Sashe 203
Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ganin damuwar ta na neman kai ta ƙasa , sai ta nemi Gnala da ta bincika mata wanene wannan sabon balaraben bawa ? me kuma yasa ta daina ganin sa ? Ko an sauya masa shiyar aiki ne ?
Ba'a ɗauki wasu kwanaki ba ta samu duk wasu bayanai game da Ghaddafi , sunan sa , asalin sa , iyayen sa da laifin da suka yi har aka kawo ƙarar su ga Maimartaba aka hukunta su .
Kuka ta zauna tana yi sosai , so take ta tunbuƙe son shi daga ran ta ji da tayi ko kusa basu dace da juna ba , shi ɗin maƙasƙanci ne ko a cikin maƙasƙanta ko ɗaya ba shi da nagarta da ya dace da samun soyayyar ta .
To sai dai ita zuciyar da so na farko ya fara fasawa ya dasu a cikin ta tauri ne da ita tare da ƙwalafaci , dan haka bayan wasu kwanaki kaɗan sai ciwon son shi ya dawo mata sabo fil ,
Jin ba zata jure rashin ganin sa ba yasa bayan ta samu tabbacin inda yake zama da la'asar sai kawai tayi badda-kama cikin baƙaƙen kayan su na buzaye ta rufe rabin fuskar ta da mayafin ta , ta ratsa sorayen gidan su ba tare da ta bari kowa ya gane ta ba ta fice daga gidan su rana tana daf da faɗuwa , bata ko damu da iskar hunturu wacce ke tayar da rai-rayi da take ta busawa tana tila ƙasa a idanu hanci har ma da kunnuwan al'umma ba ,
Kasantuwar bata saba fita ita kaɗai ba hasalima yau ce rana ta farko da ta taɓa tako ƙafafun ta shiyar unguwar da take baya da Masarautar su da take ta talakawan liƙis , sai tayi ɓatan kai , ta gagara gane kwatancen da Gnala ta yi na inda aka ce Ghaddafi yana zama , ta nemi hanyar jirgin ƙasa ta rasa .
Ƙura tayi buɗu-buɗu da baƙaken kayan jikin ta , magariba kuma ta kawo kai , da kyar ta samu ta tsayar da wata budurwa ta tambaye ta ina ne tsohon hanyar jirgin ƙasa ?
Budurwar ta gwada mata hanyar da hannu, juyawa tayi da sauri ba tare da ta ko yi mata godiya ba ta fara taku zuwa kan hanyar da ta mata nuni ,
 " hala can kike noufin zouwa ? Ko kouwa kin san da kwai hatsari bissa hanyar kou ? Kin san fa an sau waɗannan tsinananan samari da suke ratse bissa hanya nan , a shawarce kadda ki bi ta wannan hanyar war hakka .
  Tsayawa tayi cak , ba ta juyo bata kuma ce ƙala ba , sai ta sake kaɗa kan ta tayi gaba ta miƙa sosai a hanyar har ta tarar da matattciyar hanyar jirgin ƙasan da duk bola ta mamaye ta ,
Warin da yake wajen ya sanyata rufe hancin ta tana tsallaka tsumi-tsumin bolar da take wajen ,
Shal hanyar take babu kowa ko Æ´an dabbobin da suke kiwo akan bolar babu kowa ya kaÉ—a dabbar sa gida kafin a sibare masa ita gobe kasuwa .
Sai hange-hange take yi cike da burin son ganin sa ,
Taku ta fara ji daga bayan ta kafin warin taba ya mamaye ƙofofin hancin ta ,
Da sauri ta juyo karaf suka haÉ—a ido da shi tare da waÉ—ansu samari biyu daga dama da hagun sa ,
Daga cikin mayafin ta ta saki tattausan murmushi zuciyar ta na cika da farin-cikin sake ganin sa ,
Warware mayafin fuskar ta tayi , ranar da tayi jazur gaf da faɗuwa ta haske ta tana ƙarawa farar fuskar ta jaa da kyau , cikin siririyar muryar ta tace " Ghaddafi wajen ka na taho .
Zaro ido yayi yana daɗa kallon ta , babu shakka wannan gimbiyar nan ce ɗiyar sarki to me ya kawo ta wajen nan me kuma take nema a wajen sa ?? Hayaƙin tabar da ya cika bakin sa da ita ya fesar ta hanci ta baki .
