Sashe 212
Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Domin a yanzu ma kasa sanar da ita labarin ƙarin auren sa yayi , maimakon haka kawai sai ya ɓige da neman samun nutsuwar gangar jikin sa ya shiga shinshinata yana gwada mata soyayya irin wacce ita dai tunda take da shi bai taɓa yi mata makamancin haka ba , zuciyar ta ta ji ta kunburo tana daɗa tunbatsa da ƙaunar sa , gefe guda kuma wani irin tsantsar farin-ciki take ciki , "yau Doctor ne yake nuna mata zallar so tare da kalamai masu tausasa zuciyar masoyi ? Babu shakka masu iya magana suna cewa daɗewa a mabauta ma ƴanci ce ."
Shi kuwa a ɓangaren sa zuwa washegari ya tabbatar dai ba zai fa iya sanar da ita ba , sai ya kuɗurce zai tura ta can Maiduguri da wuri , su da suka rakito auren sa san yadda zasu yi su sanar da ita domin shi Allah ya sani ba zai iya ƙarawa kansa damuwar haukar da sofiya zata iya yi ba akan ta shi damuwar da yake ciki , gara tayi haukar ta acan idan yaso ma ta huce akan ita Yakaka , shi duk wannan ba damuwar sa bace tsuntsun da ya jaa ruwa .
Saɓanin yadda ya zaci damuwar sa zata zama ƙanƙanuwa sai lamarin ya zarce tunanin sa domin tunda aka yi batun auren su kullum tsaffin laifukan ta daɗa sabunta kan su suke a zuciyar sa , baki ɗaya sai ya susuce kamar farkon lamarin .
Ya zama ko office ya tafi baya wani taɓuka aikin kirki , har waɗanda ke tare da shi suka fara fahimta , Suleiman Amininsa shine ya fara farga da yawan damuwar da yake ciki ya kuma matsa masa da tambaya ? a farko Doctor Hamza ba shi da niyyar sanar da Suleiman da kan sa , sai ko bayan auren , sai dai yadda ya matsa masa da tambaya yana nuna damuwar sa a fili ya sa shi sanar da shi cewa "aure zai ƙara da ƴar Innar sa da aka ba shi , "
Wani sasakai Doctor suleiman yayi yana kallon Hamza , kafin ya wani kwashe da dariya , sai da yayi dariyar ta ishe shi , Doctor Hamza bai ce masa ƙala ba illa ma rubuce-rubucen sa da ya shiga yi , yana jin yadda ransa ke ɓaci da dariyar walaƙanci da suleiman ya sanya shi a gaba yana yi .
" Ka ce dai alƙadarin Safiya ya karye , zaka yi wani yunƙuri dan ganin ka fara tara naka zuri'ar , lamari yayi kyau haka ake son Namiji to amma nayi mamaki ina kuma kan yi ko yaya zaka yi da mata biyu ?
Da wutsiyar ido Doctor hamza ya dube shi , ba tare da ya bar abunda yake yi ba yace ,
" Su masu mata biyun me suke yi da na su ?
Wata dariyar Doctor Suleiman ya sake kwashewa da ita kafin ya É—ora da cewa ,
" wataƙila jera su suke suna ado da su a gidajen su , ya ɗora da cewa watanni nawa aka sa lokacin bikin ? Banda abunka abokina to menene abun damuwa ? Ai hurhuɗu ya kamata ma mu ajiye , domin ko nima ba domin tafiyar nan da na ɗan yi ba da yanzu batun auren mu yayi nisa da Aminah ta , wataƙila ma sai dai mu haɗa ayi rana ɗaya tunda kuwa ita ma ƴar Maidugurin ce , wata nawa aka sa ?
Muryar Doctor Hamza can ƙasa yace , " kwanaki goma kachal suka rage har da yau da muke ciki ,
Tsumu Doctor Suleiman yayi yana kallon sa wannan karon kamar bai yadda da abunda yace ba , ganin haka yasa Doctor Hamza cigaba da cewa ,
" tare za'a haɗa da na ƙanwata Rahima , saboda ayi a huta , tarewar kuma sai yadda hali ya min wataƙila ta kai watanni huɗu a maidugurin ko ma fiye da haka kasan dai kome daki-daki ake yin sa .
