Sashe 201
Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tunanin ta ya tsaya chak na wasu ƴan daƙiƙoƙi lokacin da idanun ta suka kai kan fuskar Khaalty Rahima wacce take murmushi tana raba ganin ta a tsakanin su biyun cike da nishaɗin sake samun damar ganin su tare a gaban ta .
A hankali Yakaka ta mike tana kusantar inda take bayan tsayuwar kukan ta chak , zuciyarta cike da wasi-wasin gaskanta sake ganin ta , sai dai kuma ko a cikin mafarki ta ga Mahaifiyar su ai ba zata gagara gane ta ba ko me kuwa jirkituwar kamanni da ta samu mai-kyau ko mai-muni .
Tana ƙarasowa gurinta ta kai hannu a hankali tana tattaɓa jikin Khaalty Rahima, muryar ta a dishe da kukan da tayi tace ,
  "Maama ke ce ? Ke ce Mama ?
  Hannun ta da yake taɓa jikinta khaalty Rahima ta riƙe , tana cewa , "Ni ce Aminatu , Yakaka na , ni ce ,
 Yakaka tana wata ƴar Dariya-dariya , kuka-kukan da yake fallasa tsantsar ruɗanin farin-cikin da take ciki , ta waigo ga Falmata tana mai mancewa da Falmatan ta riga ta haɗuwa da Mama , ɓakin-cikin da ta shigo da shi yana zagwanyewa tace ,
  "Falmata wallahi Maman mu ce , kin ga Maman mu ? Zo ki gan ta , ta ƙarasa magana tare da yafito Falmatan da hannu ,
  Sai kuma ta juya ta rungume ta da ƙarfi tana cewa ,"Mama na, Alhamdulillah , Alhamdulillahi .
****
Daren ranar ba suyi wani baccin kirki ba su duk huÉ—un hira kawai suke yi inda cikin labarin da Yakaka ta basu ta bayyana musu ainahin yadda haÉ—uwar ta da Youssouf ya kasance da yadda ta haifi Mama , samy baby ta yaudare ta, da kuma duk abubuwan da suka kasance tsakanin ita da Youssouf da danginsa baki É—aya bayan zuwan ta Niger har zuwa guduwar da Falmata tayi ta bar ta a Niger .
A Zuciyar ta ta ƙudiri aniyar tsage gaskiya kome ɗacin ta , ita bata ga Alfanun ƙarya ba , babu wata rana da ƙarya zata iya yiwa mutum illa sada shi da ranar Nadama .
Daga Khaalty Rahima har Amnee sun koka kan yadda mummunar kaddara ta faɗawa Yakaka sanadin duhun jahilci tare da zun-zurutun rashin wayo , haɗi da raunin wayewar mu'amalantar jama'ah , da kuma rashin wani babba majiɓanci a cikin rayuwar su .
Yadda zuciyar Yakaka ta cika da tsoron ko zasu yi mata faɗa ko ma su yi fushi da ita sai ta ga akasin haka , domin daga mamar su har Amnee tausayi kaɗai take iya hangowa a fuskokin su , dan haka sai ta ji ta samu nutsuwar zuciya irin wanda bata taɓa samu ba tunda igiyar rayuwa ta fara jan ta .
 A gareta yau ce rana ta farko da wasu nata makusanta na haƙiƙa suka fahimce ta ba tare da sun ƙalubalance ta ba , babu shakka babu kamar uwa Mahaifiya, ƙaunar ta ga abunda ta haifa daban ne , haka ma yawan sani da fahimtar ta ga 'ya'yan ta daban ne kamar yadda yawan uzuri da afuwar ta gare su ya hauhauwa .
  Amnee ita ta katse shirun tsakanin su inda ta cigaba da cewa ,
  "Amma takwarata , raba auren ƙanwar ki da Youssouf da kika so yi , ko kusa ba hanyar samar da mafita ba ce ba , idan kika duba yadda sharri ya biyo ta hannun sa haka nan ma Alkhairi ya zo ta hannun nasa , ki duba yadda ya riƙe auren ƙanwar ki har ma ya zama hanyar samar da lafiya a gare ta ? Bai walaƙanta ta ba duk kuwa da tazarar banbancin matakan matsayi ta kowacce fuska na rayuwa da yake tsakanin su , Baki ga yadda ya jajirce kan rayuwar ƴar sa ba har sai da Allah ya ɗauke ran ta ba tare da ya bari ta walaƙanta ba , kamar yadda sauran mafi akasarin ƴaƴan da aka samar ta wannan hanyar suke rasa tudun-dafawa iyayensu duk biyu na kƴamatar su musamman ma uba , amma sai shi ya kasance mai bata kariya da dukkanin ƙarfin sa , hatta a gaban dangi da Al'ummar sa .