Tun bayan wannan ranar sai soyayya mai ƙarfi ta ƙullu tsakanin ƙananan matasan biyu ba tare da tunanin me ke je ya dawo ba , soyayyar junan su ta rufe musu ido daga hango tarin banbancin dake tsakanin su ,
Cikin watanni shidda sun yi wata irin shaƙuwa ta ban mamaki duk kuwa da cewa daga ɓangaren ita Gimbiya maimounatou babu wanda yasan da batun soyayyar su ita da Ghaddafi , sau biyu kawai suka taɓa haɗuwa , rana ta farko da ta je wajen sa sai kuma rana ta biyu da ta kai masa kyautar wayar tafi da gidanka sabuwa dal , da ta sa Mahaifiyar ta ta saya mata lokacin ma wayar sai hannun wane-da-wane tare da wasu kuɗaɗe masu yawa .
Zancen tafiyar ta makarantar jami'a ta babbar birnin Niamey shine ya tayar da hankalin su , saboda nisa da zasu yi da juna .
A gobe zata tafi makaranta , ta saci jiki kamar yadda ta saba ta je wajen sa da hantsi ,
Akan Æ´ar rusasshiyar katangar wani kangon gida ta tarar da shi , a shirye tsaf yake cikin wandon gonjo da rigar sanyi mai haÉ—e da hula da ya saya daga cikin kuÉ—in da ta masa kyautar su .
Yana daga sama yayi mata nuni da gefen sa kan katangar akan ta hauro ta zauna ,
Dariya tayi da haƙoranta tana kaɗa kai tace
  " Bani iya hawa bissa nan ai kaima ka sani ,
Murmushi yayi ya diro ƙasa bata ankara ba ya ɗaga ta ya ɗora ta kan katangar runtse ido tayi zuciyar ta cike da tsoro ,
Bata san zaman sa a gefen ta ba sai da ya zunguri kafaɗar ta , a hankali ta wara ido tana kallon sa , sam ta kasa sabo da takaɗarancin Ghaddafi ita bata saba irin wannan rayuwar ta ƙarancin tarbiyya ba .
  Cikin muryar sa mai sanyi sosai ba'a ce daga bakin sa amon ta ke tasowa ba yace ,
   " ranki shi daɗe ai bashi kamata ba ke kina ƙasa ni ina sama tsololo , ke ai gimbiya ce ɗiyar sarki ni tamkar bawa nake a gare ki ,
  Hararar sa tayi sai kuma tayi murmushi , a hankali tace
  " bana so kana taɓa min jikina , kuma kai baka cikin jerun bayun gangar jikina amma zan yi farin ciki da zaka zama bawan zuciyata .
  Murmushi yayi mai sauti , " ai tun-tuni nake hadimi ga zuciyar ki gimbiyata , amma meyasa bakya son ina taɓa ki ? Ya tambaye ta yana kallon gefen fuskar ta
  " kawai ba yanzou ba , ta bashi amsa
" sai yaushe , yace yana shilla ƙafar sa
  " sai mun yi amre kou ? Ta ce tana rufe fuskar ta da tafukan hannun ta duk biyu .
 Ganin sa ya dawo kan ta , kafin ya ɗauke kan sa zuwa sama kaɗan da wata muryar dake bayyana ciwon zuci yace
  " Maimounatou bani da matsayi , nagarta , kyaun asali kou dukiyar amren ki , ke ɗin kouma ai shaida ce bisa hakka .
Ganin ta ta mayar kan sa , tana jin yanayin ta na nishaÉ—i na jirkituwa zuwa tashin hankali da damuwa tace ,
 " Amma ai muna ƙamnar juna , abunda ka lissafa bai issa hana amren mou ba , tunda ai zaka iya sauya halaye sannan kouma kai Namiji ne kana da ƙarfi neman dukiya ko baka iya zage damtse wajen neman dukiyar amre na ?
 Idanun sa da suka fara yin jaa ya nitsar cikin nata raunanan idanun ,
 " ta wacce hanya zan nemi dukiyar amren ki maimounatou baya.....
  Katse shi tayi jin yana shirin ɓata mata walwalar ta ta yau baki ɗaya alhalin kuma bankwana ta zo su yi , tace da shi
  " ka nemi dukiyar Amren Maimounatou ko ta wacce hanya Ghaddafi , buƙatata kawai muyi aure dagga na kammala ecole .
