Sashe 268
Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da zuwa zata sake dasa sabuwar ƙarya ta tarar da ashe tuni kome ya jima da kwaɓe mata asirin ta ya daɗe da tonuwa kowa kuma yasan abunda ya faru abunda ta aikata da irin hukuncin da Hamza ya yanke mata .
Babban tashin hankalin ta yadda tana ji tana gani Baban su da ya dawo ƙasar kwanaki biyu da suka wuce ya kore ta a gidan bayan ya ƙare mata tanadi .
Gidan wata dangin dangau ɗin Hajiya Kori da take mata kore a can irin unguwannin kusa da ƙyaukan Abuja nan Hajiya Kori ta sa direba ya kai Sofi ba tare da sanin Mahaifin ta ba domin idan ta shi ne kawai Sofi tayi tafiyar ta Momy kori ta ce ta zauna a can kafin Baban ta ya huce ya saurare ta .
Bata haƙƙaƙe da babu wata sa'a da ta rage mata a rayuwa ba sai da aka shafe fiye da kwanaki arba'in tana ƙirgawa babu Samy Baby ba labarin ta .
Zuwa lokacin ta haƙiƙance cikin biyu ɗaya ne ko dai Samira ta yaudare ta ta mata damfara ta gudu a duniya ko kuwa ta gamu da mummunan hatsarin da ya rutsa da rayuwar ta a can india ba tare da an mata aikin da ta aiketa yi ba .
Ƙurunƙus sai gaba ɗaya mummunar zuciyar ta da shaiɗan da bai riga ya gama cika aikin sa akan ta ba suka cigaba da mata raɗa cewar ai babu wani amfanin da rayuwa za ta iya sake mata nan gaba .
Dan haka sai kawai ta afkama shaye-shayen miyagun ƙwayoyin da basu cika tsada ba sai mugun aiki dan da haka kaɗai take iya samu ta hasko kan ta a irin rayuwar da ta kwashi shekaru tana tsarawa a kan ta ita da Doctor Hamza.
Kafin wasu watanni ta yiwa rayuwar ta illa ga kuma ciwon da yake daɗa cin jikin ta gaba ɗaya ta sururuce ta koma irin mutanen da ƙwaya ta gama musu illa a rayuwa suka zama marasa amfanin da ba zasu iya yiwa kan su ba ma bare su yiwa wani .
To ai daman a rayuwa muddin ShaiÉ—an ya zama jagorar ka ba zai kauce ba har sai ya kai ka tsakiyar kogin nadama da ba kuma za ka iya fiddo da kan ka ba.
***
Yakaka da Doctor Hamza kamar kullum suna kitchen da safe suna aikin su tare da dai mafi yawan aikin Doctor Hamza ne ke yi saboda kome Yakaka ta É—auka za tayi sai ya hana yace kar ta wahalar da kan ta da Babyn sa .
Suna gaf da kammala haɗa abun Breakfast ɗin su tattabarun rannan suka sauƙo sai dai a yau su uku ne tare da su da 'yar wata matashiyar tattabara da duk alamu ba'a jima da fara fita da ita kiwo ba.
Da sauri Yakaka ta nuna masa su tana cewa "Laa Habibi ka ga tattabarun mu na rannan har sun samu baby ko ba su bane .?
Da sauri Doctor Hamza ya mayar da ganin su kan sa yama dariya yace "ai kuwa sune wai har sun haihu ? Gaskiya sun yi ƙoƙari .
"Ba dan nima dai ga nawa Babyn yana hanya ba ai da sai nace sun cinye mu a wasan .
Dariya Yakaka tayi tana É—iban 'yar shinkafa ta watsa musu kafin ta taya shi su kwashe abincin karyarwar su kai falo .
Bayan sun gama brakfast suka yi wanka Yakaka ta taya shi ya shirya suna yi suna 'yar soyayyar su da ba'a cika magana a cikin ta sai da suka fito za ta masa rakiya yana riƙe da kunkumin ta sannan yace "Wafaa kin ga na manta har zan fita ban sanar da ke ba ƙanwar abokin aikina da yake nan unguwar ai kin san shi ko Doctor Abdallah ?
GyaÉ—a kai Yakaka tayi tana jin zuciyar ta na sauya bugu da ba ma zata iya bada amsa da baki ba.
Murmushi Doctor Hamza yayi yana mayar da ƙofa ya rufe ya jawo ta jikin sa ya matso da ita Sosai cikin ta ne kawai ya tokare ya hana haɗuwar ƙirjin su .
