Sashe 213
Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dan haka suka tsara zasu janye jikin su daga sabgar gidan sosai , sai ranar juma'a da Yamma lis , ana tsakiyar yin sakun lallen Amare tukun suka iso , ba su kaɗai bane ƙungiya suka yi da ɗan yawan su domin baki ɗayan ƙannen Prof matan sai yanzu suka zo tare da wasu daga cikin ya'yan su mata , sauran dangi kuwa mafi yawa sai gobe zasu zo .
kai tsaye iyayen suka yiwa sashin Prof tsinke ba tare da sun bi ta kan jama'ar sauran Jama'ar Amnee ba mutanen N'Djamena da su Malama Maryam wacce ta iso jiya da Yamma .
Suma kuma basu kula su ba , suka cigaba da gudanar da sakun lallen da aka tsara shi cikin irin Al'adun su na mutanen Chad ,
Kota'ina ƙamshin turaren wuta ne ke tashi da ake zuba shi ta kowacce kusurwa na filin wajen , haka Sofiya tare da wasu daga cikin yaran mata 'yan uwansu suka ratsa taro zuwa ainahin inda amaryar take zaune
Abunda ya ɗaure musu kai bai wuce ganin Amaren su biyu ba tare da wacce su sauran basu kai ga sanin ko wacece ba ? ko ita Sofi sai da ta bar yatsine-yatsinen da take yi ta nutsu sosai tukun ta iya shaida Farar balarabiyar da take zaune daga gefen Rahima da aka musu ado iri ɗaya cikin jar lafaya , tundaga kan su har wuya da hannuwa zuwa ƙafafun su adon sarƙoƙi ne masu ruwan gwal irin wanda shuwa arab ke adon bikin su da shi , ( baki ɗayan kayan gudummawa ne daga Hajje Khalsum )
Muƙut ,! Sofiya ta haɗiye busasshen yawun da ya mata saura a baki , kafin ta ɗora da ɗan siririn tsakin da ya bayyana fili .
Da ɗan sauri ta matsa kusa da Hafsa zuciyar ta na ƙara ƙarfin bugun da bata san dalili ba , " kamar nasan wannan kuma Bikin biyu ne wai ? Ta ce tana nuno Yakaka a walaƙance ,
Murmushin yaƙe Hafsa tayi sannan tace " ƙanwar mu ce 'yar Auntien mu Rahima ,
Da sauri ta sake cewa , " Ok daman wannan yarinyar ita ce ƙanwar taku da aka ce an tsinto su ? Kuma bikin ta itan ma ake yi na gan ta anan kusa da Amarya ko duk shisshigi ne da cusa kai ya bawan gado ?
Wata daga cikin ƴar dangin su da ta zo ta jaa hannun Hafsa ɗin tana bata saƙon Amnee na ƙiran ta , ita ta hutatce Hafsa daga bada Amsar da take ƙoƙarin harhaɗowa cike da zullumi .
Zare hannuwanta tayi daga cikin na Sofiya ta bar ta nan a tsaye ,
Ji tayi sam ba zata iya tsayuwa a wajen ba tana kallon Yakaka wacce sai ƙirƙiro ƴar fara'a take a tsakanin ƙawayen Rahima da suka zama kamar nata sai zuwa suke ana yin hoto , tare da yi mata fatan Alheri
Bata sake bi ta kan kowa ba ta zare jiki ta nufi sashin Amnee inda ta tarar ba yawaitar mutane a falon , mutane basu wuce huɗu ba ƙawayen Amnee , kai tsaye ta nufi ɗakin Amnee da take jiyo muryoyin su daga ciki ,
Amnee da Khaalty Rahima haÉ—i da Hajje Khalsum duk shiru suka yi daga tattaunawar da suke suka bita da kallon ganin yadda ta shigo musu É—aki bagatatan babu neman izni .
samun waje tayi ta zauna kafin ta fara gaishe da Amnee , da Æ´ar fara'a Amnee ta amsa , daga haka shiru tayi tana latse-latsen waya bata da niyyar gaishe da sauran mutanen , dan haka fuskar Amnee ta É—an sauya daga fara'ar da take tace ,
" Safiyya baki ga 'yan uwa na bane ? Wannan ƙanwata ce wannan kuma matar wana maza ki gaishe su .
Yanayin ta na bayyana rashin jin daÉ—in yadda Amnee ta disga ta a gaban mutane kamar wacce aka toshewa baki tace " Sannun ku ina wuni ?
