← Book details Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 175 OF 269

Sashe 175

Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ya rage sati biyu tafiyar su da ya ke tsawon kwanaki kusan goma da yin wayar sa da Tafeeda , wanda duk yadda ya so ya samu damar da zasu sake yin wata magana , Tafeedan yaƙi ba shi haɗin kai idan ya ƙira wayar sa ba bai ɗauka saƙonnin sa kuwa ya tura su babu adadi ta kan yanar gizo da kai tsaye ta hanyar saƙon karta kwana , nan ma ga shaidar an karanta sako amma babu amsa , dan haka shima ya zuciya ya daina neman sa .

Ya fito wanka da safe ya tarar da miss call É—in Tafeeda , da hanzari ya É—au wayar bai ko tsaya shafa mai ya sanya kaya ba ya É—au wayar ya shiga neman layin sa ,

Sai dai kakarun Amai da ya jiyo daga Falon su ya sanya shi sauƙe wayar daga kunnen sa ba tare da ya kashe wayar ba ya fito falon hankalinsa a tashe ya ƙaraso ga Falmata wacce take durƙushe daga ƙofar kitchen ɗin su tana Amai ,

Da hanzari ya ƙaraso wajen ya riƙo ta zuwa jikin sa bayan ya ajiye wayar sa a ƙasa da aka riga aka ɗaga kiran daga ɗaya ɓangaren ba tare da ya sani ba ,

"qu'est-ce qui ne va pas avec toi chérie, es-tu malade? ( me yake damun ki ? Baki da lafiya ne ? )

Bata amsa ba illa yunƙurin Aman da ta cigaba da yi duk kuwa da babu kome a cikin nata ,

Shafa bayanta ya shiga yi yana É—an bubbugawa tare da jero mata sannu ,

Mama wacce tashin ta kenan daga bacci ta jiyo muryar su ta fito , itama ta tsaya tana kallon su fuskar  ɗauke da alhini da 'yar muryar tace

"Papa qu'est-ce qui ne va pas avec Mamma ?

"Princess Maman ki bata da lafiya ne, dauko min papier mouchoir dagga É—aki na goge mata baki ,

"To ,

Ta juya da É—an gudu zuwa É—akin su ,

"Sannu Fatima ,

Yace cike da tausayawa , 

Daga can ɓangaren Hawaye masu ɗumi suka silmiyo daga idanun Hajiya Umma , ta zare wayar Tafeeda daga kunnen ta tare da miƙa masa wayar ,

Karɓar wayar yayi ya duba wayar yaga ba'a katse ta ba dan haka cike da tashin hankali ya kara a kunnen sa yana fargabar ko wani abu ne ya faru da Youssouf ɗin ,

Sai dai ya ƙarashi Maganar sa bai ji Youssouf ɗin ya amsa ba , sai muryar wata mace yake ji ƙasa-ƙasa , dan haka ya katse wayar waigo ga Hajiya Umma ,

"Umma Lafiya Yarima yake kou ?

"babu shakka lafiya yake ,
ta amsa da wata irin murya ,

Ganin yanayin ta ya sa Tafeeda miƙewa yayi mata sallama zuciyar sa cike da tunanin meye haka Youssouf ya faɗi wanda ya sa Hajiya Umma ƙwalla ?

Shi daman zouwa yayi ya gaishe ta tare da cigaba da kwantar mata da hankali bayan tashin hankalin da ta shiga a kwanaki sakamakon wani Al'amari mai girma da ya taso game da Youssouf É—in ,

wanda shi yayi tsayuwar daka wajen ganin lamarin ya dai-daita da a yanzu yake mataki na ƙarshe na gyara kome wanda kuwa hakan ba zai samu ba sai da haɗin kan Youssouf ɗin ,

tunanin ko zai yadda da lamarin da zai je masa da shi a matsayin shawara ko ba zai yadda ba ya sanya shi yin jinkiri yana nazari dan haka nema yaƙi yarda suyi magana da Youssouf ɗin

Sai fa yau da Hajiya Umma ta sa ya ƙira sa a gabanta ta warware masa labarin mummunan ƙullin da aka so yi masa ,

Sai kuma ya ga Umma ta ƙare wayar ba tare da ta ce kome ba sai ƙwalla , lamarin da ya ƙulle masa kai kenan , koma menene zai ƙira Youssouf ɗin ya ji .

A ɓangaren Su Youssouf bayan Falmata ta gama Amai ya gyara wajen ya ɗau wayarsa bai lura da Shaidar an ɗaga ƙiransa ba saboda hankalinsa da yake kan Falmata wacce sai numfarfashi take saboda ƙaruwar bugun zuciyar ta tare da ciwon kai da ya haɗu mata ,

Ko sannu da Youssouf yake yi mata da kyar take amsawa ,

"Fatima ko mu tahi hospitalisé ne ?

Jikin ta babu kuzari ta gyada kai ,

Cikin hanzari ya shiga ya shirya ya wankewa Mama jiki tare da goge mata baki , ya dawo ya tarar da ita tana baccin zomo ,

"Fatima mu je ki shirya ,

Shi da kansa ya taya ta ta gyara jikinta yana riƙe da hannun ta suka fito

" za ki iya tafiya da kan ki ko kuwa na ƙira taxi ,

"zan iya tafiya ,

Basu sha wata wahala ba kasantuwar daman tana kan ziyartar likita , dan haka suka samu ganin likitan ta inda shi kuma bayan tambayoyin da yayi mata da duk bayanan da ta ba shi , ya miƙa su ga wata likita daban , wacce ta sake yi mata tambayoyi ,

Daga haka ta yi mata gwaji , bayan bayyanar sakamako ,

da fara'a likitar take miƙa musu sakon taya murnar cewa Falmata tana ɗauke da ciki na tsawon sati huɗu ,

Duk da cewa Falmata tana jin yaren faransanci babu laifi , Amma a yau ji tayi sam bata Fahimci me likitar ke nufi ba , tamkar ta manta ma'anar kalmar ,

Sai da ta ga Biyamuradi Youssouf ya rungume ta , yana bayyana farin-cikin sa da lokaci guda Albishirin da likitar tayi masa ya wanke masa zuciya tare da yin awun gaba da duk wata damuwa tasa , "Ya'ya ai arziƙi ne .