Muryar sa a ƙasa-ƙasa yace faɗa min meye a zuciyar ki na ji ta sauya bugu me kike tunani ?
Girgiza kai ta sake yi cike da ƙagautuwa ta ji ƙarshen zance tace "ba kome , habibi me ya faru da ƙanwar Doctor Abdallah ?
'Yar sassauƙar dariya yayi ya jaa karan hancin ta kafin yace " sunan ta Madina ma'aikaciya ce a ƙungiya mai zaman kanta da take bada tallafi ga kasashen da annoba ta fadawa a sakamkon yaki ko na ɓullar cutuka watau NGOs babbar ma'aikaciya ce a kungiyar da bata dade da da dawowa daga...
Cike da gundura Yakaka ta Katse shi "Habibi mana to ni meye alakata da ita?
Wannan karon dariyar da yake gintsewa ita ce ta bayyana ya shiga kyakyatawa ganin haka yasa idanun Yakaka cika da ƙwalla ta fara ƙoƙarin zamewa ta bar gurin .
Da sauri ya riƙo ta gaba ɗaya ya rungume ta a jikin sa yana dai-daita nutsuwar sa daga barin yin dariyar da yake yace "Wafaa aina kika koyi kishi haka un ?? Haka kike sona ashe ? Ki kwantar da hankalin ki Wafaa ni naki ne ke kaɗai da yardar Allah babu wacce zata sake ratsa tsakanin mu ke kaɗai kin isheni rayuwar duniya kin ji ko ?
A tare suka yi ajiyar zuciya kafin ya cigaba da cewa "Abdallah shine ya bani labarin ƙanwar sa da shirin da take yi na tafiya Maiduguri domin yin aiki dalilin da yasa ya min zancen domin ya ji yaya lafiyar garin yake ? To bayan na ba shi amsar da ta dace shine har ma na ɗan ba shi bayani akan labarin rayuwar ku yadda kuka kasance a matsayin 'yan gudun Hijira har ma ya sake jimantawa to ashe ya faɗawa ita ƙanwar ta shi sai jiya yake shaida min cewar wai na nemawar Madina izni idan har kin amince tana so ta zo yau ta ɗan tattauna da ke kan yadda rayuwa ta kasance muku a Sanadin Boko Haram .
Ya ɗan tsahirta kafin ya ɗora da cigaba da cewa "Wafaa da fatan ban saɓa miki ba da na bada wani ɓangare na labarin ku ba tare da amin....
Da sauri Yakaka ta rufe masa baki da lallausan hannun ta tana girgiza masa kai tace "Habibi kar kace haka ni wallahi baka min laifin kome ba ina maraba da Madina kace ta zo insha Allah za ta iya samun duk wasu bayanai daga bakina daidai gwargawdon yadda rayuwar mu ta kasance .
Sumbatar ta yayi a goshi kafin ya sake ta yana jin yadda take ƙara shiga ransa saboda sanyin halin ta .
Daga nan rakiya ta masa ya tafi cike da kewar juna da suke ji a koyaushe idan zasu yi rabo da juna ko da na awa guda ne .
Bayan ta dawo cikin gidan da ƙwazo irin nata ta gyara gidan tsaf tana yi tana hanzari tana duba waya dan kar lokacin ƙiran ta kula da Ukhtee yayi .
Ta gama ƙarfe tara cif tana zama kuma Falmata ta ƙira ta a skype bayan sun gaisa Falmata tana tsokanar ta Maman biyu sai ta haɗa Su da Ukhtee ita ta shiga lectures.
Da kamar kullum idan za ta shiga lectures da take yi a sati sau uku Ukhtee bata yarda da mai rainon ta ta riƙe ta har Falmata ta gama ihu za tayi ta yi tana kuka .
Sai fa idan an ƙira Yakaka a Skype an haɗa su nan ne kuma babu ruwan ta da Falmata bare wata mai raino za tayi ta damuƙar wayar tana gwalatu da dariya Yakaka na biye mata tana mata wasa har tayi bacci idan ta farka kafin Falmata ta fito Yakaka za'a sake ƙira ta kula da ita ta waya .
Wata irin ƙauna da shaƙuwa ce ta ban mamaki a tsakanin Su biyu yadda Ukhtee ta gane da Falmata da Baban ta haka ta gane da Yakaka haka kuma take son ta .
