Sashe 121
Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Lokacin da suleiman ke bashi amsa
Hamza kenan kai dai na rasa wanne irin tabo mace tayi maka a duniya kake musu irin wannan kuɗin goro , duk kuwa da yadda safiyya take tarairayar ka tare da lelen ka kamar wani jariri sabon haihuwa , bana jin ta taɓa saɓa maka a rayuwar zaman auren ku .
Ya ƙarasa zancen tare da dariyar shaƙiyanci .
Murmushin takaici doctor hamza yayi ,
  Baza ka taɓa ganewa ba suleiman !
Ya maida ganin ga madubin motar sa , yana hango ta ta jikin madubin ƙwarai tafiyar ta ta ɗau hankalin sa , mace ɗaya ya taɓa gani da salon takun nan , wacce bai ko son giftawar tunanin ta cikin ran sa sai fa yau da ya sake ganin wata wacce fuskar ta take a rufe Bai kai ga ganin kamannin ta ba .
Yakaka ashe daman irin zaman da kike da ni kenan ??
 Cewar lubna idanun ta na bayyana ɓacin rai ,
A kaikaice yakaka ta dube ta , kin ga sahiba bana ciki da rigima , daga kawai mutum ...
 Hmm
 Lubna ta katse ta ,
Wallahi sahiba abu É—aya zan faÉ—a miki a matsayin ki na wacce na É—auka Æ´ar uwa ,
Kar ki yadda kiyi wasa da damar da ta zo miki , idan har wannan mutumin da gaske yake ki bashi dama ku fahimci juna , aka yi bincike bashi da wani aibu wallahi ki bada dama kuyi auren ku shekarun mu sun fara tafiya ishirin da biyu mun rufa ta da uku muke hari ,wallahi wasa ba namu bane dama kuma sau É—aya take zuwa a rayuwa ,
 Shiru yakaka tayi
Kalmar ,"Dama," na maimaituwa a cikin kan ta , ita har tana da wata dama da ta rage mata kuwa ? Ai damar guda ɗaya da take da ita ta riga ta zo ta wuce tun a shekarun baya , " damar da mahaluki ɗaya ya bata wanda ta tabbatar baza ta taɓa samun makamancin sa ba, bata yi amfani da damar ba a maimakon haka ma sai tayi masa mummunan sakamo da har yau idan ta tuno shi kunya tare da nadama basa ƙasa a guiwa wajen danne ta ,
ina ma ina ma ina ma ?? Da ace dama zata dawo mata ? Da ace zai sake ba ta dama ko da gutsire daga irin damar da ya bata a baya ? Wataƙila da ta gyara kuskuren ta ta wata fuskar ,
, abunda ta sani shi ɗin ya riga ya mata nisa ita ta zama wata shuɗaɗɗɗan lamari da ya taɓa giftawa cikin rayuwar sa ,
Bata da wani shauƙi ko tunani mai armashi akan wani ɗa namiji har yau ta gaza sake son wani ɗa namiji , " zata iya cewa ta ƙi maza ," ƙi irin na wanda kunama ta taɓa harbin sa babu shakka idan ya ga gizo-gizo kakkaɓe shi yake , dangantakar nesa nesa ce ke tsakanin ta da maza ,
shiyasa har yau ta gaza samun saurayi ɗaya tak , ita ce bata saurarar su bata bada fuska , take boye kan ta tare da killace surar ta daidai da fuskar ta a rufe take , ta zaɓi hakan , ta kuma fi son tayi tsarayuwar ta a haka ba tare da wani ɗa namiji ya sake ratsa rayuwar ta , burin ta ɗaya ne shine tayi ilmi kuma tana godiya ga Allah tana godewa malama maryam tare da addu'ar Allah saka da alkhairi ga baki ɗayan zuri'ar ta ,
Ko da ko kusa bata sahun malumma amma kai tsaye a yau ta wuce a ƙira ta da jahila , ta nemi ilmi tana kan nema kuma zata cigaba da nema har.....
  Har suka kawo gida bata cewa lubna ƙala ba ,
  Sai da suka shigo gidan ta ruga da ɗan gudun ta ta rungume malama maryam wacce take tsaye daga ƙofar kitchen tana amsa sallamar su .
