← Book details Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 210 OF 269

Sashe 210

Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Dumm Yakaka tayi , zuciyar ta na sauya bugu , a lokacin ba wanda ya faɗo mata sai wannan mutumin da yayi ta nacin bibiyar ta shekaru kusan biyu tana zille masa a abuja , kafin barinta Abuja dai Lubna tace ta ba shi number ta Amma ko sau ɗaya bata taɓa riskar ƙiran sa ba , wataƙila daman wasa yake , ita kuwa bayan shi ai ba wanda ta taɓa saurara mafi yawan masu cewa suna son ta duk gani take fasiƙanci zasu yi da ita , domin tunda tasan illar zina da zunubin ta take jin tsoron maza ma gaba ɗaya .

Tunanin ta ya katse lokacin da taji Amnee na maimaita mata tambayar , a hankali ta girgiza kai , " Babu kowa Amnee ,
    " kin tabbata ?  Ki fa faɗa min idan akwai ,
  Amnee ta sake furta haka domin haƙaƙewa ,
   Zuciyar Yakaka ta fara shiga ruɗu da son sanin dalilin da ya kawo wannan maganar ta sake cewa , " Allah babu kowa Amnee ,
  " To Alhamdulillah , Aminatu kina jina ko ?
  Bata jira ta amsa ba ta cigaba da cewa , " Baa Alaji , Baban ku na gidan nan ya yanke shawarar haɗa aure a tsakanin ku ke da Yayan ku Hamza , muna fatan ba za ki bijirewa Umarnin mu ba ?

  A razane ta ɗago kan ta saboda yadda zancen ya zo mata baga-tatan , ta shiga raba ganin ta tsakanin Mamar su da Amnee cikin wani irin jirkitatcen yanayi ,

Ganin yadda fuskar ta ta nuna yasa Khaalty Rahima hanzarin tare ko wanne irin sakamakon da zai biyo baya ta hanyar cewa ,
   " kuma har an riga an gama yanke magana za'a haɗa bikin ku rana guda da na takwarata nan da kwanaki goma sha biyu , babu sauran wata magana .

Ihun da Rahima ta sa tana tsalle ta taho ta rungume Yakaka  shi ya katse zancen khaalty Rahima ,
   " Alhamdulillah burin Big bro zai cika , Masha Allah Baa mun gode sosai wallahi , sai ta sake ta da gudu tana barin ɗakin tana cewa , " bari naje na taya bro murna wayyo Allah ,

   Shiru ne ya ratsa ɗakin sai tashin sautin murmushin Falmata da farin-ciki mai tsanani ya bayyana kan sa a fuskar ta ,

" Takwara baki ce kome ba ? , Amnee ta sake katse shirun ,

A hankali Yakaka ta É—ago kan ta ta É—an dubi Amnee muryar ta can ciki tace , " Shi ya yarda ?
  Tambayar da ta karya zuciyar iyayen nata biyu har ma da Falmata , kafin Amnee ta amsa ta sake cewa , " Idan har shi ya yadda shikenan Amnee ni ai koyaushe mai muku biyayya ce Baa kuma nima Babana ne , nagode da duk abunda kuka min .

Hannuwanta duk biyu Amnee ta sanya ta É—ago ta , ta zarce da rungumeta a jikinta ,
  " Allah ya miki Albarka takwarata Allah ya baku 'ya'yan da zasu muku fiye da irin biyayyar da kuka yi mana ,

Addu'o'i ta cigaba da yi mata Falmata na amsawa da Æ´ar muryar ta dake bayyana amon murna ,

Miƙewa Amnee tayi tare da cewa ," bari naje na sake sabunta tsari da shiri bikin ya zama biyu , kai wannan shekarar ta zo min da ɗinbin Alheru Alhamdulillah Allah nagode ma ,

Bata jira cewar su ba ta fita ta bar su , su ukun ,
   Yakaka ta ɗago idanunta dake cike da ƙwalla damuwa ɓaro-ɓaro a fuskar ta take kallon fuskar Mamar su tana son ko yaya ta bata damar da zata ce wani abu ,

A hankali Khaalty Rahima ta tako ta zauna a inda Amnee ta tashi , bata yadda sun haɗa ido ba tace " Naji daɗi da kika nuna halacci baki yi butulci ba , abu na gaba shine ki ɗauko haƙuri da juriya akan duk wani ƙalubale da za ki fuskanta a gaba ki riƙe su a matsayin makamin ki , sannan a ko'ina kika tsinci kan ki cikin kowanne hali ki ji tsoron Allah , Allah ya miki Albarka Amina .
   " Amin,  Yakaka ta amsa hawayen idanun ta na sauƙa bisa ƙuncin ta ,

Miƙewa khaalty Rahima tayi saboda zuciyar ta ba zata juri ganin irin wannan damuwar mai tarin yawa da take hangowa daga Yakaka ba , abunda ta riga ta sani inshaAllah cikin auren nan nasu akwai alheri mai tarin yawa ,

Tasan abunda Yakaka take tsoro bai wuce illar dake tare da ita ba akan irin abunda ta aikata , ita ta ɗau hakan a matsayin kaddarar Yakaka, kuma inshaAllah a wannan gaɓar ta ƙudurci aniyar yakice kunya irin wacce iyaye mata ke nunawa ƴaƴan su , zata ɗauri ɗamarar gyara ɗiyar ta ciki da bai tare da mata darussa masu inganci cikin ɗan zaman da ya rage musu tare , da zai taimaka wajen sauƙaƙa mata duk wasu ƙalubalen da ka iya taso mata a gidan aure .