Fuskar Khaalty Rahima ɗauke da murmushi sosai ta amsa mata har tana ƙarawa da tambayar ta Mamar ta ?
Bata bata amsa ba ta mayar da kan ta ga fuskar wayar ta ,
Sun cigaba da tattauna yadda wasu al'amuran da suka shafi bikin zasu kasance , kafin su tsinkayo muryar Hajja kori da take ƙwalawa Amnee ƙira tundaga ƙofar falo ,
A kusan tare suka miƙe da sofi wacce ita ma tashin hankalin da ta ji a muryar Mamar ta ya firgita ta ,
Suka fito falon a tare kichiɓus suka yi da tawagar su Hajja kori tare da sauran ƴan uwan su na kurkusa da suka zo tare ,
Kamar zata cukumo Amnee haka ta tsaya a gaban ta tana huci , sannan tace
" Amina baza ki taɓa sauyawa daga mummunar zuciyar ki mai cike da baƙin-hali ba ke da wannan Annamimiyar ƙanwar taki , da daga dawowar ku ke da ita shine kuka haɗa kai kuka maƙalawa ɗan mu auren Shegiyar ƴar da ....
A tsawace Amnee ta katse ta bayan ta matsa baya kaÉ—an tace ,
"Hajja kori ki dakata , ya isa kar ki sake ki ce za ki tozartani ko ki tozartamin 'yar uwa ta , wanda kuka yi a da can ma ya isa wannan masifar taku da bala'in a yanzu bazan ɗauke shi ba domin kuwa kunne ya sake ƙaho ya girma .
aure kuma tsakanin Yakaka da Hamza babu wanda ya isa ya hana ƙulluwar sa muddin ni na tsugunna na haifi Ɗana nayi ɗawainiyar sa sai ya auri Amina Yakaka , idan kuma a wannan karon ma za ku hana ne to Bismillah sai mu gani .
Ƙara matsowa Hajja kori tayi jikinta har tsuma yake tace " tsohuwar kilaki haka kika ce ? Babu shakka dole kice ƙaho ya girma saboda kin gama yawon banzan ki a bariki kin dawo za ki laƙawa....
" Momy kori ki saurara haka nan Dan Allah duk abunda za kiyi kada ki aibata min uwa da mummunan ƙazafi ,
Muryar Doctor Hamza a kausashe ta ratso falon wanda sauƙar sa kenan a garin ya nufo gida yana faka motar sa bai ko gama tsayawa ba Hafsa ta ƙira shi hankalin ta a tashe tana shaida masa rigimar da ƴan uwan Baa suka zo su nayi musu .
Cikin takun sa na nutsuwa ya ƙaraso wajen , yana zuwa ya shiga tsakanin su yana fuskantar Amnee , hannuwan sa duk biyu yasa ya dafa kafaɗun ta , cikin kwantatciyar muryarsa marar amo yace ,
" khaalas Amnee , Dan Allah kar kiyi hayaniya ki bawa kan ki stress kiyi haƙuri kin ji ?
Ganin ta ta sauƙe akan sa idanun ta cike da ƙwallar ɓacin rai , jin irin mummunan ƙazafin da Hajja kori ta yi mata a gaban jama'a , zata yi magana ya katse ta " Kiyi haƙuri Ummii mu je ki huta .
Hajja kori wacce ta ƙulu da yadda ya juya mata ƙeya yana rarrashin uwar sa alhalin ita tudu biyu take ci a wajen sa na babar sa kuma surukar sa , a fusace tace " Kai Hamza ƙaramin marar kunya munafikin maza , tare da kai watau aka haɗa baki aka munafunce mu kana sane , watau kai gaka mai uwa ko ? To ka tabbatar da cewa sai ka zaɓa tsakanin 'yata da wannan koɗaɗɗiyar shegiyar yarinyar da ake shirin aura maka , ƴar da ba'a san asalinta ba .
Bai juyo ba , yace " Momy kori kema kiyi haƙuri Dan Allah .
"Amnee mu tafi É—aki ki huta , yace yana juya kafaÉ—un ta suka fara taku ,
" Doctor ,
Chak ya tsaya lokacin da sautin muryar Sofiya ya doki kunnuwan sa ,da sassarfa kamar ana tunkuɗa ta ta ƙaraso ta zagayo ta gaban su , idon ta da suka firfito da ke bayyana tsantsar firgicin da zuciyar ta take ciki ta tsattsare sa da su , cikin wata irin murya tace
" Da gaske za ka ƙara aure ? Kai ne za ka auri yarinyar nan Yakaka ? kuma wai gobe ne auren naku ?