 Ni bazan yi aure ba har sai nayi ilmi na zama kamar ummi malama ta , sai ki san yadda zaki yi da mutumin da kika ba wa phone number .
Murmushi ummi tayi ,
  Anya kuwa yakaka ? Aure ai shine cikar darajar ɗiya mace
Lubna wacce take zama akan kujera ta shiga bada labari tiryan tiryan tana yi tana hararar yakaka wacce take yanka musu cabbage da zasu ci abincin rana da shi .
Sosai malama maryam ta yiwa yakaka faɗa daga ƙarshe ta ƙarƙare da yi mata nasiha tare da faɗa mata fa'idojin aure da girman matsayin sa a addini .
Jikin yakaka yayi sanyi har idanun ta na tara ƙwalla , ta gaza cin abinci na kirki .
A ƙarshe ta jaa kunnen ta akan daga yau kar ta ƙara ƙin saurarar duk wani namijin da yake da kamala da ya nuna yana son ta , ta ƙoƙarta ta saurare shi na ɗan wani lokaci ta fahimci wanene shi , daga nan idan ta yarda da halayen sa na ƙwarai ta bashi dama ita ma tayi aure , ko kusa kar ta kawo aƙidar ƙin aure kusa da ran ta saboda wani shuɗaɗɗan dalili nata , .
A ladabce ta amsa mata da zata yi yadda ta faÉ—a mata .
Bata wani jima ba saboda yadda walwalar ta tayi ƙaura ta musu sallama tana barin gidan ƙarƙashin rakiyar lubna wacce duk ta damu da rashin walwalar ƙawar ta ta , sai faman jan ta da hirar raha take ,
Har ƙofar gida ta rako ta ,
Zata tura ƙofar gidan ta shige lubna ta riƙo hannun ta , ta waiwayo tana kallon ta da sakakkiyar fuska .
Sahiba idan baƙya son sa idan ya ƙira insha Allah zan faɗa masa dan Allah ki bar damuwa .
Murmushi yakaka tayi ,
  Ni dai ban ce miki ba , kawai ....shiru tayi ,
  Baza ki gane ba sahiba .
Zan gane dan Allah ki faÉ—a min meye ne ? Duk banji daÉ—i ba da naga ranki a jagule
Ni bana son kowanne É—a namiji ilmi me zurfi nake da burin yi saboda ina da mummunan rauni a zuciyata wanda jahilci ne ya assasa min ina so na samu ilmin da zai warkar min da ciwon da na ji akan jahilci ,
A hankali lubna ta gyaÉ—a kai tana sakin hannun ta ,
 na fahimta,
ta furta hakan ba domin ta fahimce ta da gasken ba , abunda ta daɗe da sani cewa yakaka tana da wani binannen ƙuduri wanda take dakon sa boye cikin ran ta da ita bata riga ta san wanne irin kuɗiri ne ba .
Daga cikin niƙab ta sake yin murmushi ,
  Sahiba sai gobe zan zo ki bani labarin yadda kuka yi da ,"direba,"
  Ta ƙarasa zancen da dariya cikin muryar ta , ko kafin lubna ta bata amsa wacce ta yamutsa fuska tare da ƙanƙance ido
 Ta shige gidan da ɗan gudun ta tana jin lokacin da lubna ke cewa daɗin abun ma direban jirgin sama ne .
Da sallama ta shiga falon duk da cewa tayi ne ba domin tana sanya ran za'a amsa mata ba sai dan sanin muhimmancin sallama a musulunci da ta riga tayi .
Kamar yadda ta zata kuwa daga samira har hamshaƙiyar ƙawar ta da take haƙimce akan kujerar falon babu wanda ya amsa sallamar ta , hirar su suke cigaba da yi da take cike da shewa da dararraki irin na yaran matan da suke juya duniya a tafin hannun su .
Rage tsawo tayi ta ɗan durƙusa ,
Anty samy sannu da hutawa ,
Ke ke yaks wanne irin iskanci ne wannan ?? So nawa zan faɗa miki bana son kina shigo min gida da wannan maya-mayan yadikan da kike yawo da su a jiki , musamman ma na fuskar nan taki kamar wata korarriya daga makka ? To na faɗa miki yau ce rana ta ƙarshe .