Da fara'a sosai a fuskar sa Doctor Suleiman ya shiga taya shi murna yana taya sa shi da fatan alheri cikin raha ya É—ora da tsokanar sa ,
" kace ciwon so kake ciki mana tare da kewa , shiyasa duk ka wani zama haka , babu shakka wannan ƙanwar tamu mai sa'a ce , to sabon shiri kenan zamu fara dan angwanci ya same mu da rana tsaka ba tare da mun shirya ba , amma duk da haka ma ɗan yi wasu tsare-tsare a gurguje me da me za'a yi na biki ?
Kallo mai kama da harara Doctor Hamza ya masa , kafin yace
" Dan Allah zan roƙe ka Alfarma Suleiman, kar ka ƙara min damuwa , duk garin nan bayan kai ba wanda na faɗawa zancen nan , ko ita sofiya bata san da zancen ba dan haka ka ma bar maganar wani biki zancen ya tsaya kawai a tsakanin mu , bayan kai da daman zaka je bikin Rahima babu wanda zan gayyata .
Da wani irin yanayi Suleiman ya dube shi kafin yace " ko meyasa ?
" kawai ra'ayina ne , mu ba yara bane da za'a yi wani raye-rayen biki ina ma muka ga lokutan ɓatawa ?.
GÆ´aÉ—a kai Suleiman yayi cike da shakku yace " to shikenan tunda kace haka Allah ya kyauta .
" Amin nagode abokina , Doctor Hamza ya amsa masa , domin ya sauƙaƙa yanayin rashin daɗi da ya hango a tare da Suleiman sai yace , " ina aka kwana kan batun lamarin ita Aminar taka ? ko idan muka je Maidugurin za'a yi wani motsi mai ƙarfi ne ? kasan fa kun jima da yarinyar nan ya ci ace anyi auren nan .
Cike da zaƙuwar jin an masa susa inda ke mar ƙaiƙayi Doctor Suleiman yace ," bari kawai abokina wannan yarinyar ko yau aka kawota gidana ta walashe ni , gyara zancen nan ka ma , saboda ai ni na jima ina son ta ba wai mun jima a tare ba , domin kuwa ai ita har yau bata wani bani dama ba , ni kaɗai ke fama ,
Ya dubi fuskar Doctor hamza da yayi kasaƙe cike da takaicin yadda ya zauna gotai-gotai da shi 'yar yarinya ƙanƙanuwa na masa yawo da hankali wajen shekaru uku , sai kace ƴa gwal ?
Doctor Suleiman ya katse zancen da Doctor Hamza yake son ɗorawa ta hanyar cigaba da cewa , " kar ka ga laifina Abokina , Amina ta cancani da kowanne ɗa Namiji yayi sha'awar ajiye mace mai nagartartun halaye da Addini haɗi da nutsuwa irin ta , wallahi ko kai da kan ka idan na baka labarin irin rayuwar da yarinyar take yi mai cike da tsantsanin kiyaye kan ta duk kuwa da cewa inda take rayuwa ƙazamtatce ne , halayyanta na ƙwarai nake kwaɗayi ba kome ba , saboda na sha gwada ta ba sau ɗaya ba , na kuma sa mutane wasu daban ma sun gwada ta amma ko sau ɗaya ban taɓa kamata da wani laifi saɓanin zahirin ta da take bayyane kullum cikin kamala da nutsuwa ba .
a yadda kake ƙyamatar halayen wasu matan nasan zaka yi mamakin nagartar da ita take da shi , kuma zaka bada goyan baya ɗari bisa ɗari akan na auro ta , musamman idan ka ji irin hali na tausayawa da suka riski kan su a ciki ita da ƴar uwar ta ,
Cike da gajiya da yadda ya zauna yana yabon wata wacce har yau shi da kan sa bata bashi darajar da za ta saurare shi ba , bare kuma su abokan sa Doctor Hamza yace " to Allah ya tabbatar da Alheri abokina .