****
Bayan tafiyar Maimounatou sun cigaba da kasancewa a waya ita da Ghaddafi suna sake cinye zuciyoyin juna da so da ƙaunar juna ,
Basu sake haÉ—uwa ba sai bayan shekara guda a ranar da take ta zagayowar haihuwar Maimounatou ,
Babu zato aka sanar mata da sakon ƙiran da wani baƙo ke yi mata a can filin makaranta , tayi mamaki sosai saboda duk cikar jami'ar babu wani ɗa namiji ɗaya da suke ko da gaisuwar kirki ne .
Amma haka kawai ta ji zuciyar ta na son zuwa amsa ƙiran koma wanene , dan haka ta kama hanyar inda aka kwatanta mata
A tsaye ta tarar da mai ƙiran nata ya bada baya a jikin wata ƴar ƙaramar mota ƙirar golf da ta sha jaan fenti tana ta ɗaukar ido .
Daga sama har ƙasa take kallon sa zuciyar ta na kai-kawo wajen tantance shi ɗin ne ko ba shi bane ?
Juyowar da yayi ya hutatshe da zuciyar ta daga tunanin tantance shi , saɓanin haka zallar farin ciki ta ji yana tunbuƙowa daga ƙasan ranta , tamkar tayi tsalle ta rungume shi take ji a lokacin
  Hannunta biyu ta kai tana rufe bakin ta da haƙoranta ke buɗe tana dariya , sai kuma tayi ɗan tsalle tana matsawa daf da shi ta haɗo haruffan sunan sa cikin wani irin sauti mai nuni da ɗoki da farin-ciki da take ciki tace.
   " Gha°ddafi ? Kai ne ? je ne peux pas croire mes yeux mon amour ,
  Dariya yake lokacin da ya zare baƙin tabarau ɗin dake idanun sa , cike da murnar ganin ta ya kai hannu ya riƙo hannuwanta ya jaa ta yana ƙarasa rufe tazarar dake tsakanin su ya haɗa ta da jikin sa , cike da salon son ya burge ta ya harhaɗo kalmomin da ya shafe tsawon wata guda yana koyon su yace ,
   " tu m'as tellement manqué chérie ,
Ba'a ɗauki wasu kwanaki ba ta samu duk wasu bayanai game da Ghaddafi , sunan sa , asalin sa , iyayen sa da laifin da suka yi har aka kawo ƙarar su ga Maimartaba aka hukunta su .
Kuka ta zauna tana yi sosai , so take ta tunbuƙe son shi daga ran ta ji da tayi ko kusa basu dace da juna ba , shi ɗin maƙasƙanci ne ko a cikin maƙasƙanta ko ɗaya ba shi da nagarta da ya dace da samun soyayyar ta .
To sai dai ita zuciyar da so na farko ya fara fasawa ya dasu a cikin ta tauri ne da ita tare da ƙwalafaci , dan haka bayan wasu kwanaki kaɗan sai ciwon son shi ya dawo mata sabo fil ,
Jin ba zata jure rashin ganin sa ba yasa bayan ta samu tabbacin inda yake zama da la'asar sai kawai tayi badda-kama cikin baƙaƙen kayan su na buzaye ta rufe rabin fuskar ta da mayafin ta , ta ratsa sorayen gidan su ba tare da ta bari kowa ya gane ta ba ta fice daga gidan su rana tana daf da faɗuwa , bata ko damu da iskar hunturu wacce ke tayar da rai-rayi da take ta busawa tana tila ƙasa a idanu hanci har ma da kunnuwan al'umma ba ,
Kasantuwar bata saba fita ita kaɗai ba hasalima yau ce rana ta farko da ta taɓa tako ƙafafun ta shiyar unguwar da take baya da Masarautar su da take ta talakawan liƙis , sai tayi ɓatan kai , ta gagara gane kwatancen da Gnala ta yi na inda aka ce Ghaddafi yana zama , ta nemi hanyar jirgin ƙasa ta rasa .
Ƙura tayi buɗu-buɗu da baƙaken kayan jikin ta , magariba kuma ta kawo kai , da kyar ta samu ta tsayar da wata budurwa ta tambaye ta ina ne tsohon hanyar jirgin ƙasa ?
