 Yakaka ta bi bayan ta da kallo tana murmushi
Ta kai gaf da shiga falon ta É—aga murya tana cewa ,
  A gaishe min da yayan namu da kyau da kyau kin ji sahiba ta ?
Da gudu lubna ta ƙarasa shigewa falon tana dariyar jin kunyar ummi .
Ƙarfe biyu dai-dai da idar da sallar juma'a yakaka da lubna sun kammala ɗaura fura guda uku uku a cikin farar leda tare da kindirmo me ɗan dama shima a ƙulle a leda daban , suka haɗa su suka zuba a ƴar bakar leda daban daban , ba laifi dayawa ,
Yakaka ta jaa hijabinta saka lokacin da ta gama saka socks ɗin ta a kafa ta zura hijabin tana kallon lubna wacce take ƙoƙarin ɗaura niƙaf ɗin ta ,
  Sahiba dan Allah muyi sauri kar mabuƙata su watse ,
  Taku biyu tayi ta ɗauko niƙab ɗin ta ruwan madara , mahaɗin hijabin ta ta fara ƙoƙarin ɗaurawa a fuskar ta ,
Da sauri lubna ta riƙe niƙaf ɗin ,
 Haba sahiba ta ? Ina mun yi cewa kin daina saka niƙab ɗin nan haka sai bayan kin yi aure ??
Hararar ta tayi
  Shiyasa na ga ai kema yanzu da za ki fita babu naƙib ɗin a fuskar ki , ni dan Allah sakar min mahaɗin kwalliya ta , cikamakon martaba ta ,na sanya abuna ,
  Amma ai ni kin san dai an riga an sanya rana , babu sauran wani ɗa namiji da zai sake cewa yana so na na kula shi ,
  Ok to maza yi min gorin aure sahiba ,
  Ta furta hakan muryar ta babu alamun wasa .
 A hankali ta sakar mata niƙab ɗin , Allah ya baki haƙuri sahiba ba manufata ba kenan . Mu tafi .
Yakaka wacce bata furta zancen da wata manufa ta daban ba daga cikin ran ta sai domin ta samu lubna ta sakar mata niƙab ɗin ta da take neman ƙarfi da yaji ta hana ta sawa a cewar ta shi yake hana samari kula yakakar tunda ba ganin fuskar ta suke ba , duk sai ta ji ta ba daɗi da ta ga kamar zancen ta ya sa aminiyar ta a damuwa .
Tafe suke akan hanyar su ta dawowa daga rabar da furar suna tafe suna hirar su hankali kwance irin ta shaƙiƙan ƙawayen da halin su da ra'ayoyin su suka zo ɗaya suke kuma ƙaunar juna domin Allah ,
Æata rai tayi ta É—auke kai
Murmushi youssouf yayi , shi dai rigimar hajja da falmata na ba shi dariyaÂ
Duba fatima ki bar mama a wajen hajja har ki tai école ki dawo Kin ji kou ? Ba'a tafiya da yara école.
Shiru tayi idanun ta na kawo ƙwalla ita dai bata ƙaunar abunda zai raba ta da mama ko na ƴan mintoci ne bare fa makaranta da awanni zata yi a can , kai anya zata iya , ?
To hajja mu dunga zuwa tare da ke mana makarantar ? Sai ki dunga riƙe min mama nayi karatun na fito ?
Ke raba ni da wannan gudun birin , gotai gotai da ni zani makarantar ? Yaushe rabon duniya da ayyaraye ? Babu inda za ni ke kaɗai zaki tafi makarantar ki ki dawo ki same ni ina nan , ilmin ai shine Babban gatan ki falmata kin ji ko ?
Naji hajja
Yauwa mutuniyar ai shiyasa nake son ki akwai ki da saurin fahimta ,
Sallama suka yi da youssouf yana sake yiwa hajja godiya me tarin yawa tare da ɗanka mata ƴan kuɗaɗe wanda da kyar hajjan ta yadda ta karɓa sai da yayi ta roƙon ta da Allah .
Daga nan Dosso yayiwa tsinke bai jin marmarin zuwa maraɗi duk da cewa fiye da kaso talatin na ɓacin ran sa game da sha'anin sa da gimbiya maimouna ya kau , domin har sun yi waya ma cikin kwanaki biyun .
 Â
Assalamu Alaikum kowa da kowa !
Da fatan kuna lafiya ?