"Babu shakka laifin sa maigirma ne sannan alkhairin sa kuma mai yawa ne , na fahimci irin ciwon da kika ji , kike kuma kan ji bisa dalilin faruwar kome , ina nufin auren sa da Fatima , to amma kiyi haƙuri ki rungumi kaddarar ki , ki yafe masa domin 'yar uwar ki da ya alkintawa rayuwa , ki bari su cigaba da zaman su na aure , Ubangiji Allah zai dube ki kema takwara zai baki Miji nagari wanda zai tallafawa rayuwar ki , ya rufe duk wani aibunki , ya ƙi duba zuwa duk wasu shuɗaɗɗun laifukan ki , ya zamar miki abun Alfahari , Allah yana son bayun sa masu yawan yafiya kin ji ko ?
Ta ɗago kan ta a hankali tana murmushin da iyakar sa bisa siraran laɓɓan ta , idanun ta na sheƙin hawayen da suka cika gurbin su ta ce ,
"Amnee nagode , nagode da addu'ar da ki ka min , kuma inshaAllah na yafe masa Allah ya yafe min nima ,
  Hannu ta kai ta riƙo hannun Falmata wacce tayi lamo a kwance kusa da Mamar su , ta juya musu bayan ta , duk zaman su a ɗakin bata cika cewa kome ba , a sarari damuwa mai-yawa take bayyane a fuskar ta ,
   Cikin sanyin murya Yakaka tace ,
  " Falmata ke ma ki yafe min duk wasu laifukan da nayi miki da saka ki a damuwa da tashin hankalin da nayi , ki yi haƙuri kin ji ko ? ban yi da gangan ba .
  Miƙewa zaune tayi tana riƙo hannuwan Yakaka duk biyu , muryar ta na rawa ta ce ,
  "Yakaka meyasa za ki bani haƙuri ? Bayan ke kika cike min gurbin Mahaifiya , Mahaifi ,dangin da kowa namu lokacin da muka rasa kowa ?Bayan ke ce kika dunga ɗawainiya dani Alhalin ina musaƙa ? Ke ce kike zama da yunwa domin ni naci , ke ce kika sadauƙar da rayuwa ƙarƙashin rufin ɗaki kan katifa kika zaɓi kwanan cikin zaure domin ni na kwanta ? Yakaka, ke ce fa Mamar Mama 'yar da dalilin ki samar muna da rayuwar jin daɗi kaddara ta sa aka samar da ita , 'yar da ni kuma ban so wata halitta sama da ita ba , dalilin Mama na samu lafiyar idanuna , tsawon zamana da shi Albarkacin Mama nake ci ,...
 Hannu Yakaka ta kai da nufin rufe mata baki , " ya isa Falmata ki ce kawai kin yafe min nima ,
  Janye hannun Yakaka tayi daga kan bakin ta hawayen idanun ta da suka taru suna zubowa tace ,
  " Yakaka ai ni ce zan nemi yafiyar ki akan butulcin da nayi miki , shaiɗan ne ya min huɗuba da har ya sa nayi fushi da ke , ruɗewa nayi Yakaka ban taɓa zaton abinda ya cutar da ke ni kuma zai kyautata min ba , ban yi zaton sanadiyyar shan wahalar ki ni zan samu salama ba , ban so ba kika zamto mafarauciya ni kuma cima-zaune ba , Yakaka nima bazan iya cigaba da zama da shi ba ..
  Kuka ya ci ƙarfin ta , zuciyar ta na mata zogi ,
Yakaka ma hawayen take yi a dai-dai lokacin bata da sauran kalmar da zata yi amfani da ita ta rarrashi Falmata , ta ta zuciyar ma jinya take .
****
Washe gari da safe bayan sun shirya sun yi karin-kumallo Amnee ta musu jagora zuwa wajen Prof da daman tun a jiya labarin zuwan su ya same shi , haÉ—i da dangantakar su da Amnee da Rahima .