Budurwar ta gwada mata hanyar da hannu, juyawa tayi da sauri ba tare da ta ko yi mata godiya ba ta fara taku zuwa kan hanyar da ta mata nuni ,
 " hala can kike noufin zouwa ? Ko kouwa kin san da kwai hatsari bissa hanyar kou ? Kin san fa an sau waɗannan tsinananan samari da suke ratse bissa hanya nan , a shawarce kadda ki bi ta wannan hanyar war hakka .
  Tsayawa tayi cak , ba ta juyo bata kuma ce ƙala ba , sai ta sake kaɗa kan ta tayi gaba ta miƙa sosai a hanyar har ta tarar da matattciyar hanyar jirgin ƙasan da duk bola ta mamaye ta ,
Warin da yake wajen ya sanyata rufe hancin ta tana tsallaka tsumi-tsumin bolar da take wajen ,
Shal hanyar take babu kowa ko Æ´an dabbobin da suke kiwo akan bolar babu kowa ya kaÉ—a dabbar sa gida kafin a sibare masa ita gobe kasuwa .
Sai hange-hange take yi cike da burin son ganin sa ,
Taku ta fara ji daga bayan ta kafin warin taba ya mamaye ƙofofin hancin ta ,
Da sauri ta juyo karaf suka haÉ—a ido da shi tare da waÉ—ansu samari biyu daga dama da hagun sa ,
Daga cikin mayafin ta ta saki tattausan murmushi zuciyar ta na cika da farin-cikin sake ganin sa ,
Warware mayafin fuskar ta tayi , ranar da tayi jazur gaf da faɗuwa ta haske ta tana ƙarawa farar fuskar ta jaa da kyau , cikin siririyar muryar ta tace " Ghaddafi wajen ka na taho .
Zaro ido yayi yana daɗa kallon ta , babu shakka wannan gimbiyar nan ce ɗiyar sarki to me ya kawo ta wajen nan me kuma take nema a wajen sa ?? Hayaƙin tabar da ya cika bakin sa da ita ya fesar ta hanci ta baki .
Tun bayan wannan ranar sai soyayya mai ƙarfi ta ƙullu tsakanin ƙananan matasan biyu ba tare da tunanin me ke je ya dawo ba , soyayyar junan su ta rufe musu ido daga hango tarin banbancin dake tsakanin su ,
Cikin watanni shidda sun yi wata irin shaƙuwa ta ban mamaki duk kuwa da cewa daga ɓangaren ita Gimbiya maimounatou babu wanda yasan da batun soyayyar su ita da Ghaddafi , sau biyu kawai suka taɓa haɗuwa , rana ta farko da ta je wajen sa sai kuma rana ta biyu da ta kai masa kyautar wayar tafi da gidanka sabuwa dal , da ta sa Mahaifiyar ta ta saya mata lokacin ma wayar sai hannun wane-da-wane tare da wasu kuɗaɗe masu yawa .
Zancen tafiyar ta makarantar jami'a ta babbar birnin Niamey shine ya tayar da hankalin su , saboda nisa da zasu yi da juna .
A gobe zata tafi makaranta , ta saci jiki kamar yadda ta saba ta je wajen sa da hantsi ,
Akan Æ´ar rusasshiyar katangar wani kangon gida ta tarar da shi , a shirye tsaf yake cikin wandon gonjo da rigar sanyi mai haÉ—e da hula da ya saya daga cikin kuÉ—in da ta masa kyautar su .
Yana daga sama yayi mata nuni da gefen sa kan katangar akan ta hauro ta zauna ,
Dariya tayi da haƙoranta tana kaɗa kai tace
  " Bani iya hawa bissa nan ai kaima ka sani ,
Murmushi yayi ya diro ƙasa bata ankara ba ya ɗaga ta ya ɗora ta kan katangar runtse ido tayi zuciyar ta cike da tsoro ,
Bata san zaman sa a gefen ta ba sai da ya zunguri kafaɗar ta , a hankali ta wara ido tana kallon sa , sam ta kasa sabo da takaɗarancin Ghaddafi ita bata saba irin wannan rayuwar ta ƙarancin tarbiyya ba .