"Fatima Tu es enceinte, tu portes mon bébé , Alhamdulillah

Ya É—ago fuskar ta ya sumbanci goshin ta ,

Hannunta ta kai kan nasa hannun da yake tallafe da kumatun ta , kyawawan idanun ta na bayyana farin-cikin dake maƙare da zuciyar da

"Baban Mama da gaske ina da ciki ? Zan haifi jariri daga cikina Mama Zata samu dan uwa , Mama zata wa....

Katse ta yayi ta hanya ɗora laɓɓansa akan nata ya sumbace ta ,

"Mama da Yumna zasu samu É—an ouwa ko Æ´ar ouwa insha Allah nayi Farin-ciki Fatima .

Mama da take tsaye tana kallon su ba tare da ta san me suke yiwa murna ba , sai ita ma ta sa dariya ta taho ta rungumo su ,

Hannuwansa ya sa ya zagaye a jikinsa yana jin waɗannan rayukan guda biyu sun zama wani ɓangare na daga rayuwar sa ,

Da wannan farin-cikin me tarin yawa suka baro asibitin zuwa gida , bayan likita ta basu shawarwari tare da  'yan magungunan da zasu taimaka a matakin farko na zaman ciki .

Falmata Ji take babu wata rana da take kai wannan ranar farin-ciki a wajen ta , minti kaÉ—an zata kai hannu ta shafi cikin ta , farin-cikin ta biyu ne ,

Tana ganin cewa lokacin warkewar Mama yayi tunda gata É—auke da ciki ,

Da shigowarsu gida wayar sa tayi ƙara  Tafeeda ne ya sake ƙiran farin-cikin sa bai ɓuya ba a muryar sa suka gaisa da Tafeeda ,

Kafin Tafeeda ya É—ora da cewa ,

"Yarima magana nake so muyi kou ka bani dama ?

Jin haka sai ya miƙe daga jikin Falmata ya fita zuwa 'yar barandar gaban gidan ,

"É—an ouwa na baka dama faÉ—i ina jin ka ,

Yace masa a taƙaice ,

"Magana ce zamu yi game da lamarin yarinyar nan da kake boyen sa gareni tsawon wannan shekaru , na riga nasan koume kan zaman ka tare da su da amren innan ita yarinyar da kake har gidan da kun ka tare a Niamey na shina Yarima ,

"To munin Al'amarin ba dagga gareni yake ba , sai fa dagga maƙiya waɗanda sunka dunga bin lamarinka , a cikin binciken da nai kai tamkar da sanya hannun su kome da ya faru ya kai ga faruwa  ,

"Lamari ya munana ta inda zance ya taho ga Fada ya iske kunnen Maimartaba da Hajiya Umma bai tsaya nan ba har sai da ya iske mutanen cikin Fada baki É—ai ba'a kouma san waye ya fiddo maganar ba ,

"cewa Yariman MaraÉ—i yana da É—iyar banza bata Amre ba , tare da yin zaman banza da Mahaifiyar ta zaman dadiro , tun dagga Nigeria ,

"Yarima nayi duk bakin ƙoƙarina wajen ganin anbi daddigin masu yaɗa maganar nan an dakile bazuwar ta , kouma anyi nasara ,sannan na ƙaryata batun gaban moutanen cikin fada tare da Maimartaba ,

"Amma nasan wannan yunƙuri nawa ai bai isa ba ya kawo ƙarshen maganar nan tunda kouwa akwai ta da gaskiya , maƙiya ba za su bar lamarin nan ba .

"Menene mafita a yanzou ?

Youssouf ya katse dogon bayanin da Tafeeda ke yi masa ,cikin miƙa wuya

'Mafita gouda ce ,ka rabu da ita wannan yarinyar da kake amre , ka sallame su su tafi tare da É—iyar nan ,

"ka rabou da ita domin tsarkake kan ka dagga zargin al'umma ,tare da aibatawa ,

"ka rabou da ita domin tsira da mutuncin tare da ƙimar ka ,

"ka rabou da ita doumin gujewa russa alaƙar ka da iyaye da 'yan ouwan ka ,

"ka rabou da ita doumin gujewa samar da bakin-ciki a zuciyar Mahaifiyar ka ,

"ka rabou da ita domin gudun samun galabar maƙiya a kan ka ,

"ka rabou da ita domin tsarkake masarautar ku tare da kaiwa ga matakin nasarar zama sarkin maraÉ—i a watarana .

"ka nesanta kan ka daga wannan ɗiya da innarta doumin tsallake ramin maƙiya , muddin ka ƙiya ? Za ka gamou da dariyar maƙiya da baƙin-cikin iyayen ka .

"cigaba da zama da itta yana nufin rassa kowa tare da kai ciki kouwa har da ni kaina .

"Tafeeda ,

Youssouf ya ƙira shi da wata irin murya mai cike da tashin hankali ,

"Yarima shawara ce ni na baka zaɓi yana dagga gare ka , ni na barka lafiya ,

Wani iri yake ji tamkar an zare masa laka , menene yake shirin Faruwa da rayuwarsa ne ?

Kalmar Rabuwa da Fatima tayi masa nawin saurara ko a kunne kawai ,
Chapter 175 · 0% Book details