Kamar yadda suka yi alƙawari ana saura kwanaki biyar ɗaurin Aure Mutanen N'Djamena suka iso ,sun tasamma mutane ishirin da ɗoriya , domin sun kusan cika falon Prof da anan suka fara ssuƙa , bayan an gaisa murnar sake ganin juna ta kachame a tsakanin su har da 'yan koke-koke , banda yaren su na larabaccin Chad babu abunda ke tashi a wajen ,
Zainab , Hafsa da suka iso tun jiya , har Rahima haÉ—i da Yakaka da Falmata , a tsakanin su duk babu wani mai jin yaren har sosai , dan haka sai suka tsaya kallon su fuskokin su É—auke da murmushi ,
Bayan sun ɗan nutsu sun sha ruwa da lemu , sai Matan suka shiga ciki inda za'a musu masauƙi ,
Mazan kuma suka tsaya anan Sashin Prof .
A ciki Amnee ta sake gabatar da Yakaka da Falmata , nan aka fara rungumar su ana sumbatar kumatun su da goshi , cike da nuna zallar ƙauna , daga baya kuma aka sake sabuwar gaisuwa har da su Hafsa da mafi yawa sun riga sun san su , su Yakaka ne baƙi .
Ba'a kwana ba Hajje Nadiya tare da tawagar ta mata huɗu da ta taho da su domin su taya ta suka buƙaci da su fara aikin da ya kawo su na gyaran Amare .
Tun ana saura kwanaki biyu ɗaurin Aure Sofiya ta iso Maiduguri , amma sai ta ƙi ƙarasawa gidan su Doctor Hamza tayi zaman ta a gidan su tare da Mamar ta Hajja kori , da ita ta zuga ta tace tayi zaman ta sai ana gobe ɗaurin auren da Yamma sai su tafi tare , ba dan kome ba kuwa sai dan rashin shirin da yake tsakanin su da Amnee da Khaalty Rahima .
Da ko kusa basu so Auren Amnee da yayan su ya sake ƙulluwa ba , kuma duk yadda suka so hana tabbatuwar lamarin fir Prof yaƙi saurarar su , ita kanta zuwan ta wajen sa biyu da zummar yi masa famfo amma bata samun fuska dan haka ta haƙura .
Babu abunda yafi ƙara basu haushi irin dawowar Khaalty Rahima da suka fi tsana gidan wannan karon har ma da marayun 'ya'yan ta kamar yadda labari ya iske su
Shi kuwa a ɓangaren sa zuwa washegari ya tabbatar dai ba zai fa iya sanar da ita ba , sai ya kuɗurce zai tura ta can Maiduguri da wuri , su da suka rakito auren sa san yadda zasu yi su sanar da ita domin shi Allah ya sani ba zai iya ƙarawa kansa damuwar haukar da sofiya zata iya yi ba akan ta shi damuwar da yake ciki , gara tayi haukar ta acan idan yaso ma ta huce akan ita Yakaka , shi duk wannan ba damuwar sa bace tsuntsun da ya jaa ruwa .
Saɓanin yadda ya zaci damuwar sa zata zama ƙanƙanuwa sai lamarin ya zarce tunanin sa domin tunda aka yi batun auren su kullum tsaffin laifukan ta daɗa sabunta kan su suke a zuciyar sa , baki ɗaya sai ya susuce kamar farkon lamarin .
Ya zama ko office ya tafi baya wani taɓuka aikin kirki , har waɗanda ke tare da shi suka fara fahimta , Suleiman Amininsa shine ya fara farga da yawan damuwar da yake ciki ya kuma matsa masa da tambaya ? a farko Doctor Hamza ba shi da niyyar sanar da Suleiman da kan sa , sai ko bayan auren , sai dai yadda ya matsa masa da tambaya yana nuna damuwar sa a fili ya sa shi sanar da shi cewa "aure zai ƙara da ƴar Innar sa da aka ba shi , "
Wani sasakai Doctor suleiman yayi yana kallon Hamza , kafin ya wani kwashe da dariya , sai da yayi dariyar ta ishe shi , Doctor Hamza bai ce masa ƙala ba illa ma rubuce-rubucen sa da ya shiga yi , yana jin yadda ransa ke ɓaci da dariyar walaƙanci da suleiman ya sanya shi a gaba yana yi .