A hankali yakaka ta kai hannu ta kunce niƙab ɗin fuskar ta , lokacin da sofi take kai ganin ta kan ta ,
Kiyi hakuri anty na cire .
To ya dai fi miki , yo Allah na tuba na sanya wannan mayanin a fuskata ai ya shaƙe min numfashi ya sheƙa da ni barzahu ban shirya ba ,
Kallon kallo suka yi a tsakanin su , kafin sofi ta janye idanun ta tana yatsina fuskar da ya zama halittar ta ,
Kirjin yakaka yayi dakan lugude , tsawon shekaru biyar bai isa a ce ta manta fuskar sofi ba matar da ganin farko haɗuwar su ta fari ta ɗau karan tsana ta aza musu ita da ƙanwar ta falmata , dan haka cikin hanzari ta miƙe tare da haɗiye kalaman gaisuwar da tayi niyyar miƙa mata , ta juya tana nufar ɗakin ta .
Friend wannan wacece ? Aina kika samo ƴar ƙwara ? Ko dai ko dai .... Ta ƙarasa zancen tana sakin wata shashashar dariya .
Ɗan murmushi samy baby tayi cikin ran ta bata mamakin rashin gane yakaka da sofi ta yi , ko ita da kan ta bata gajiya da kallon yakaka , wata irin fata ce da ita wacce bayan haske tana ɗauke da wani irin taushi tare da ƙyalli a idanu , ya haɗu da gyara tare da jimaka me kyau da take samu daga ita samy baby , haɗi da girma tare da cikar macen da take kan ganiyar ƙuruciyar ta , sai ta zama tamkar farin wata idan ta gifta dole ta ɗau hankali , ɗan tsararren jikin ta da yake a murmure kowanne irin kaya ta sanya masa kyau yake .
Ai ba domin tirjiya da yakakar take gwada mata ba da tuni maƙudan kuɗaɗe sun fara shigo mata ta hanyar yaks , amma wani ɗan lokaci kaɗan take jira wanda zata kammala aiwatar da nufin ta , ta kuma fara kwasar adashen da ta dunga zubawa a dalilin ta ,
Hamza kenan kai dai na rasa wanne irin tabo mace tayi maka a duniya kake musu irin wannan kuɗin goro , duk kuwa da yadda safiyya take tarairayar ka tare da lelen ka kamar wani jariri sabon haihuwa , bana jin ta taɓa saɓa maka a rayuwar zaman auren ku .
Ya ƙarasa zancen tare da dariyar shaƙiyanci .
Murmushin takaici doctor hamza yayi ,
  Baza ka taɓa ganewa ba suleiman !
Ya maida ganin ga madubin motar sa , yana hango ta ta jikin madubin ƙwarai tafiyar ta ta ɗau hankalin sa , mace ɗaya ya taɓa gani da salon takun nan , wacce bai ko son giftawar tunanin ta cikin ran sa sai fa yau da ya sake ganin wata wacce fuskar ta take a rufe Bai kai ga ganin kamannin ta ba .
Yakaka ashe daman irin zaman da kike da ni kenan ??
 Cewar lubna idanun ta na bayyana ɓacin rai ,
A kaikaice yakaka ta dube ta , kin ga sahiba bana ciki da rigima , daga kawai mutum ...
