Sashe 189
Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
duba guda Maimartaba yayi musu ita da su Yakaka yayi wucewar sa , Tafeeda ya bi bayansa da gawar Mama , Youssouf ma ya sauƙa ya nufi ƙofar ficewa , ya zo ficewa ya waiga garesu da har lokacin suke ƙasa dirshen a zube , muryarsa a ciki yace
"ku tasso mu tai ku wanke ta ,
Shiru suka yi babu wacce ta amsa masa ,
Ganin ya fita yasa Hajja cewa ,
"ku tashi mu tafi Falmata , Yakaka kuyi haƙuri kun ji , haka Allah yake ikonsa uwa ta haifo ɗan da ta fi nisan kwana, kuyi haƙuri kuyi ta addu'a mutuwar Mama hutu ce a gareta , kuyi haƙuri .
Zuciyoyin su a lokacin basa aikin da ya wuce na kuka da jin raɗaɗin mutuwar ƴar da suka shirya sadauƙarwa a domin ta sai gashi mutuwa ta ɗauketa a lokacin da kowaccen su take jin rayuwarta kachokam zata sadauƙar domin ta tsaya tare da ita ,
Suka miƙe ƙafafun su babu ƙarfi suka rufa masa baya , a motar da suka zo a ciki suka koma sai dai wannan karon wani ne ke jaan motar da basu kai ga sanin sa ba ,
Gidan suka tarar da yalwar mutane da suka wuce yadda suka barsu a farko yawa ,
Mutane maza da suke sanye da kaya mai launi guda , da kuma mata a falon nasu , Yakaka da Falmata ratsawa suka yi basu dubi kowa ba suka wuce É—akin da yake na Falmata , suna shiga su duka biyun kuka suka sake sawa , a tsakanin su an rasa mai rarrashin wani ,
Shigowar Tafeeda É—auke da gawar Mama shi ya dakatar da Æ´an guna-gunin da ya fara tashi bayan wucewar su
Kai tsaye ya miƙata ga Hajja wacce take raƙube daga gefe tunda ta shigo babu wanda ya dubeta bare su amsa gaisuwar ta'aziyyar da take yi musu da basu kai ga sanin wa ya rasu ba , ganin sun yi biris da ita ya sa tayi shiru tana sharar ƙwallar ta ,
"Ki miƙata ga uwayenta sui mata wanka , su shirya ta yanzou za'a kawo likkafani ,
Sai ta ƙarbeta ta ratsa ta tsakanin su ta wuce ɗakin Falmata , zuwa lokacin hankalunsu baki ɗaya ya koma ga Tafeeda ,
Bai jira sun tambayeshi ba , ya ceÂ
"Diyar Biyamuradi Youssoufa ce da Allah ya amshi ranta a yanzou ,
Daga haka bai É—ora kome ba ya juya ya fita ,
Shiru wajen ya ɗauka , kafin lokacin da Hamshaƙiyar matar da ita ce ƙwal ɗaya a bisa kujera ta motsa , fuskar ta da wani yanayi da kai tsaye ba'a iya fassara shi ba ta soma da cewa ,
"Allahu Akbar innalillahi wa inna ilaihi raji'oon , kaico yarinya wahalar ki ta ƙare kin kuma huttashe da wasu dagga samuwar baƙin-ciki sanadin duban ki , to Allah shi jiƙan ki , ta tabbata dai Youssoufa yana da ɗiya mai shekarun ya wannan da kuma Amre ko ba Amre ?
Bata tsaya ba ta cigaba da cewa , "Mutumin da ya ƙi faɗar gaskiya yana haddasa wahala, wautace babba a ɓatar da lokaci akan aikin banza , mutumin da ya ƙamnaci zunubi ya irin haka , ai ya shiryawa hukunci ne , zunubi da kunyata kuwa tare suke rungumar mai su, shiyasa asharari bashi da wata ƙima ,
Ta murza zoben hannunta , tana wani ɗan guntun murmushin cikar buri , ta ɗora
" gaskiya ita dawwamammiya ce ƙarya kuwa ai ƙurarriya ce , ɗan da ya jawo wa Mahaifinsa ɓacin rai ya haka ,? Ai abun baƙin-ciki yake ga Mahaifiyarsa , to wanne farin-ciki za'a yi da samuwar baragurbi cikin 'ya'ya ?