Bayan ya amsa gaisuwar su , ya dunga bin su da kallo cike da tausayi , can daga ƙasan ran sa yana jin tamkar yana da kamasho mai yawa na kasancewar rayuwar su a haka ,
Ba domin shi da danginsa da suka ƙi auren Rahima da ɗan uwan su ba da hakan ya kawo barin Rahimar gidan da wataƙila yaran basu tashi 'ya'yan ƙauye marasa galihu irin haka ba ,
Da ace ko da mahaifiyar su da sauran 'yan uwan su sun ƙi auren , shi bai biye musu wajen nuna tsanar lamarin ba da har ya kawo saɓani tsakanin sa da Matar sa ba , ya tsayawa Rahimar har ta samu wani mijin ko da ba ɗan uwansa ba , da Rahima da yaranta basu sha wahalar rayuwa irin haka ba , da suka faɗawa hatsararruka da dama mafi munin su hatsarin Ƴan tawayen Boko Haram , da ko babu kome mutumin birni zai aura mata mai daraja da ƙima kamar ta sa .
Yana jin yanzu lokaci ne yayi da zai gyara kuskuren sa , har yanzu yana da damar sake zaɓowa Rahima wani mijin muddin ta amince , 'ya'yan ta kuwa daman Allah ya faɗo da taimakon su ta hannun sa , ashe akwai abunda Ubangiji ya ɓoye ,
Dan haka ƙudirin haɗin Auren Hamza da Yakaka da ya yi niyyar yi tuntuni ya ji ya sake kaurara a cikin ran sa , har ma ya ji dacewar matso da lamarin kusa , wataƙila da jajircewar da zai yi cikin Rayuwar Rahima da 'ya'yan ta a sauran rayuwar da ta yi masa saura zai samu ya ragewa kan sa girman laifin da yayi wajen tayawa a wargaza rayuwar Marainiyar yarinyar da take amana a wajen sa .
Cike da nuna tsantsar kulawa ya shiga jan su da hira ba tare da ya shigo musu da wata tambayar da ta shafi ɓangare na rayuwar su ba , cikin hirar da kusan su biyun ke yin ta a tsakanin su Amnee tace ,
  " Baa Alaji , a ƙira yaran nan duk a sanar da su dawowar ƴan uwan su , saboda a sa rana su zo su gana da juna ko kuwa ?
A hankali Yakaka ta mike tana kusantar inda take bayan tsayuwar kukan ta chak , zuciyarta cike da wasi-wasin gaskanta sake ganin ta , sai dai kuma ko a cikin mafarki ta ga Mahaifiyar su ai ba zata gagara gane ta ba ko me kuwa jirkituwar kamanni da ta samu mai-kyau ko mai-muni .
Tana ƙarasowa gurinta ta kai hannu a hankali tana tattaɓa jikin Khaalty Rahima, muryar ta a dishe da kukan da tayi tace ,
  "Maama ke ce ? Ke ce Mama ?
  Hannun ta da yake taɓa jikinta khaalty Rahima ta riƙe , tana cewa , "Ni ce Aminatu , Yakaka na , ni ce ,
 Yakaka tana wata ƴar Dariya-dariya , kuka-kukan da yake fallasa tsantsar ruɗanin farin-cikin da take ciki , ta waigo ga Falmata tana mai mancewa da Falmatan ta riga ta haɗuwa da Mama , ɓakin-cikin da ta shigo da shi yana zagwanyewa tace ,
  "Falmata wallahi Maman mu ce , kin ga Maman mu ? Zo ki gan ta , ta ƙarasa magana tare da yafito Falmatan da hannu ,
  Sai kuma ta juya ta rungume ta da ƙarfi tana cewa ,"Mama na, Alhamdulillah , Alhamdulillahi .
****
Daren ranar ba suyi wani baccin kirki ba su duk huÉ—un hira kawai suke yi inda cikin labarin da Yakaka ta basu ta bayyana musu ainahin yadda haÉ—uwar ta da Youssouf ya kasance da yadda ta haifi Mama , samy baby ta yaudare ta, da kuma duk abubuwan da suka kasance tsakanin ita da Youssouf da danginsa baki É—aya bayan zuwan ta Niger har zuwa guduwar da Falmata tayi ta bar ta a Niger .