Ina neman afuwar ku bisa jinkirin zuwan wannan shafin , hakan ya faru ne sakamakon tafiya da ni zuwa gida , ban samu zama ba ziyarar dangi da sauran Al'amuran yau da kullum .
Da fatan zaku cigaba da haƙuri da tsaikon da ake samu cikin ajizanci irin na ɗan Adam ?
Nagode
 Â
[9/3, 10:14 PM] +234 806 122 1116: Fikrah writers association
MAFARI
( Hargitsin Rayuwa )
Umm'muaz
32
Bayan Shekaru Biyar
Lokaci baya jira sai dai a jira shi , ba'a masa shamaƙi a yayin wucewar sa , Lokaci gudu ne da shi fiye da saurin bugun zuciyar ɗan adam ,
Lokaci yayi juyi ya juya ya zo da sauyi ta mabanbantan fuskoki a rayuwar mutane a cikin tsawon shakaru biyar .
Yakaka tana ɗaya daga cikin mutanen da suka samu sauyi ta fuska me kyau tare da tarin nasarori daki-daki cikin rayuwar ta , wanda a yau ta kawo matakin kammala makarantar ta secondry wacce ta rayu tsawon shekaru biyar tana faɗi tashin neman ilmi a cikin ta , da jajircewar ta tare da nuna ƙwazo ya sa aka ɗaga ta aka mata tsallaken aji na shekara guda daga jss3 zuwa ss2.
Da hakan ya kawo kammaluwar karatun nata cikin shekaru biyar kachal .
Ta fito da sakamako mafi kyau da ya sanyata farin ciki ita da duk wasu makusantan ta musamma malama maryam da lubna waÉ—anda da jajircewar su cikin taimakon yakaka a harkar ilmin ta har ta kawo wannan matsayin .
Samy baby ma wacce ta tashi daga matsayin samy baby ta koma ,Hajiya samira ," ita ma ta taya yakaka farin cikin kammala karatun ta wanda duk wasu kuɗaɗen hidindimun karatun daga farkon sa har ƙarshen sa ya fito ne daga aljihun Alhaji Gali da har kawo yau suke liƙe a naniƙe da juna , bata da wata maraba da matar sa , kai har ma ta zarta matar sa ta aure iko da shi tare da samun kuɗaɗen hannun sa , Alhalin kuwa har yau da suke samun wajen shekaru takwas tare sun gaza yin aure ."illar bariki kenan ,!
Karo na uku yakaka ta ajiye ƴar madaidaiciyar taɓaryar hannun ta da take dakan fura da ita , ta murza tafin hannun ta da suka yi ruwan hoda hoda saboda dakan da basu saba yin irin sa ba ,
  Ta ɗago fuskar ta tana yamutsa ta ,
Ummi wallahi nagaji da dakan nan É—an Allah ummi a min sassauci ki yadda na tafi ko'ina ne cikin garin nan na nemo furar nan nayi sadakar nan da ita , Allah bazan iya yin fura da hannu na ba ,
Malama maryam wacce take zaune daga gefe akan kujerar tsakar gida tana karatun littafin Al'mauduat Al'kubra , ta É—an janye littafin daga fuskar ta
  Fuskar ta babu alamun wasa ta ce ,
  Sai fa kin daka furar nan yakaka kiyi sadaka da abunda kika sha wahala wajen samun sa yafi ɗaukaka darajar sadakar ki a wajen ubangiji , tsawon shekaru biyar kina faɗi tashin neman ilmin nan , a yanzu kin samu kin kai wata gaɓa me kauri ashe baza ki iya dakan fura kaɗai kiyi sadaka domin nuna godiya ga ubangijin ki ba ??
Jikin yakaka a sanyaye ta amsa
  Zan iya ummi ,
To maza kiyi sauri ki gama dan shabiyu ta kusa , kar har a sauƙo daga juma'ah baki gama ba kin ga kamata yayi a ce ki rabar da ita ga mabaratan da suke bakin masallacin juma'ar unguwar nan kin ji ko ?
 To ummi tace tana saɓar taɓaryar ta fara daka ,
  Lubna wacce take zaune a gefe kusa da ita kan ƴar darduma tana yankar ƙumba , ta ɗago kan ta fuskar ta da murmushi ta sanya hannu cikin faffaɗan kwanon silver da aka ajiye guntun dafaffiyar furar da ba'a kai ga daka ta ba , ta gutsuro wata ƙatuwa ta sake jefawa cikin turmin da yakaka ke daka ,
  Yauwa ƴar ummi yi maza ki daka, na ɗebo madara na fara damu ni ce ta farkon sanya Albarka a result ɗin nan kin sani ko ?