" Ka ce dai alƙadarin Safiya ya karye , zaka yi wani yunƙuri dan ganin ka fara tara naka zuri'ar , lamari yayi kyau haka ake son Namiji to amma nayi mamaki ina kuma kan yi ko yaya zaka yi da mata biyu ?
Da wutsiyar ido Doctor hamza ya dube shi , ba tare da ya bar abunda yake yi ba yace ,
" Su masu mata biyun me suke yi da na su ?
Wata dariyar Doctor Suleiman ya sake kwashewa da ita kafin ya É—ora da cewa ,
" wataƙila jera su suke suna ado da su a gidajen su , ya ɗora da cewa watanni nawa aka sa lokacin bikin ? Banda abunka abokina to menene abun damuwa ? Ai hurhuɗu ya kamata ma mu ajiye , domin ko nima ba domin tafiyar nan da na ɗan yi ba da yanzu batun auren mu yayi nisa da Aminah ta , wataƙila ma sai dai mu haɗa ayi rana ɗaya tunda kuwa ita ma ƴar Maidugurin ce , wata nawa aka sa ?
Muryar Doctor Hamza can ƙasa yace , " kwanaki goma kachal suka rage har da yau da muke ciki ,
Tsumu Doctor Suleiman yayi yana kallon sa wannan karon kamar bai yadda da abunda yace ba , ganin haka yasa Doctor Hamza cigaba da cewa ,
" tare za'a haɗa da na ƙanwata Rahima , saboda ayi a huta , tarewar kuma sai yadda hali ya min wataƙila ta kai watanni huɗu a maidugurin ko ma fiye da haka kasan dai kome daki-daki ake yin sa .
Da fara'a sosai a fuskar sa Doctor Suleiman ya shiga taya shi murna yana taya sa shi da fatan alheri cikin raha ya É—ora da tsokanar sa ,
" kace ciwon so kake ciki mana tare da kewa , shiyasa duk ka wani zama haka , babu shakka wannan ƙanwar tamu mai sa'a ce , to sabon shiri kenan zamu fara dan angwanci ya same mu da rana tsaka ba tare da mun shirya ba , amma duk da haka ma ɗan yi wasu tsare-tsare a gurguje me da me za'a yi na biki ?
Kallo mai kama da harara Doctor Hamza ya masa , kafin yace
" Dan Allah zan roƙe ka Alfarma Suleiman, kar ka ƙara min damuwa , duk garin nan bayan kai ba wanda na faɗawa zancen nan , ko ita sofiya bata san da zancen ba dan haka ka ma bar maganar wani biki zancen ya tsaya kawai a tsakanin mu , bayan kai da daman zaka je bikin Rahima babu wanda zan gayyata .
Da wani irin yanayi Suleiman ya dube shi kafin yace " ko meyasa ?
" kawai ra'ayina ne , mu ba yara bane da za'a yi wani raye-rayen biki ina ma muka ga lokutan ɓatawa ?.
GÆ´aÉ—a kai Suleiman yayi cike da shakku yace " to shikenan tunda kace haka Allah ya kyauta .
" Amin nagode abokina , Doctor Hamza ya amsa masa , domin ya sauƙaƙa yanayin rashin daɗi da ya hango a tare da Suleiman sai yace , " ina aka kwana kan batun lamarin ita Aminar taka ? ko idan muka je Maidugurin za'a yi wani motsi mai ƙarfi ne ? kasan fa kun jima da yarinyar nan ya ci ace anyi auren nan .
Cike da zaƙuwar jin an masa susa inda ke mar ƙaiƙayi Doctor Suleiman yace ," bari kawai abokina wannan yarinyar ko yau aka kawota gidana ta walashe ni , gyara zancen nan ka ma , saboda ai ni na jima ina son ta ba wai mun jima a tare ba , domin kuwa ai ita har yau bata wani bani dama ba , ni kaɗai ke fama ,
Ya dubi fuskar Doctor hamza da yayi kasaƙe cike da takaicin yadda ya zauna gotai-gotai da shi 'yar yarinya ƙanƙanuwa na masa yawo da hankali wajen shekaru uku , sai kace ƴa gwal ?