Kayan gyara kuwa daga nan har N'Djamena, zata ɗau hanya ta tafi domin ta ga ta yiwa ƴar ta gyara mai kyau da zai taimaka ko kaɗan ne wajen samar mata da ɗan matsayi ko yaya a wajen Mijinta, sanin da tayi tana da abokiyar zama ko kusa ba zata so ƴar ta ta walaƙanta ba . ( Khaalty Rahima nima ina da saƙo zuwa N'Djamena nan amma ni turaren wuta nake so 🙄🤐 )

Tana bada baya daga ɗakin Falmata ta taso da sassarfa ta isa inda Yakaka take zaune kamar an dasa ta ko motsin kirki bata yi , tana zuwa ta rungume ta tana ƴar dariya-dariya tace , " Yakaka na Alhamdulillah , kin ga Al'amarin Allah ko ? Allah baya bacci Yakaka nayi murna , nayi murna , a kunne ta ta raɗa mata ,"Félicitations Mme Hamza Mustapha Dilmari,

Kukan da tun-tuni ke cin Yakaka a rai shi ta saki lokacin da tashin hankali yayi nasarar lillisa zuciyar ta , " Aure ? Aure tsakanin ta da Doctor hamza mutumin da ya tsani kallon ko fuskar ta ?  mutumin da yake zargin ta da tafiya yawon banza ? Mijin sofi ƙawar samy Baby ? Anya Mamaa ba zasu kaita inda za'a kashe ta bane tun kwananta bai ƙare ba , a gareta wannan ba gata bane ba .

****

Duk yadda Rahima ta dunga ƙwanƙwasa ƙofar falon Doctor Hamza bai taso ya buɗe ba duk kuwa da cewa yana zaune dirshan a ƙasa a falon sai dai damuwar da yake ciki ta toshe masa kunne daga jin hayaniyar Rahima , ya zurfafa cikin tunani .

  Wani irin yanayi marar daɗi ya tsinci kansa a ciki , ko kusa da yasan abunda zai riska kenan a garin da bai zo ba ,

Yarinyar da ta gama yawon banzan ta bai sani ba ma ko ta maƙalo wata cutar ita ce dan kawai Baa yana son gyara wani shuɗaɗɗan kuskure sai ya laƙa masa auren ta ?

Wannan da bata ajiye kome ba sai tarin ƙarairayi da yaudarar banza , har ita ce ake so ya gatata ? To wanne gata zai mata da bai nuna mata sumfurin sa ba a baya ?

Shi ya sani a da ya so ta amma yanzu ko alama baya jin ɗigo na son ta sai ma baƙin-ciki da yake ji a duk lokacin da ya gan ta .

Babu yadda zai yi , bashi da wata mafita shiyasa ya amsa auren ta da aka liƙa masa , da ace ba Khaalty Rahima bace uwar ta da Wallahi da ko ta halin ƙaka sai ya cisge wannan liƙin da ake son yi masa ,

To amma kasancewar ta 'ya ga Khaalty Rahima ya sa dole ya amince , zai aure ta , su zauna a yadda yanayi ya zo musu shi da ita ..!

Assalamu Alaikum masu karatu

Da fatan kun wuni lafiya ? Ina miƙo saƙon gaisuwa tare da fatan alheri agare ku baki ɗaya .

To ga fa abun yazo , wai inji mai tsoron wanka , Ina nufin bikin Yakaka da Hamza 😂
sister J , da Raly Garba , ku ne fa masu rabon anko , sai dai kuma ga lokaci ya zo a ƙure kwana goma sha biyu kachal ai ya muku kaɗan. 🤔

  
  
[1/4, 12:40 PM] +234 816 886 5113: MAFARI
( HARGITSIN RAYUWA )

UMM'MUAZ

48

MAFI TSAWON DA BAI ZAMA KARSHE BA.

A washegarin ranar da aka tabbatar masa da haɗin Auren sa da Yakaka nan da kwanaki goma sha ɗaya masu zuwa , Doctor Hamza ya tattara ya nasa ya nasa ya koma Abuja da sassafe , duk yadda Amnee ta dunga son shigo masa da zancen Yakaka tana son ta haɗa su , lokacin da ya shiga yi musu sallama ita da Baa , ƙi yayi , ko Khaalty Rahima sai ta wajen Amnee ya bar mata saƙon tafiyar sa .

Gaba É—aya baya cikin nutsuwar sa garin ya masa wani irin zafi .
Chapter 210 · 0% Book details