  Ummi kina ganin ta fa ? Tana ƙara min wata bayan na kusa gama dakan
 Lubna maza ajiye nails clipper nan ki karɓi dakan nan ki taya ta ,
  Ta furta hakan tana gyara zama gilashin idanun tana cigaba da karatun ta .
 Ummiii , dan Allah ni lokacin da nayi nawa dakan futar gama makarantar ta taya ni Haba ummi dan Allah,Â
 Wallahi na taya ki kin manta ranar ....
  Yanzu aikin samun ladan kuke yiwa haka ?
  To shikenan duk ku bari ni zan zo na ƙarba nayi tunda da alamu ku lada yayi muku yawan da ya sa har kuka fara gudun sa ,
 Da sauri lubna ta zaburo tana ƙoƙarin karɓe taɓaryar hannun yakaka ita kuma yakakar ta riƙe gam ta hana ta ,
 Dan Allah ki bar ni na taya ki kin ji sahiba ta.
  Tare da marairaice murya
 Naƙi ɗin , nima zan daka kaya na duk na mulmula na ɗau abuna a kai naje na rabar , kin ji sahiba ta .
Wayar lubna da ta É—au kiÉ—a ita ta raba musu gardama
  Cikin sauri lubna ta ɗau wayar ta ta yi hanyar falo tana satar kallon ummi wacce bata nuna alamun ta san duk abunda suke a wajen ,
 Yakaka ta bi bayan ta da kallo tana murmushi
Ta kai gaf da shiga falon ta É—aga murya tana cewa ,
  A gaishe min da yayan namu da kyau da kyau kin ji sahiba ta ?
Da gudu lubna ta ƙarasa shigewa falon tana dariyar jin kunyar ummi .
Ƙarfe biyu dai-dai da idar da sallar juma'a yakaka da lubna sun kammala ɗaura fura guda uku uku a cikin farar leda tare da kindirmo me ɗan dama shima a ƙulle a leda daban , suka haɗa su suka zuba a ƴar bakar leda daban daban , ba laifi dayawa ,
Yakaka ta jaa hijabinta saka lokacin da ta gama saka socks ɗin ta a kafa ta zura hijabin tana kallon lubna wacce take ƙoƙarin ɗaura niƙaf ɗin ta ,
  Sahiba dan Allah muyi sauri kar mabuƙata su watse ,
  Taku biyu tayi ta ɗauko niƙab ɗin ta ruwan madara , mahaɗin hijabin ta ta fara ƙoƙarin ɗaurawa a fuskar ta ,
Da sauri lubna ta riƙe niƙaf ɗin ,
 Haba sahiba ta ? Ina mun yi cewa kin daina saka niƙab ɗin nan haka sai bayan kin yi aure ??
Hararar ta tayi
  Shiyasa na ga ai kema yanzu da za ki fita babu naƙib ɗin a fuskar ki , ni dan Allah sakar min mahaɗin kwalliya ta , cikamakon martaba ta ,na sanya abuna ,
  Amma ai ni kin san dai an riga an sanya rana , babu sauran wani ɗa namiji da zai sake cewa yana so na na kula shi ,
  Ok to maza yi min gorin aure sahiba ,
  Ta furta hakan muryar ta babu alamun wasa .
 A hankali ta sakar mata niƙab ɗin , Allah ya baki haƙuri sahiba ba manufata ba kenan . Mu tafi .
Yakaka wacce bata furta zancen da wata manufa ta daban ba daga cikin ran ta sai domin ta samu lubna ta sakar mata niƙab ɗin ta da take neman ƙarfi da yaji ta hana ta sawa a cewar ta shi yake hana samari kula yakakar tunda ba ganin fuskar ta suke ba , duk sai ta ji ta ba daɗi da ta ga kamar zancen ta ya sa aminiyar ta a damuwa .
Tafe suke akan hanyar su ta dawowa daga rabar da furar suna tafe suna hirar su hankali kwance irin ta shaƙiƙan ƙawayen da halin su da ra'ayoyin su suka zo ɗaya suke kuma ƙaunar juna domin Allah ,