A Zuciyar ta ta ƙudiri aniyar tsage gaskiya kome ɗacin ta , ita bata ga Alfanun ƙarya ba , babu wata rana da ƙarya zata iya yiwa mutum illa sada shi da ranar Nadama .
Daga Khaalty Rahima har Amnee sun koka kan yadda mummunar kaddara ta faɗawa Yakaka sanadin duhun jahilci tare da zun-zurutun rashin wayo , haɗi da raunin wayewar mu'amalantar jama'ah , da kuma rashin wani babba majiɓanci a cikin rayuwar su .
Yadda zuciyar Yakaka ta cika da tsoron ko zasu yi mata faɗa ko ma su yi fushi da ita sai ta ga akasin haka , domin daga mamar su har Amnee tausayi kaɗai take iya hangowa a fuskokin su , dan haka sai ta ji ta samu nutsuwar zuciya irin wanda bata taɓa samu ba tunda igiyar rayuwa ta fara jan ta .
 A gareta yau ce rana ta farko da wasu nata makusanta na haƙiƙa suka fahimce ta ba tare da sun ƙalubalance ta ba , babu shakka babu kamar uwa Mahaifiya, ƙaunar ta ga abunda ta haifa daban ne , haka ma yawan sani da fahimtar ta ga 'ya'yan ta daban ne kamar yadda yawan uzuri da afuwar ta gare su ya hauhauwa .
  Amnee ita ta katse shirun tsakanin su inda ta cigaba da cewa ,
  "Amma takwarata , raba auren ƙanwar ki da Youssouf da kika so yi , ko kusa ba hanyar samar da mafita ba ce ba , idan kika duba yadda sharri ya biyo ta hannun sa haka nan ma Alkhairi ya zo ta hannun nasa , ki duba yadda ya riƙe auren ƙanwar ki har ma ya zama hanyar samar da lafiya a gare ta ? Bai walaƙanta ta ba duk kuwa da tazarar banbancin matakan matsayi ta kowacce fuska na rayuwa da yake tsakanin su , Baki ga yadda ya jajirce kan rayuwar ƴar sa ba har sai da Allah ya ɗauke ran ta ba tare da ya bari ta walaƙanta ba , kamar yadda sauran mafi akasarin ƴaƴan da aka samar ta wannan hanyar suke rasa tudun-dafawa iyayensu duk biyu na kƴamatar su musamman ma uba , amma sai shi ya kasance mai bata kariya da dukkanin ƙarfin sa , hatta a gaban dangi da Al'ummar sa .
"Babu shakka laifin sa maigirma ne sannan alkhairin sa kuma mai yawa ne , na fahimci irin ciwon da kika ji , kike kuma kan ji bisa dalilin faruwar kome , ina nufin auren sa da Fatima , to amma kiyi haƙuri ki rungumi kaddarar ki , ki yafe masa domin 'yar uwar ki da ya alkintawa rayuwa , ki bari su cigaba da zaman su na aure , Ubangiji Allah zai dube ki kema takwara zai baki Miji nagari wanda zai tallafawa rayuwar ki , ya rufe duk wani aibunki , ya ƙi duba zuwa duk wasu shuɗaɗɗun laifukan ki , ya zamar miki abun Alfahari , Allah yana son bayun sa masu yawan yafiya kin ji ko ?
Ta ɗago kan ta a hankali tana murmushin da iyakar sa bisa siraran laɓɓan ta , idanun ta na sheƙin hawayen da suka cika gurbin su ta ce ,
"Amnee nagode , nagode da addu'ar da ki ka min , kuma inshaAllah na yafe masa Allah ya yafe min nima ,
  Hannu ta kai ta riƙo hannun Falmata wacce tayi lamo a kwance kusa da Mamar su , ta juya musu bayan ta , duk zaman su a ɗakin bata cika cewa kome ba , a sarari damuwa mai-yawa take bayyane a fuskar ta ,
   Cikin sanyin murya Yakaka tace ,
  " Falmata ke ma ki yafe min duk wasu laifukan da nayi miki da saka ki a damuwa da tashin hankalin da nayi , ki yi haƙuri kin ji ko ? ban yi da gangan ba .