A hankali Adda Ammi ta ɗaga kai ta kai ganin ta gareta bayan gama jawabinta lokacin da ƙaramar jakadiya tace ,
" Babu shakka ko kokonto cikin kalamanki ranki ya daÉ—e , kowa ya aikata abunda ransa ke so zai ga abunda bai so a lokacin da bai so ba ,
Kallon-kallo aka yi tsakani Ammi da Ubbo da kawo yanzu suka rasa halin da zuciyoyin su ke ciki kan mutuwar ƴar ɗan uwansu da ake duk wani ƙiƙi-ƙaƙa akanta ,
Sai dai kalaman Matar da take mazaunin uwa agare su , Matar Mahaifinsu , da kuma ta wakilci Mahaifiyar su wajen wanzuwarta anan , da kalaman nata ke nuni ƙarara da tazorci gami da kausasawa ga ƙaninsu , ko kusa bai musu daɗi ba , duba da cewa wajen gauraye yake da bayun su ,waɗanda Youssouf shugaba yake a wajen su duk da laifin sa ,
sai dai su basu da ikon tankawa ,"Hajiya Mama uwa take kuma shugaba a gurin suÂ
Ba'a ɗau lokaci ba Tafeeda ya dawo hannunsa riƙe da likkafani , ya miƙawa Ubbo ba tare da yace kome ba ,
Sai ta karɓa ta nufi ɗakin da ta ga sun shiga ta tarar da su su ukun suna kewaye da gawar Mama da take shimfiɗe a ƙasa ,
Yanayin da ta gansu ya taɓa ranta , bata ce ƙala ba ta miƙawa Hajja likkafanin ,
Ta juya , har ta kai ƙofa ta juyo , "kun iya wankan ? Ta tambayesu
Babu jinkiri Yakaka ta gyaÉ—a kanta , sai ta juya tayi ficewarta tana É—auke ganinta daga kan hoton Mama da yake bangon É—akin Falmata , tsananin kamannin da yake tsakanin Mama da nata Æ´a'Æ´an ya girgiza ranta .
Yakaka ita ta wanki gawar Mama da take rungume a jikin Falmata , ƙwarar idanun su bata huta ba wajen zubar hawaye ,
Tunawa Yakaka take tun daga ranar da suka ɗora ƙazamtatciyar alaƙa da Youssouf , har zuwa ɗaukar rainon cikin ta da ta samun ta ta haramtatciyar hanya , zuwa da ranar da ta haifeta , da ko fuskarta bata kai ga gani ba , ta tuno da ranar da ta zo irin kallon da tayi mata dake bayyana tsoro da rashin sanayya ,
' tsawon rayuwar da Mama tayi shekaru shida a duniya bazata ɗorar da kome na daga rayuwar yarinyar ba , ƴar da ta ƙi kallonta lokacin farko da ta fito duniya , ta kuma tafi ta barta bata ji tausayin ta tayi tunanin me zata ci ta rayu alhalin abincinta na jikinta ba , ina zata ji ɗumin jikin uwa irin wanda jariri ke buƙata a lokaci na hunturu ?
Babu shakka Samy Baby ta zalunceta da ta cisgeta daga cikin Æ´ar gajeriyar rayuwar Æ´arta , ta yi mata yaudara mafi girma da ciwo , irin ciwon da ba zai rabu da ruhinta ba har ta koma ga Maliccinta ,
" Mama Allah ya jiƙan ki yasa kin samu hutu dawwamamme daga barin rayuwarki mai cike da jinyar gangar jiki , ki yafe min Mama , ki yafe min , addu'o'i ta cigaba da yi mata tana wanke ta .
Bayan sun shiryata suka fito da ita , Hajja ta fita ta ƙira Ubbo , zama tayi a ɗakin sannan ta ƙira Tafeeda ta sanar da shi an shiryata , babu jimawa suka shigo su biyu da wani , suka ɗau gawar Mama zuwa waje da za'a sallaceta ,
Falmata kasa riƙe kukan da yazo mata tayi ta fashe da kuka mai ƙarfin gaske , dake bayyana jin ciwon rabuwarta da ƴar da ta ƙwallafawa rai fiye da abunda ke cikin cikinta ,
Ƴar da ta so tare da sadauƙar da kome a domin ta , ƙaunar da ta mata ta fara daga ranar da ta rungumeta a jikinta bayan rashin mahaifiya da tayi , ta ɗau alwashin maye mata gurbin uwa da ta rasa , ta dunga tuno da yadda suka ƙaunaci juna ita da Mama , da bata san tana da wata uwa ba bayanta har ta koma ga mahaliccinta ita ce mahaifiyarta ɗaya tal, tabbas Mama ta bar mata gurbi a zucia sa babu ranar cikata shi .