 Hmm
 Lubna ta katse ta ,
Wallahi sahiba abu É—aya zan faÉ—a miki a matsayin ki na wacce na É—auka Æ´ar uwa ,
Kar ki yadda kiyi wasa da damar da ta zo miki , idan har wannan mutumin da gaske yake ki bashi dama ku fahimci juna , aka yi bincike bashi da wani aibu wallahi ki bada dama kuyi auren ku shekarun mu sun fara tafiya ishirin da biyu mun rufa ta da uku muke hari ,wallahi wasa ba namu bane dama kuma sau É—aya take zuwa a rayuwa ,
 Shiru yakaka tayi
Kalmar ,"Dama," na maimaituwa a cikin kan ta , ita har tana da wata dama da ta rage mata kuwa ? Ai damar guda ɗaya da take da ita ta riga ta zo ta wuce tun a shekarun baya , " damar da mahaluki ɗaya ya bata wanda ta tabbatar baza ta taɓa samun makamancin sa ba, bata yi amfani da damar ba a maimakon haka ma sai tayi masa mummunan sakamo da har yau idan ta tuno shi kunya tare da nadama basa ƙasa a guiwa wajen danne ta ,
ina ma ina ma ina ma ?? Da ace dama zata dawo mata ? Da ace zai sake ba ta dama ko da gutsire daga irin damar da ya bata a baya ? Wataƙila da ta gyara kuskuren ta ta wata fuskar ,
, abunda ta sani shi ɗin ya riga ya mata nisa ita ta zama wata shuɗaɗɗɗan lamari da ya taɓa giftawa cikin rayuwar sa ,
Bata da wani shauƙi ko tunani mai armashi akan wani ɗa namiji har yau ta gaza sake son wani ɗa namiji , " zata iya cewa ta ƙi maza ," ƙi irin na wanda kunama ta taɓa harbin sa babu shakka idan ya ga gizo-gizo kakkaɓe shi yake , dangantakar nesa nesa ce ke tsakanin ta da maza ,
shiyasa har yau ta gaza samun saurayi ɗaya tak , ita ce bata saurarar su bata bada fuska , take boye kan ta tare da killace surar ta daidai da fuskar ta a rufe take , ta zaɓi hakan , ta kuma fi son tayi tsarayuwar ta a haka ba tare da wani ɗa namiji ya sake ratsa rayuwar ta , burin ta ɗaya ne shine tayi ilmi kuma tana godiya ga Allah tana godewa malama maryam tare da addu'ar Allah saka da alkhairi ga baki ɗayan zuri'ar ta ,
Ko da ko kusa bata sahun malumma amma kai tsaye a yau ta wuce a ƙira ta da jahila , ta nemi ilmi tana kan nema kuma zata cigaba da nema har.....
  Har suka kawo gida bata cewa lubna ƙala ba ,
  Sai da suka shigo gidan ta ruga da ɗan gudun ta ta rungume malama maryam wacce take tsaye daga ƙofar kitchen tana amsa sallamar su .
 Ni bazan yi aure ba har sai nayi ilmi na zama kamar ummi malama ta , sai ki san yadda zaki yi da mutumin da kika ba wa phone number .
Murmushi ummi tayi ,
  Anya kuwa yakaka ? Aure ai shine cikar darajar ɗiya mace
Lubna wacce take zama akan kujera ta shiga bada labari tiryan tiryan tana yi tana hararar yakaka wacce take yanka musu cabbage da zasu ci abincin rana da shi .
Sosai malama maryam ta yiwa yakaka faɗa daga ƙarshe ta ƙarƙare da yi mata nasiha tare da faɗa mata fa'idojin aure da girman matsayin sa a addini .
Jikin yakaka yayi sanyi har idanun ta na tara ƙwalla , ta gaza cin abinci na kirki .
A ƙarshe ta jaa kunnen ta akan daga yau kar ta ƙara ƙin saurarar duk wani namijin da yake da kamala da ya nuna yana son ta , ta ƙoƙarta ta saurare shi na ɗan wani lokaci ta fahimci wanene shi , daga nan idan ta yarda da halayen sa na ƙwarai ta bashi dama ita ma tayi aure , ko kusa kar ta kawo aƙidar ƙin aure kusa da ran ta saboda wani shuɗaɗɗan dalili nata , .
A ladabce ta amsa mata da zata yi yadda ta faÉ—a mata .
Bata wani jima ba saboda yadda walwalar ta tayi ƙaura ta musu sallama tana barin gidan ƙarƙashin rakiyar lubna wacce duk ta damu da rashin walwalar ƙawar ta ta , sai faman jan ta da hirar raha take ,
Har ƙofar gida ta rako ta ,
Zata tura ƙofar gidan ta shige lubna ta riƙo hannun ta , ta waiwayo tana kallon ta da sakakkiyar fuska .
Sahiba idan baƙya son sa idan ya ƙira insha Allah zan faɗa masa dan Allah ki bar damuwa .
Murmushi yakaka tayi ,
  Ni dai ban ce miki ba , kawai ....shiru tayi ,
  Baza ki gane ba sahiba .