Sai da ta gama mata wasa ta samu tayi bacci sannan suka yi sallama da mai rainon ta ajiye wayar fuskarta ɗauke da murmushi tana jin ƙarin ƙaunar Ukhtee na bin jikin ta "daga an yaye ki zan je na ɗauko ki takwara koda kuwa Baban ki baya so sai dai yayi haƙuri sa samu wasu bayan ke amma ke kam tawa ce 'yata 'yar gidana.
Ta furta hakan a sarari dai-dai lokacin da aka ƙwanƙwasa ƙofar gidan.
A hankali ta miƙe tana ɗan tura cikin ta gaba da duk cikin watannin sa biyar amma yayi girma sosai "Matar likita ko 'yan tagwaye zata haifa ?
Lokacin da ta buɗe ƙofar sai ta ci karo da wata kyakkyawar mace da zata girme mata da kaɗan a shekaru wacce kallo ɗaya tal za'a mata a hango tarin ilmin Boko da wayewar da suka samun wajen zama na dindin a tare da ita bayan hutu da yake numfasawa a jikin ta .
Daga kan takalman ƙafafun ta marasa tudu har kan ɗan farin gilashin da yake saƙale akan doron siririn karan hancin suna nuni ne da irin tsadaddiyar rayuwar da take yi ta 'ya'yan gata 'ya'yan manya.
"Madina ce .
Yakaka ta aiyana hakan a cikin ran ta kafin ta ɗan sake faɗaɗa fuskar ta da murmushi cikin muryar ta mai sanyin ta ce "sannu da zuwa ki shigo mana .
Da taƙaitatciyar Sallama ta shiga gidan kamar yadda fuskar ta ma ke ɗauke da taƙaitatcen murmushi.
Bayan sun gaisa Yakaka ta kawo mata zoɓo mai sanyi da yake tashin ƙamshin kayan shai irin na mutan Ndjamena da take ƙamshin ya ɗau hankalin Madina '
Bayan sun ɗan taɓa hira lokacin da Madina take shan Zoɓon da daɗin sa yake ratsa ta "bata taɓa zaton irin wannan local juice ɗin yana da daɗi haka ba , ta aiyana hakan a cikin ranta.
Da ta gama sha sai ta fuskanci Yakaka sosai ta sake gabatar da kan ta tare da yi mata godiya da amincewar da tayi ta bata damar tattaunawa da ita .
Babban tashin hankalin ta yadda tana ji tana gani Baban su da ya dawo ƙasar kwanaki biyu da suka wuce ya kore ta a gidan bayan ya ƙare mata tanadi .
Gidan wata dangin dangau ɗin Hajiya Kori da take mata kore a can irin unguwannin kusa da ƙyaukan Abuja nan Hajiya Kori ta sa direba ya kai Sofi ba tare da sanin Mahaifin ta ba domin idan ta shi ne kawai Sofi tayi tafiyar ta Momy kori ta ce ta zauna a can kafin Baban ta ya huce ya saurare ta .
Bata haƙƙaƙe da babu wata sa'a da ta rage mata a rayuwa ba sai da aka shafe fiye da kwanaki arba'in tana ƙirgawa babu Samy Baby ba labarin ta .
Zuwa lokacin ta haƙiƙance cikin biyu ɗaya ne ko dai Samira ta yaudare ta ta mata damfara ta gudu a duniya ko kuwa ta gamu da mummunan hatsarin da ya rutsa da rayuwar ta a can india ba tare da an mata aikin da ta aiketa yi ba .
Ƙurunƙus sai gaba ɗaya mummunar zuciyar ta da shaiɗan da bai riga ya gama cika aikin sa akan ta ba suka cigaba da mata raɗa cewar ai babu wani amfanin da rayuwa za ta iya sake mata nan gaba .
Dan haka sai kawai ta afkama shaye-shayen miyagun ƙwayoyin da basu cika tsada ba sai mugun aiki dan da haka kaɗai take iya samu ta hasko kan ta a irin rayuwar da ta kwashi shekaru tana tsarawa a kan ta ita da Doctor Hamza.
Kafin wasu watanni ta yiwa rayuwar ta illa ga kuma ciwon da yake daɗa cin jikin ta gaba ɗaya ta sururuce ta koma irin mutanen da ƙwaya ta gama musu illa a rayuwa suka zama marasa amfanin da ba zasu iya yiwa kan su ba ma bare su yiwa wani .