***
Tamkar wutar daji haka labarin mutuwar ɗiyar Biyamuradi Youssouf/MaJor Youssouf da mutane basu san da wanzuwarta ba ya dunga kewaya ko'ina ɗauke da mummunan tambarin da Youssouf ya ƙi tabbatuwar sa ga rayuwar Mama sai ga shi bayan mutuwar ta labari ya bayyana an kuma ƙira ta da sunan da bai so ba .
Zaman makoki sosai ya kankama tun yammacin ranar da aka bizneta da kuma tun bayan jana'izar da Maimartaba sarkin Maraɗi da kansa yayi limanci , ya bar wajen tun kafin dawowar su daga maƙabarta ,
Ƙarƙashin rakiyar maƙarrabansa da suka zo tare suka koma , waɗanda mafi yawa manyan fada ne , masu faɗa a ji a harkar sarautar masarautarsu da amintattun manyan bayunsa , zaɓaɓɓu da aka aminta da Amanarsu
Da tafiyar tasu musamman ta samo asali ne kan zuwa su ganewa idanunsu inda Youssouf ɗin ya ɓoye yana rayuwar banza kamar yadda aka yi ta jita-jita a kwanaki zancen kuma ya dawo kunnuwansu Amma suka yi binciƙe basu samu shaida ba ko guda a wancen lokacin
Sai fa da yanzu shaida ta bayyana ta hannun Mouhammadou da yace shi ma fa bayani aka ba shi ,
Mafiya yawan masu zuwa ta'aziyyar abokan aikinsa ne da matan su sai kuma tsirarun mutanen gari da yake mutunci da su , daga masarautar su babu mutum guda da ya ƙiraye shi ko kuwa ya zo yi masa ta'aziyya tun bayan juyawar tawagar sarki da kuma ta su Hajiya mama ,
Tsakanin Hajiya Umma ko matansa babu wacce ta ƙira shi , haka ma 'ƴan uwansa idan aka cire Ubbo da Ammi da kawo yau da ake kwanaki biyu da mutuwar Kullum suna zuwa gidan nashi su yini a karɓi gaisuwa da su duk a ƙoƙarin su na son ganin sun rufa asirin ɗan uwansu daga mutanen da basu riga da sun san ta hanyar da ya samar da Mama ba ,
Sai dai a yau su ma sun kudurce cewa sun yi zuwan ƙarshe dan haka suka yanke shawarar yi masa magana ,
Har falon sa suka shiga suka tarar da shi , tare da Tafeeda da tunda aka yi mutuwar yana tare da shi , duk da cewa babu wata doguwar mu'amala ko da kuwa ta maganar baki ce da take shiga tsakanin su ,
"ku tasso mu tai ku wanke ta ,
Shiru suka yi babu wacce ta amsa masa ,
Ganin ya fita yasa Hajja cewa ,
"ku tashi mu tafi Falmata , Yakaka kuyi haƙuri kun ji , haka Allah yake ikonsa uwa ta haifo ɗan da ta fi nisan kwana, kuyi haƙuri kuyi ta addu'a mutuwar Mama hutu ce a gareta , kuyi haƙuri .
Zuciyoyin su a lokacin basa aikin da ya wuce na kuka da jin raɗaɗin mutuwar ƴar da suka shirya sadauƙarwa a domin ta sai gashi mutuwa ta ɗauketa a lokacin da kowaccen su take jin rayuwarta kachokam zata sadauƙar domin ta tsaya tare da ita ,
Suka miƙe ƙafafun su babu ƙarfi suka rufa masa baya , a motar da suka zo a ciki suka koma sai dai wannan karon wani ne ke jaan motar da basu kai ga sanin sa ba ,
Gidan suka tarar da yalwar mutane da suka wuce yadda suka barsu a farko yawa ,
Mutane maza da suke sanye da kaya mai launi guda , da kuma mata a falon nasu , Yakaka da Falmata ratsawa suka yi basu dubi kowa ba suka wuce É—akin da yake na Falmata , suna shiga su duka biyun kuka suka sake sawa , a tsakanin su an rasa mai rarrashin wani ,
Shigowar Tafeeda É—auke da gawar Mama shi ya dakatar da Æ´an guna-gunin da ya fara tashi bayan wucewar su
Kai tsaye ya miƙata ga Hajja wacce take raƙube daga gefe tunda ta shigo babu wanda ya dubeta bare su amsa gaisuwar ta'aziyyar da take yi musu da basu kai ga sanin wa ya rasu ba , ganin sun yi biris da ita ya sa tayi shiru tana sharar ƙwallar ta ,
"Ki miƙata ga uwayenta sui mata wanka , su shirya ta yanzou za'a kawo likkafani ,
Sai ta ƙarbeta ta ratsa ta tsakanin su ta wuce ɗakin Falmata , zuwa lokacin hankalunsu baki ɗaya ya koma ga Tafeeda ,
Bai jira sun tambayeshi ba , ya ceÂ
"Diyar Biyamuradi Youssoufa ce da Allah ya amshi ranta a yanzou ,
Daga haka bai É—ora kome ba ya juya ya fita ,
Shiru wajen ya ɗauka , kafin lokacin da Hamshaƙiyar matar da ita ce ƙwal ɗaya a bisa kujera ta motsa , fuskar ta da wani yanayi da kai tsaye ba'a iya fassara shi ba ta soma da cewa ,
"Allahu Akbar innalillahi wa inna ilaihi raji'oon , kaico yarinya wahalar ki ta ƙare kin kuma huttashe da wasu dagga samuwar baƙin-ciki sanadin duban ki , to Allah shi jiƙan ki , ta tabbata dai Youssoufa yana da ɗiya mai shekarun ya wannan da kuma Amre ko ba Amre ?