Ganin sa ya kai kan Amnee da take raba ganin ta a tsakanin su , fuskar ta na bayyana ciwon da ran ta ke ciki, muryar sa can ƙasa yace
" Gaskiya ne Amma ki bar maganar nan daga baya zamu yi .
Kewaye ta yayi suka wuce cikin ɗaki , Ukhtee Rahima da take tsaye daga bakin ƙofar ɗakin idanun ta cike da ƙwallar tuno da wata rana mai kama da wannan a cikin wannan falon lamari mai muni ya haka ya faru ta silar dangin Prof da sanadin haka ne rayuwar su ita da 'ya'yan da ta haifa suka faɗa a garari , sai ga shi a yau tarihi yana sake maimaita kan sa sun kuma gwada hakan akan 'yar ta, daga ƙasan ranta take tambayar kanta wai laifin me ta musu ne da suka tsane ta , tsana mai muni ya haka ? Juyawa tayi ta rufa musu baya suka rufo ƙofar .
Wani irin zaman 'yan dabaro Sofiya tayi a ƙasa dirshan kafin ta ƙwala wani irin ihun da yasa Rahima da Yakaka hanzarin ƙarasa shigowa falon da suke daf da ƙarasowa daman .
" Ƙarya ne , inaa no no wallahi ƙarya ne , Doctor baka isa ka min haka ba , Momy kice mafarki nake dan Allah ?
Ta ƙarasa sambatun da take tana miƙawa Momy kori hannu daga inda take kamar 'yar yayen da take son uwar ta ta ɗauke ta,
A fusace Momy kori ta ƙaraso wajen , ta fara jaan hannun ta tana ƙoƙarin ɗaga ta , bakin ta har kumfa yake lokacin da take cewa ,
" sai ki tashi mu tafi ai shugabar 'yan taurin kai marar zuciya , tun farko ai na faɗa miki akwai ranar ƙin dillaci muddin kika yadda kika auri ɗan wannan Annamimiyar matar , amma da yake kafiya ce da ke kika nace kika liƙe masa kika ƙi kowa kika zauna zaman jiransa shekara da shekaru .
kai tsaye iyayen suka yiwa sashin Prof tsinke ba tare da sun bi ta kan jama'ar sauran Jama'ar Amnee ba mutanen N'Djamena da su Malama Maryam wacce ta iso jiya da Yamma .
Suma kuma basu kula su ba , suka cigaba da gudanar da sakun lallen da aka tsara shi cikin irin Al'adun su na mutanen Chad ,
Kota'ina ƙamshin turaren wuta ne ke tashi da ake zuba shi ta kowacce kusurwa na filin wajen , haka Sofiya tare da wasu daga cikin yaran mata 'yan uwansu suka ratsa taro zuwa ainahin inda amaryar take zaune
Abunda ya ɗaure musu kai bai wuce ganin Amaren su biyu ba tare da wacce su sauran basu kai ga sanin ko wacece ba ? ko ita Sofi sai da ta bar yatsine-yatsinen da take yi ta nutsu sosai tukun ta iya shaida Farar balarabiyar da take zaune daga gefen Rahima da aka musu ado iri ɗaya cikin jar lafaya , tundaga kan su har wuya da hannuwa zuwa ƙafafun su adon sarƙoƙi ne masu ruwan gwal irin wanda shuwa arab ke adon bikin su da shi , ( baki ɗayan kayan gudummawa ne daga Hajje Khalsum )
Muƙut ,! Sofiya ta haɗiye busasshen yawun da ya mata saura a baki , kafin ta ɗora da ɗan siririn tsakin da ya bayyana fili .
Da ɗan sauri ta matsa kusa da Hafsa zuciyar ta na ƙara ƙarfin bugun da bata san dalili ba , " kamar nasan wannan kuma Bikin biyu ne wai ? Ta ce tana nuno Yakaka a walaƙance ,
Murmushin yaƙe Hafsa tayi sannan tace " ƙanwar mu ce 'yar Auntien mu Rahima ,
Da sauri ta sake cewa , " Ok daman wannan yarinyar ita ce ƙanwar taku da aka ce an tsinto su ? Kuma bikin ta itan ma ake yi na gan ta anan kusa da Amarya ko duk shisshigi ne da cusa kai ya bawan gado ?