To ai daman a rayuwa muddin ShaiÉ—an ya zama jagorar ka ba zai kauce ba har sai ya kai ka tsakiyar kogin nadama da ba kuma za ka iya fiddo da kan ka ba.
***
Yakaka da Doctor Hamza kamar kullum suna kitchen da safe suna aikin su tare da dai mafi yawan aikin Doctor Hamza ne ke yi saboda kome Yakaka ta É—auka za tayi sai ya hana yace kar ta wahalar da kan ta da Babyn sa .
Suna gaf da kammala haɗa abun Breakfast ɗin su tattabarun rannan suka sauƙo sai dai a yau su uku ne tare da su da 'yar wata matashiyar tattabara da duk alamu ba'a jima da fara fita da ita kiwo ba.
Da sauri Yakaka ta nuna masa su tana cewa "Laa Habibi ka ga tattabarun mu na rannan har sun samu baby ko ba su bane .?
Da sauri Doctor Hamza ya mayar da ganin su kan sa yama dariya yace "ai kuwa sune wai har sun haihu ? Gaskiya sun yi ƙoƙari .
"Ba dan nima dai ga nawa Babyn yana hanya ba ai da sai nace sun cinye mu a wasan .
Dariya Yakaka tayi tana É—iban 'yar shinkafa ta watsa musu kafin ta taya shi su kwashe abincin karyarwar su kai falo .
Bayan sun gama brakfast suka yi wanka Yakaka ta taya shi ya shirya suna yi suna 'yar soyayyar su da ba'a cika magana a cikin ta sai da suka fito za ta masa rakiya yana riƙe da kunkumin ta sannan yace "Wafaa kin ga na manta har zan fita ban sanar da ke ba ƙanwar abokin aikina da yake nan unguwar ai kin san shi ko Doctor Abdallah ?
GyaÉ—a kai Yakaka tayi tana jin zuciyar ta na sauya bugu da ba ma zata iya bada amsa da baki ba.
Murmushi Doctor Hamza yayi yana mayar da ƙofa ya rufe ya jawo ta jikin sa ya matso da ita Sosai cikin ta ne kawai ya tokare ya hana haɗuwar ƙirjin su .
Muryar sa a ƙasa-ƙasa yace faɗa min meye a zuciyar ki na ji ta sauya bugu me kike tunani ?
Girgiza kai ta sake yi cike da ƙagautuwa ta ji ƙarshen zance tace "ba kome , habibi me ya faru da ƙanwar Doctor Abdallah ?
'Yar sassauƙar dariya yayi ya jaa karan hancin ta kafin yace " sunan ta Madina ma'aikaciya ce a ƙungiya mai zaman kanta da take bada tallafi ga kasashen da annoba ta fadawa a sakamkon yaki ko na ɓullar cutuka watau NGOs babbar ma'aikaciya ce a kungiyar da bata dade da da dawowa daga...
Cike da gundura Yakaka ta Katse shi "Habibi mana to ni meye alakata da ita?
Wannan karon dariyar da yake gintsewa ita ce ta bayyana ya shiga kyakyatawa ganin haka yasa idanun Yakaka cika da ƙwalla ta fara ƙoƙarin zamewa ta bar gurin .
Da sauri ya riƙo ta gaba ɗaya ya rungume ta a jikin sa yana dai-daita nutsuwar sa daga barin yin dariyar da yake yace "Wafaa aina kika koyi kishi haka un ?? Haka kike sona ashe ? Ki kwantar da hankalin ki Wafaa ni naki ne ke kaɗai da yardar Allah babu wacce zata sake ratsa tsakanin mu ke kaɗai kin isheni rayuwar duniya kin ji ko ?
A tare suka yi ajiyar zuciya kafin ya cigaba da cewa "Abdallah shine ya bani labarin ƙanwar sa da shirin da take yi na tafiya Maiduguri domin yin aiki dalilin da yasa ya min zancen domin ya ji yaya lafiyar garin yake ? To bayan na ba shi amsar da ta dace shine har ma na ɗan ba shi bayani akan labarin rayuwar ku yadda kuka kasance a matsayin 'yan gudun Hijira har ma ya sake jimantawa to ashe ya faɗawa ita ƙanwar ta shi sai jiya yake shaida min cewar wai na nemawar Madina izni idan har kin amince tana so ta zo yau ta ɗan tattauna da ke kan yadda rayuwa ta kasance muku a Sanadin Boko Haram .