Zan gane dan Allah ki faÉ—a min meye ne ? Duk banji daÉ—i ba da naga ranki a jagule
Ni bana son kowanne É—a namiji ilmi me zurfi nake da burin yi saboda ina da mummunan rauni a zuciyata wanda jahilci ne ya assasa min ina so na samu ilmin da zai warkar min da ciwon da na ji akan jahilci ,
A hankali lubna ta gyaÉ—a kai tana sakin hannun ta ,
 na fahimta,
ta furta hakan ba domin ta fahimce ta da gasken ba , abunda ta daɗe da sani cewa yakaka tana da wani binannen ƙuduri wanda take dakon sa boye cikin ran ta da ita bata riga ta san wanne irin kuɗiri ne ba .
Daga cikin niƙab ta sake yin murmushi ,
  Sahiba sai gobe zan zo ki bani labarin yadda kuka yi da ,"direba,"
  Ta ƙarasa zancen da dariya cikin muryar ta , ko kafin lubna ta bata amsa wacce ta yamutsa fuska tare da ƙanƙance ido
 Ta shige gidan da ɗan gudun ta tana jin lokacin da lubna ke cewa daɗin abun ma direban jirgin sama ne .
Da sallama ta shiga falon duk da cewa tayi ne ba domin tana sanya ran za'a amsa mata ba sai dan sanin muhimmancin sallama a musulunci da ta riga tayi .
Kamar yadda ta zata kuwa daga samira har hamshaƙiyar ƙawar ta da take haƙimce akan kujerar falon babu wanda ya amsa sallamar ta , hirar su suke cigaba da yi da take cike da shewa da dararraki irin na yaran matan da suke juya duniya a tafin hannun su .
Rage tsawo tayi ta ɗan durƙusa ,
Anty samy sannu da hutawa ,
Ke ke yaks wanne irin iskanci ne wannan ?? So nawa zan faɗa miki bana son kina shigo min gida da wannan maya-mayan yadikan da kike yawo da su a jiki , musamman ma na fuskar nan taki kamar wata korarriya daga makka ? To na faɗa miki yau ce rana ta ƙarshe .
A hankali yakaka ta kai hannu ta kunce niƙab ɗin fuskar ta , lokacin da sofi take kai ganin ta kan ta ,
Kiyi hakuri anty na cire .
To ya dai fi miki , yo Allah na tuba na sanya wannan mayanin a fuskata ai ya shaƙe min numfashi ya sheƙa da ni barzahu ban shirya ba ,
Kallon kallo suka yi a tsakanin su , kafin sofi ta janye idanun ta tana yatsina fuskar da ya zama halittar ta ,
Kirjin yakaka yayi dakan lugude , tsawon shekaru biyar bai isa a ce ta manta fuskar sofi ba matar da ganin farko haɗuwar su ta fari ta ɗau karan tsana ta aza musu ita da ƙanwar ta falmata , dan haka cikin hanzari ta miƙe tare da haɗiye kalaman gaisuwar da tayi niyyar miƙa mata , ta juya tana nufar ɗakin ta .
Friend wannan wacece ? Aina kika samo ƴar ƙwara ? Ko dai ko dai .... Ta ƙarasa zancen tana sakin wata shashashar dariya .
Ɗan murmushi samy baby tayi cikin ran ta bata mamakin rashin gane yakaka da sofi ta yi , ko ita da kan ta bata gajiya da kallon yakaka , wata irin fata ce da ita wacce bayan haske tana ɗauke da wani irin taushi tare da ƙyalli a idanu , ya haɗu da gyara tare da jimaka me kyau da take samu daga ita samy baby , haɗi da girma tare da cikar macen da take kan ganiyar ƙuruciyar ta , sai ta zama tamkar farin wata idan ta gifta dole ta ɗau hankali , ɗan tsararren jikin ta da yake a murmure kowanne irin kaya ta sanya masa kyau yake .
Ai ba domin tirjiya da yakakar take gwada mata ba da tuni maƙudan kuɗaɗe sun fara shigo mata ta hanyar yaks , amma wani ɗan lokaci kaɗan take jira wanda zata kammala aiwatar da nufin ta , ta kuma fara kwasar adashen da ta dunga zubawa a dalilin ta ,