Wata daga cikin ƴar dangin su da ta zo ta jaa hannun Hafsa ɗin tana bata saƙon Amnee na ƙiran ta , ita ta hutatce Hafsa daga bada Amsar da take ƙoƙarin harhaɗowa cike da zullumi .
Zare hannuwanta tayi daga cikin na Sofiya ta bar ta nan a tsaye ,
Ji tayi sam ba zata iya tsayuwa a wajen ba tana kallon Yakaka wacce sai ƙirƙiro ƴar fara'a take a tsakanin ƙawayen Rahima da suka zama kamar nata sai zuwa suke ana yin hoto , tare da yi mata fatan Alheri
Bata sake bi ta kan kowa ba ta zare jiki ta nufi sashin Amnee inda ta tarar ba yawaitar mutane a falon , mutane basu wuce huɗu ba ƙawayen Amnee , kai tsaye ta nufi ɗakin Amnee da take jiyo muryoyin su daga ciki ,
Amnee da Khaalty Rahima haÉ—i da Hajje Khalsum duk shiru suka yi daga tattaunawar da suke suka bita da kallon ganin yadda ta shigo musu É—aki bagatatan babu neman izni .
samun waje tayi ta zauna kafin ta fara gaishe da Amnee , da Æ´ar fara'a Amnee ta amsa , daga haka shiru tayi tana latse-latsen waya bata da niyyar gaishe da sauran mutanen , dan haka fuskar Amnee ta É—an sauya daga fara'ar da take tace ,
" Safiyya baki ga 'yan uwa na bane ? Wannan ƙanwata ce wannan kuma matar wana maza ki gaishe su .
Yanayin ta na bayyana rashin jin daÉ—in yadda Amnee ta disga ta a gaban mutane kamar wacce aka toshewa baki tace " Sannun ku ina wuni ?
Fuskar Khaalty Rahima ɗauke da murmushi sosai ta amsa mata har tana ƙarawa da tambayar ta Mamar ta ?
Bata bata amsa ba ta mayar da kan ta ga fuskar wayar ta ,
Sun cigaba da tattauna yadda wasu al'amuran da suka shafi bikin zasu kasance , kafin su tsinkayo muryar Hajja kori da take ƙwalawa Amnee ƙira tundaga ƙofar falo ,
A kusan tare suka miƙe da sofi wacce ita ma tashin hankalin da ta ji a muryar Mamar ta ya firgita ta ,
Suka fito falon a tare kichiɓus suka yi da tawagar su Hajja kori tare da sauran ƴan uwan su na kurkusa da suka zo tare ,
Kamar zata cukumo Amnee haka ta tsaya a gaban ta tana huci , sannan tace
" Amina baza ki taɓa sauyawa daga mummunar zuciyar ki mai cike da baƙin-hali ba ke da wannan Annamimiyar ƙanwar taki , da daga dawowar ku ke da ita shine kuka haɗa kai kuka maƙalawa ɗan mu auren Shegiyar ƴar da ....
A tsawace Amnee ta katse ta bayan ta matsa baya kaÉ—an tace ,
"Hajja kori ki dakata , ya isa kar ki sake ki ce za ki tozartani ko ki tozartamin 'yar uwa ta , wanda kuka yi a da can ma ya isa wannan masifar taku da bala'in a yanzu bazan ɗauke shi ba domin kuwa kunne ya sake ƙaho ya girma .
aure kuma tsakanin Yakaka da Hamza babu wanda ya isa ya hana ƙulluwar sa muddin ni na tsugunna na haifi Ɗana nayi ɗawainiyar sa sai ya auri Amina Yakaka , idan kuma a wannan karon ma za ku hana ne to Bismillah sai mu gani .
Ƙara matsowa Hajja kori tayi jikinta har tsuma yake tace " tsohuwar kilaki haka kika ce ? Babu shakka dole kice ƙaho ya girma saboda kin gama yawon banzan ki a bariki kin dawo za ki laƙawa....