  Cikin muryar sa mai sanyi sosai ba'a ce daga bakin sa amon ta ke tasowa ba yace ,
   " ranki shi daɗe ai bashi kamata ba ke kina ƙasa ni ina sama tsololo , ke ai gimbiya ce ɗiyar sarki ni tamkar bawa nake a gare ki ,
  Hararar sa tayi sai kuma tayi murmushi , a hankali tace
  " bana so kana taɓa min jikina , kuma kai baka cikin jerun bayun gangar jikina amma zan yi farin ciki da zaka zama bawan zuciyata .
  Murmushi yayi mai sauti , " ai tun-tuni nake hadimi ga zuciyar ki gimbiyata , amma meyasa bakya son ina taɓa ki ? Ya tambaye ta yana kallon gefen fuskar ta
  " kawai ba yanzou ba , ta bashi amsa
" sai yaushe , yace yana shilla ƙafar sa
  " sai mun yi amre kou ? Ta ce tana rufe fuskar ta da tafukan hannun ta duk biyu .
 Ganin sa ya dawo kan ta , kafin ya ɗauke kan sa zuwa sama kaɗan da wata muryar dake bayyana ciwon zuci yace
  " Maimounatou bani da matsayi , nagarta , kyaun asali kou dukiyar amren ki , ke ɗin kouma ai shaida ce bisa hakka .
Ganin ta ta mayar kan sa , tana jin yanayin ta na nishaÉ—i na jirkituwa zuwa tashin hankali da damuwa tace ,
 " Amma ai muna ƙamnar juna , abunda ka lissafa bai issa hana amren mou ba , tunda ai zaka iya sauya halaye sannan kouma kai Namiji ne kana da ƙarfi neman dukiya ko baka iya zage damtse wajen neman dukiyar amre na ?
 Idanun sa da suka fara yin jaa ya nitsar cikin nata raunanan idanun ,
 " ta wacce hanya zan nemi dukiyar amren ki maimounatou baya.....
  Katse shi tayi jin yana shirin ɓata mata walwalar ta ta yau baki ɗaya alhalin kuma bankwana ta zo su yi , tace da shi
  " ka nemi dukiyar Amren Maimounatou ko ta wacce hanya Ghaddafi , buƙatata kawai muyi aure dagga na kammala ecole .
****
Bayan tafiyar Maimounatou sun cigaba da kasancewa a waya ita da Ghaddafi suna sake cinye zuciyoyin juna da so da ƙaunar juna ,
Basu sake haÉ—uwa ba sai bayan shekara guda a ranar da take ta zagayowar haihuwar Maimounatou ,
Babu zato aka sanar mata da sakon ƙiran da wani baƙo ke yi mata a can filin makaranta , tayi mamaki sosai saboda duk cikar jami'ar babu wani ɗa namiji ɗaya da suke ko da gaisuwar kirki ne .
Amma haka kawai ta ji zuciyar ta na son zuwa amsa ƙiran koma wanene , dan haka ta kama hanyar inda aka kwatanta mata
A tsaye ta tarar da mai ƙiran nata ya bada baya a jikin wata ƴar ƙaramar mota ƙirar golf da ta sha jaan fenti tana ta ɗaukar ido .
Daga sama har ƙasa take kallon sa zuciyar ta na kai-kawo wajen tantance shi ɗin ne ko ba shi bane ?
Juyowar da yayi ya hutatshe da zuciyar ta daga tunanin tantance shi , saɓanin haka zallar farin ciki ta ji yana tunbuƙowa daga ƙasan ranta , tamkar tayi tsalle ta rungume shi take ji a lokacin
  Hannunta biyu ta kai tana rufe bakin ta da haƙoranta ke buɗe tana dariya , sai kuma tayi ɗan tsalle tana matsawa daf da shi ta haɗo haruffan sunan sa cikin wani irin sauti mai nuni da ɗoki da farin-ciki da take ciki tace.
   " Gha°ddafi ? Kai ne ? je ne peux pas croire mes yeux mon amour ,
  Dariya yake lokacin da ya zare baƙin tabarau ɗin dake idanun sa , cike da murnar ganin ta ya kai hannu ya riƙo hannuwanta ya jaa ta yana ƙarasa rufe tazarar dake tsakanin su ya haɗa ta da jikin sa , cike da salon son ya burge ta ya harhaɗo kalmomin da ya shafe tsawon wata guda yana koyon su yace ,
   " tu m'as tellement manqué chérie ,