Ya ɗan tsahirta kafin ya ɗora da cigaba da cewa "Wafaa da fatan ban saɓa miki ba da na bada wani ɓangare na labarin ku ba tare da amin....
Da sauri Yakaka ta rufe masa baki da lallausan hannun ta tana girgiza masa kai tace "Habibi kar kace haka ni wallahi baka min laifin kome ba ina maraba da Madina kace ta zo insha Allah za ta iya samun duk wasu bayanai daga bakina daidai gwargawdon yadda rayuwar mu ta kasance .
Sumbatar ta yayi a goshi kafin ya sake ta yana jin yadda take ƙara shiga ransa saboda sanyin halin ta .
Daga nan rakiya ta masa ya tafi cike da kewar juna da suke ji a koyaushe idan zasu yi rabo da juna ko da na awa guda ne .
Bayan ta dawo cikin gidan da ƙwazo irin nata ta gyara gidan tsaf tana yi tana hanzari tana duba waya dan kar lokacin ƙiran ta kula da Ukhtee yayi .
Ta gama ƙarfe tara cif tana zama kuma Falmata ta ƙira ta a skype bayan sun gaisa Falmata tana tsokanar ta Maman biyu sai ta haɗa Su da Ukhtee ita ta shiga lectures.
Da kamar kullum idan za ta shiga lectures da take yi a sati sau uku Ukhtee bata yarda da mai rainon ta ta riƙe ta har Falmata ta gama ihu za tayi ta yi tana kuka .
Sai fa idan an ƙira Yakaka a Skype an haɗa su nan ne kuma babu ruwan ta da Falmata bare wata mai raino za tayi ta damuƙar wayar tana gwalatu da dariya Yakaka na biye mata tana mata wasa har tayi bacci idan ta farka kafin Falmata ta fito Yakaka za'a sake ƙira ta kula da ita ta waya .
Wata irin ƙauna da shaƙuwa ce ta ban mamaki a tsakanin Su biyu yadda Ukhtee ta gane da Falmata da Baban ta haka ta gane da Yakaka haka kuma take son ta .
Sai da ta gama mata wasa ta samu tayi bacci sannan suka yi sallama da mai rainon ta ajiye wayar fuskarta ɗauke da murmushi tana jin ƙarin ƙaunar Ukhtee na bin jikin ta "daga an yaye ki zan je na ɗauko ki takwara koda kuwa Baban ki baya so sai dai yayi haƙuri sa samu wasu bayan ke amma ke kam tawa ce 'yata 'yar gidana.
Ta furta hakan a sarari dai-dai lokacin da aka ƙwanƙwasa ƙofar gidan.
A hankali ta miƙe tana ɗan tura cikin ta gaba da duk cikin watannin sa biyar amma yayi girma sosai "Matar likita ko 'yan tagwaye zata haifa ?
Lokacin da ta buɗe ƙofar sai ta ci karo da wata kyakkyawar mace da zata girme mata da kaɗan a shekaru wacce kallo ɗaya tal za'a mata a hango tarin ilmin Boko da wayewar da suka samun wajen zama na dindin a tare da ita bayan hutu da yake numfasawa a jikin ta .
Daga kan takalman ƙafafun ta marasa tudu har kan ɗan farin gilashin da yake saƙale akan doron siririn karan hancin suna nuni ne da irin tsadaddiyar rayuwar da take yi ta 'ya'yan gata 'ya'yan manya.
"Madina ce .
Yakaka ta aiyana hakan a cikin ran ta kafin ta ɗan sake faɗaɗa fuskar ta da murmushi cikin muryar ta mai sanyin ta ce "sannu da zuwa ki shigo mana .
Da taƙaitatciyar Sallama ta shiga gidan kamar yadda fuskar ta ma ke ɗauke da taƙaitatcen murmushi.
Bayan sun gaisa Yakaka ta kawo mata zoɓo mai sanyi da yake tashin ƙamshin kayan shai irin na mutan Ndjamena da take ƙamshin ya ɗau hankalin Madina '
Bayan sun ɗan taɓa hira lokacin da Madina take shan Zoɓon da daɗin sa yake ratsa ta "bata taɓa zaton irin wannan local juice ɗin yana da daɗi haka ba , ta aiyana hakan a cikin ranta.
Da ta gama sha sai ta fuskanci Yakaka sosai ta sake gabatar da kan ta tare da yi mata godiya da amincewar da tayi ta bata damar tattaunawa da ita .