Bata tsaya ba ta cigaba da cewa , "Mutumin da ya ƙi faɗar gaskiya yana haddasa wahala, wautace babba a ɓatar da lokaci akan aikin banza , mutumin da ya ƙamnaci zunubi ya irin haka , ai ya shiryawa hukunci ne , zunubi da kunyata kuwa tare suke rungumar mai su, shiyasa asharari bashi da wata ƙima ,
Ta murza zoben hannunta , tana wani ɗan guntun murmushin cikar buri , ta ɗora
" gaskiya ita dawwamammiya ce ƙarya kuwa ai ƙurarriya ce , ɗan da ya jawo wa Mahaifinsa ɓacin rai ya haka ,? Ai abun baƙin-ciki yake ga Mahaifiyarsa , to wanne farin-ciki za'a yi da samuwar baragurbi cikin 'ya'ya ?
A hankali Adda Ammi ta ɗaga kai ta kai ganin ta gareta bayan gama jawabinta lokacin da ƙaramar jakadiya tace ,
" Babu shakka ko kokonto cikin kalamanki ranki ya daÉ—e , kowa ya aikata abunda ransa ke so zai ga abunda bai so a lokacin da bai so ba ,
Kallon-kallo aka yi tsakani Ammi da Ubbo da kawo yanzu suka rasa halin da zuciyoyin su ke ciki kan mutuwar ƴar ɗan uwansu da ake duk wani ƙiƙi-ƙaƙa akanta ,
Sai dai kalaman Matar da take mazaunin uwa agare su , Matar Mahaifinsu , da kuma ta wakilci Mahaifiyar su wajen wanzuwarta anan , da kalaman nata ke nuni ƙarara da tazorci gami da kausasawa ga ƙaninsu , ko kusa bai musu daɗi ba , duba da cewa wajen gauraye yake da bayun su ,waɗanda Youssouf shugaba yake a wajen su duk da laifin sa ,
sai dai su basu da ikon tankawa ,"Hajiya Mama uwa take kuma shugaba a gurin suÂ
Ba'a ɗau lokaci ba Tafeeda ya dawo hannunsa riƙe da likkafani , ya miƙawa Ubbo ba tare da yace kome ba ,
Sai ta karɓa ta nufi ɗakin da ta ga sun shiga ta tarar da su su ukun suna kewaye da gawar Mama da take shimfiɗe a ƙasa ,
Yanayin da ta gansu ya taɓa ranta , bata ce ƙala ba ta miƙawa Hajja likkafanin ,
Ta juya , har ta kai ƙofa ta juyo , "kun iya wankan ? Ta tambayesu
Babu jinkiri Yakaka ta gyaÉ—a kanta , sai ta juya tayi ficewarta tana É—auke ganinta daga kan hoton Mama da yake bangon É—akin Falmata , tsananin kamannin da yake tsakanin Mama da nata Æ´a'Æ´an ya girgiza ranta .
Yakaka ita ta wanki gawar Mama da take rungume a jikin Falmata , ƙwarar idanun su bata huta ba wajen zubar hawaye ,
Tunawa Yakaka take tun daga ranar da suka ɗora ƙazamtatciyar alaƙa da Youssouf , har zuwa ɗaukar rainon cikin ta da ta samun ta ta haramtatciyar hanya , zuwa da ranar da ta haifeta , da ko fuskarta bata kai ga gani ba , ta tuno da ranar da ta zo irin kallon da tayi mata dake bayyana tsoro da rashin sanayya ,
' tsawon rayuwar da Mama tayi shekaru shida a duniya bazata ɗorar da kome na daga rayuwar yarinyar ba , ƴar da ta ƙi kallonta lokacin farko da ta fito duniya , ta kuma tafi ta barta bata ji tausayin ta tayi tunanin me zata ci ta rayu alhalin abincinta na jikinta ba , ina zata ji ɗumin jikin uwa irin wanda jariri ke buƙata a lokaci na hunturu ?