" Momy kori ki saurara haka nan Dan Allah duk abunda za kiyi kada ki aibata min uwa da mummunan ƙazafi ,
Muryar Doctor Hamza a kausashe ta ratso falon wanda sauƙar sa kenan a garin ya nufo gida yana faka motar sa bai ko gama tsayawa ba Hafsa ta ƙira shi hankalin ta a tashe tana shaida masa rigimar da ƴan uwan Baa suka zo su nayi musu .
Cikin takun sa na nutsuwa ya ƙaraso wajen , yana zuwa ya shiga tsakanin su yana fuskantar Amnee , hannuwan sa duk biyu yasa ya dafa kafaɗun ta , cikin kwantatciyar muryarsa marar amo yace ,
" khaalas Amnee , Dan Allah kar kiyi hayaniya ki bawa kan ki stress kiyi haƙuri kin ji ?
Ganin ta ta sauƙe akan sa idanun ta cike da ƙwallar ɓacin rai , jin irin mummunan ƙazafin da Hajja kori ta yi mata a gaban jama'a , zata yi magana ya katse ta " Kiyi haƙuri Ummii mu je ki huta .
Hajja kori wacce ta ƙulu da yadda ya juya mata ƙeya yana rarrashin uwar sa alhalin ita tudu biyu take ci a wajen sa na babar sa kuma surukar sa , a fusace tace " Kai Hamza ƙaramin marar kunya munafikin maza , tare da kai watau aka haɗa baki aka munafunce mu kana sane , watau kai gaka mai uwa ko ? To ka tabbatar da cewa sai ka zaɓa tsakanin 'yata da wannan koɗaɗɗiyar shegiyar yarinyar da ake shirin aura maka , ƴar da ba'a san asalinta ba .
Bai juyo ba , yace " Momy kori kema kiyi haƙuri Dan Allah .
"Amnee mu tafi É—aki ki huta , yace yana juya kafaÉ—un ta suka fara taku ,
" Doctor ,
Chak ya tsaya lokacin da sautin muryar Sofiya ya doki kunnuwan sa ,da sassarfa kamar ana tunkuɗa ta ta ƙaraso ta zagayo ta gaban su , idon ta da suka firfito da ke bayyana tsantsar firgicin da zuciyar ta take ciki ta tsattsare sa da su , cikin wata irin murya tace
" Da gaske za ka ƙara aure ? Kai ne za ka auri yarinyar nan Yakaka ? kuma wai gobe ne auren naku ?
Ganin sa ya kai kan Amnee da take raba ganin ta a tsakanin su , fuskar ta na bayyana ciwon da ran ta ke ciki, muryar sa can ƙasa yace
" Gaskiya ne Amma ki bar maganar nan daga baya zamu yi .
Kewaye ta yayi suka wuce cikin ɗaki , Ukhtee Rahima da take tsaye daga bakin ƙofar ɗakin idanun ta cike da ƙwallar tuno da wata rana mai kama da wannan a cikin wannan falon lamari mai muni ya haka ya faru ta silar dangin Prof da sanadin haka ne rayuwar su ita da 'ya'yan da ta haifa suka faɗa a garari , sai ga shi a yau tarihi yana sake maimaita kan sa sun kuma gwada hakan akan 'yar ta, daga ƙasan ranta take tambayar kanta wai laifin me ta musu ne da suka tsane ta , tsana mai muni ya haka ? Juyawa tayi ta rufa musu baya suka rufo ƙofar .
Wani irin zaman 'yan dabaro Sofiya tayi a ƙasa dirshan kafin ta ƙwala wani irin ihun da yasa Rahima da Yakaka hanzarin ƙarasa shigowa falon da suke daf da ƙarasowa daman .
" Ƙarya ne , inaa no no wallahi ƙarya ne , Doctor baka isa ka min haka ba , Momy kice mafarki nake dan Allah ?
Ta ƙarasa sambatun da take tana miƙawa Momy kori hannu daga inda take kamar 'yar yayen da take son uwar ta ta ɗauke ta,
A fusace Momy kori ta ƙaraso wajen , ta fara jaan hannun ta tana ƙoƙarin ɗaga ta , bakin ta har kumfa yake lokacin da take cewa ,
" sai ki tashi mu tafi ai shugabar 'yan taurin kai marar zuciya , tun farko ai na faɗa miki akwai ranar ƙin dillaci muddin kika yadda kika auri ɗan wannan Annamimiyar matar , amma da yake kafiya ce da ke kika nace kika liƙe masa kika ƙi kowa kika zauna zaman jiransa shekara da shekaru .