Doctor Suleiman ya katse zancen da Doctor Hamza yake son ɗorawa ta hanyar cigaba da cewa , " kar ka ga laifina Abokina , Amina ta cancani da kowanne ɗa Namiji yayi sha'awar ajiye mace mai nagartartun halaye da Addini haɗi da nutsuwa irin ta , wallahi ko kai da kan ka idan na baka labarin irin rayuwar da yarinyar take yi mai cike da tsantsanin kiyaye kan ta duk kuwa da cewa inda take rayuwa ƙazamtatce ne , halayyanta na ƙwarai nake kwaɗayi ba kome ba , saboda na sha gwada ta ba sau ɗaya ba , na kuma sa mutane wasu daban ma sun gwada ta amma ko sau ɗaya ban taɓa kamata da wani laifi saɓanin zahirin ta da take bayyane kullum cikin kamala da nutsuwa ba .
a yadda kake ƙyamatar halayen wasu matan nasan zaka yi mamakin nagartar da ita take da shi , kuma zaka bada goyan baya ɗari bisa ɗari akan na auro ta , musamman idan ka ji irin hali na tausayawa da suka riski kan su a ciki ita da ƴar uwar ta ,
Cike da gajiya da yadda ya zauna yana yabon wata wacce har yau shi da kan sa bata bashi darajar da za ta saurare shi ba , bare kuma su abokan sa Doctor Hamza yace " to Allah ya tabbatar da Alheri abokina .
Kamar yadda suka yi alƙawari ana saura kwanaki biyar ɗaurin Aure Mutanen N'Djamena suka iso ,sun tasamma mutane ishirin da ɗoriya , domin sun kusan cika falon Prof da anan suka fara ssuƙa , bayan an gaisa murnar sake ganin juna ta kachame a tsakanin su har da 'yan koke-koke , banda yaren su na larabaccin Chad babu abunda ke tashi a wajen ,
Zainab , Hafsa da suka iso tun jiya , har Rahima haÉ—i da Yakaka da Falmata , a tsakanin su duk babu wani mai jin yaren har sosai , dan haka sai suka tsaya kallon su fuskokin su É—auke da murmushi ,
Bayan sun ɗan nutsu sun sha ruwa da lemu , sai Matan suka shiga ciki inda za'a musu masauƙi ,
Mazan kuma suka tsaya anan Sashin Prof .
A ciki Amnee ta sake gabatar da Yakaka da Falmata , nan aka fara rungumar su ana sumbatar kumatun su da goshi , cike da nuna zallar ƙauna , daga baya kuma aka sake sabuwar gaisuwa har da su Hafsa da mafi yawa sun riga sun san su , su Yakaka ne baƙi .
Ba'a kwana ba Hajje Nadiya tare da tawagar ta mata huɗu da ta taho da su domin su taya ta suka buƙaci da su fara aikin da ya kawo su na gyaran Amare .
Tun ana saura kwanaki biyu ɗaurin Aure Sofiya ta iso Maiduguri , amma sai ta ƙi ƙarasawa gidan su Doctor Hamza tayi zaman ta a gidan su tare da Mamar ta Hajja kori , da ita ta zuga ta tace tayi zaman ta sai ana gobe ɗaurin auren da Yamma sai su tafi tare , ba dan kome ba kuwa sai dan rashin shirin da yake tsakanin su da Amnee da Khaalty Rahima .
Da ko kusa basu so Auren Amnee da yayan su ya sake ƙulluwa ba , kuma duk yadda suka so hana tabbatuwar lamarin fir Prof yaƙi saurarar su , ita kanta zuwan ta wajen sa biyu da zummar yi masa famfo amma bata samun fuska dan haka ta haƙura .
Babu abunda yafi ƙara basu haushi irin dawowar Khaalty Rahima da suka fi tsana gidan wannan karon har ma da marayun 'ya'yan ta kamar yadda labari ya iske su