  Miƙewa zaune tayi tana riƙo hannuwan Yakaka duk biyu , muryar ta na rawa ta ce ,
  "Yakaka meyasa za ki bani haƙuri ? Bayan ke kika cike min gurbin Mahaifiya , Mahaifi ,dangin da kowa namu lokacin da muka rasa kowa ?Bayan ke ce kika dunga ɗawainiya dani Alhalin ina musaƙa ? Ke ce kike zama da yunwa domin ni naci , ke ce kika sadauƙar da rayuwa ƙarƙashin rufin ɗaki kan katifa kika zaɓi kwanan cikin zaure domin ni na kwanta ? Yakaka, ke ce fa Mamar Mama 'yar da dalilin ki samar muna da rayuwar jin daɗi kaddara ta sa aka samar da ita , 'yar da ni kuma ban so wata halitta sama da ita ba , dalilin Mama na samu lafiyar idanuna , tsawon zamana da shi Albarkacin Mama nake ci ,...
 Hannu Yakaka ta kai da nufin rufe mata baki , " ya isa Falmata ki ce kawai kin yafe min nima ,
  Janye hannun Yakaka tayi daga kan bakin ta hawayen idanun ta da suka taru suna zubowa tace ,
  " Yakaka ai ni ce zan nemi yafiyar ki akan butulcin da nayi miki , shaiɗan ne ya min huɗuba da har ya sa nayi fushi da ke , ruɗewa nayi Yakaka ban taɓa zaton abinda ya cutar da ke ni kuma zai kyautata min ba , ban yi zaton sanadiyyar shan wahalar ki ni zan samu salama ba , ban so ba kika zamto mafarauciya ni kuma cima-zaune ba , Yakaka nima bazan iya cigaba da zama da shi ba ..
  Kuka ya ci ƙarfin ta , zuciyar ta na mata zogi ,
Yakaka ma hawayen take yi a dai-dai lokacin bata da sauran kalmar da zata yi amfani da ita ta rarrashi Falmata , ta ta zuciyar ma jinya take .
****
Washe gari da safe bayan sun shirya sun yi karin-kumallo Amnee ta musu jagora zuwa wajen Prof da daman tun a jiya labarin zuwan su ya same shi , haÉ—i da dangantakar su da Amnee da Rahima .
Bayan ya amsa gaisuwar su , ya dunga bin su da kallo cike da tausayi , can daga ƙasan ran sa yana jin tamkar yana da kamasho mai yawa na kasancewar rayuwar su a haka ,
Ba domin shi da danginsa da suka ƙi auren Rahima da ɗan uwan su ba da hakan ya kawo barin Rahimar gidan da wataƙila yaran basu tashi 'ya'yan ƙauye marasa galihu irin haka ba ,
Da ace ko da mahaifiyar su da sauran 'yan uwan su sun ƙi auren , shi bai biye musu wajen nuna tsanar lamarin ba da har ya kawo saɓani tsakanin sa da Matar sa ba , ya tsayawa Rahimar har ta samu wani mijin ko da ba ɗan uwansa ba , da Rahima da yaranta basu sha wahalar rayuwa irin haka ba , da suka faɗawa hatsararruka da dama mafi munin su hatsarin Ƴan tawayen Boko Haram , da ko babu kome mutumin birni zai aura mata mai daraja da ƙima kamar ta sa .
Yana jin yanzu lokaci ne yayi da zai gyara kuskuren sa , har yanzu yana da damar sake zaɓowa Rahima wani mijin muddin ta amince , 'ya'yan ta kuwa daman Allah ya faɗo da taimakon su ta hannun sa , ashe akwai abunda Ubangiji ya ɓoye ,
Dan haka ƙudirin haɗin Auren Hamza da Yakaka da ya yi niyyar yi tuntuni ya ji ya sake kaurara a cikin ran sa , har ma ya ji dacewar matso da lamarin kusa , wataƙila da jajircewar da zai yi cikin Rayuwar Rahima da 'ya'yan ta a sauran rayuwar da ta yi masa saura zai samu ya ragewa kan sa girman laifin da yayi wajen tayawa a wargaza rayuwar Marainiyar yarinyar da take amana a wajen sa .
Cike da nuna tsantsar kulawa ya shiga jan su da hira ba tare da ya shigo musu da wata tambayar da ta shafi ɓangare na rayuwar su ba , cikin hirar da kusan su biyun ke yin ta a tsakanin su Amnee tace ,
  " Baa Alaji , a ƙira yaran nan duk a sanar da su dawowar ƴan uwan su , saboda a sa rana su zo su gana da juna ko kuwa ?