Babu shakka Samy Baby ta zalunceta da ta cisgeta daga cikin Æ´ar gajeriyar rayuwar Æ´arta , ta yi mata yaudara mafi girma da ciwo , irin ciwon da ba zai rabu da ruhinta ba har ta koma ga Maliccinta ,
" Mama Allah ya jiƙan ki yasa kin samu hutu dawwamamme daga barin rayuwarki mai cike da jinyar gangar jiki , ki yafe min Mama , ki yafe min , addu'o'i ta cigaba da yi mata tana wanke ta .
Bayan sun shiryata suka fito da ita , Hajja ta fita ta ƙira Ubbo , zama tayi a ɗakin sannan ta ƙira Tafeeda ta sanar da shi an shiryata , babu jimawa suka shigo su biyu da wani , suka ɗau gawar Mama zuwa waje da za'a sallaceta ,
Falmata kasa riƙe kukan da yazo mata tayi ta fashe da kuka mai ƙarfin gaske , dake bayyana jin ciwon rabuwarta da ƴar da ta ƙwallafawa rai fiye da abunda ke cikin cikinta ,
Ƴar da ta so tare da sadauƙar da kome a domin ta , ƙaunar da ta mata ta fara daga ranar da ta rungumeta a jikinta bayan rashin mahaifiya da tayi , ta ɗau alwashin maye mata gurbin uwa da ta rasa , ta dunga tuno da yadda suka ƙaunaci juna ita da Mama , da bata san tana da wata uwa ba bayanta har ta koma ga mahaliccinta ita ce mahaifiyarta ɗaya tal, tabbas Mama ta bar mata gurbi a zucia sa babu ranar cikata shi .
***
Tamkar wutar daji haka labarin mutuwar ɗiyar Biyamuradi Youssouf/MaJor Youssouf da mutane basu san da wanzuwarta ba ya dunga kewaya ko'ina ɗauke da mummunan tambarin da Youssouf ya ƙi tabbatuwar sa ga rayuwar Mama sai ga shi bayan mutuwar ta labari ya bayyana an kuma ƙira ta da sunan da bai so ba .
Zaman makoki sosai ya kankama tun yammacin ranar da aka bizneta da kuma tun bayan jana'izar da Maimartaba sarkin Maraɗi da kansa yayi limanci , ya bar wajen tun kafin dawowar su daga maƙabarta ,
Ƙarƙashin rakiyar maƙarrabansa da suka zo tare suka koma , waɗanda mafi yawa manyan fada ne , masu faɗa a ji a harkar sarautar masarautarsu da amintattun manyan bayunsa , zaɓaɓɓu da aka aminta da Amanarsu
Da tafiyar tasu musamman ta samo asali ne kan zuwa su ganewa idanunsu inda Youssouf ɗin ya ɓoye yana rayuwar banza kamar yadda aka yi ta jita-jita a kwanaki zancen kuma ya dawo kunnuwansu Amma suka yi binciƙe basu samu shaida ba ko guda a wancen lokacin
Sai fa da yanzu shaida ta bayyana ta hannun Mouhammadou da yace shi ma fa bayani aka ba shi ,
Mafiya yawan masu zuwa ta'aziyyar abokan aikinsa ne da matan su sai kuma tsirarun mutanen gari da yake mutunci da su , daga masarautar su babu mutum guda da ya ƙiraye shi ko kuwa ya zo yi masa ta'aziyya tun bayan juyawar tawagar sarki da kuma ta su Hajiya mama ,
Tsakanin Hajiya Umma ko matansa babu wacce ta ƙira shi , haka ma 'ƴan uwansa idan aka cire Ubbo da Ammi da kawo yau da ake kwanaki biyu da mutuwar Kullum suna zuwa gidan nashi su yini a karɓi gaisuwa da su duk a ƙoƙarin su na son ganin sun rufa asirin ɗan uwansu daga mutanen da basu riga da sun san ta hanyar da ya samar da Mama ba ,
Sai dai a yau su ma sun kudurce cewa sun yi zuwan ƙarshe dan haka suka yanke shawarar yi masa magana ,
Har falon sa suka shiga suka tarar da shi , tare da Tafeeda da tunda aka yi mutuwar yana tare da shi , duk da cewa babu wata doguwar mu'amala ko da kuwa ta maganar baki ce da take shiga tsakanin su ,