Sashe 193
Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bata san ita kanta a matse take da son cin abincin ba sai da tayi arba da fari sol ɗin tuwon garin shinkafa da miyar kuɓewa busasshiya da aka ɗan ɗiga mata man shanu a ciki , babu laifi abincin su bai cika tsada ba da ɗan aukinsa , domin 'yan madai-daitan curi/mal-mala ne biyu kuma har da nama yanka biyu .
Da zaƙuwa ta fara cin abincin bayan ta juya baya daga mutanen da suke wajen ,
Tas ta cinye tuwon , ta É—an sha kunun gyaÉ—a da É—anyar shinkafa da yake fari sol shima ba'a cika sugar ba .
Kamar yadda Ahmadou gayu yace su yi guzuri bayan ta gama cin abincin sau kuma ta sayi gasasshen nama da ruwan roba biyu bata jinkirta ba koma mota , nan ta samu duk kowa ya dawo ita É—aya ake jira dan haka tana shiga , Gayu ya danna totur suka sake É—aukar hanya .
***
Biyamuradi Youssouf tare da Yakaka da Hajja babu inda basu nemi Falmata ba a tsuƙin unguwar suna haɗawa da cigiya , basu haɗu da ko wanda yace musu ya gan ta ba ,
Iyakar gigita Yakaka ta shige ta , hawaye da gumin zafin rana sun haɗar mata , tsoronta ɗaya ne kada Falmata ta yanke hukuncin tafiya yawan duniya , kamar yadda ita tayi , ta san halin Falmata sarai , tana da zafin rai idan har aka taɓo ta .
Tun a jiyan yadda tayi mata daman ya bata tsoro , sai dai bata yi tunanin zata iya yanke É—anyen hukunci irin haka ba , meyasa Falmata zata yi mata haka ? Meyasa baza ta yafe mata ba ?
Zuwa ƙarfe goma na safe sun gama cire rai da ganin ta , haɗuwa suka yi a falon kowannen su ya yi jugum ,
Youssouf ya É—ago kansa yana yiwa Yakaka kallon da yafi kama da harara ,
" Ina sake faɗi miki muddin ke kin ka ɓoye ta , ki fiddo ta kafin na kai ga sani da kaina,
A zuciye Yakaka ta katse shi ,
" Ka daina faɗa min maganar da bata da tushe , Falmata ƙanwa ta ce tare ka gan mu idan har ni ban ce sai ka nemo Falmata ba kai baka isa kace na sace ta ba Dan Allah ka barni na ji da damuwa ta .
"Kuyi haÆ™uri ku duka , lamarin ba na sa'in'sa bane mu ji da tashin hankalin da muke ciki , Babban soja ko za'a kai cigiya kafar watsa labarai ?? Abun yafi kama da sace ta aka yi idan ba haka ba ina UwarÉ—akina ta san gari bare har ta fita da kan ta , to ta tafi ina ? Ita da ba lafiyar ido da ta jiki ta cika ba , O Allah gamu gareka , ka iyar muna.Â
  Hajja ta ƙarasa zancen ta tana sake rafka tagumi
Tamkar an tsikareta Yakaka ta miƙe tana cewa
"muje tasha , tashar da ake hawa motar barin gari , wataƙila Falmata ta tafi Nigeria ne ,
Cikin ƴan mintoci suka cimma tasha , gurin da ake lodin fasinjan zuwa Nigeria suka nufa , suka tarar mafiyawan motoci sun riga sun tafi sai ɗaya ce bata kai ga tafiya ba ita ma mutane biyu ake jira ,
Babu Falmata a cikin su , dan haka Youssouf ya dunga bin Æ´an kamashon yana nuna musu hoton Falmata dake fuskar wayarsa tare da tambayar ko ta hau motar zuwa Nigeria ?
Kowa yace bai ganta a tashar ba , zuwa lokacin duk wani firgici da tashin hankali sun zana kansu ɓaro-ɓaro a fuskar sa da tayi jaa , jijiyoyin kansa kuma suka bayyana ruɗu-ruɗu , a sarari ya furta
" Fatima ina kin ka tafi ??
Dattijon ɗan kamashon da ya sa Falmata a motar Mallam Ahmadou shine ya ƙaraso gaban Youssouf da yake tsaye riƙe da kunkumin sa , sai duban gabas da yamma yake cikin rashin samun madafa,
" ance kun taho ne neman watta É—iya ko ta tai Nigeria kou ?
Cikin sarewa Youssouf ya amsa da "eh , yana share gumin goshin sa ,
"itta ce wata 'yar baƙa kakkaura mai matsakaicin tsawo tana da zanen barebari a fuskar ta ?
Youssouf da Yakaka a tare suka yi rige-rigen amsa masa da cewa "ita ce , tana ina ?
  Youssouf ya dora da nuna masa hoton Falmata domin ƙarin tabbatarwa, ya karɓi wayar bayan ya kashe idanu ya ƙure mata kallo , miƙawa Youssouf wayar yayi da yake ta bin sa da kallo cikin zaƙuwa ,
"Babu shakka itta ce wannan ta zou nan da gefen Alfijir, tana biÉ—ar motar zouwar jahar Borno Nigeria dagga nan kai tsaye , nan nayi mata togaciyar kan nisan dake tsakanin Niame....
  "Baba ina take yanzou ? Ta tahi ne ko kuwa tana ina ?
A kaikaice dattijon ya dubi Youssouf da ya katse masa hanzari , ya ɓantari goron sa kafin yace
 " ta taihi tun motar farko dagga nan kai tsaye zouwa Borno ta yankin diffa zasu ɓulla Nigeria zuwa yanzu wataƙila sun kusan cimma sandamun Maraɗi , ai Ahmadou gayu zaƙaƙurin direba ne ,
 " nufin ka dagga nan Fatima ta tai Borno ta yankin Diffa ? Yankin da yake cike da hatsarin ƴan tawayen Boko Haram suna kama mutane suna garkuwa da su bayan sun kashe wasu ? Bodar da take a rufe , sai ta ɓarauniyar hanya ake bi ? Shine kun ka turata baku hanata tafiya ba , ba kuyi yi la'akari da ƙarancin shekaru gami da rauninta na ɗiya macce ba ?
Wani irin raruma ya kaiwa Dattijon kafin ya ankara ya É—ago shi , cewa yake ,
 "ko waye direban kayi ƙiransa maza ya dawo da matata , kadda ya yarda ya jefa rayuwarta ga wannan mummunan hatsarin da kai da shi da zuri'ar ku baki ɗaya sai na ɗaure ku muddin wani mummunan abu ya afku ga matata ,
Da kyar mutane suka ɓanɓare hannuwan Youssouf daga wuyan dattijon nan da kawo lokacin numfashin sa ya fara ƙaƙarewa ,
Da ban baki gami da lallashi jama'a suka danni Youssouf ya nutsu aka nemo number Ahamdou gayu aka bashi ya shiga ƙira jikinsa sai tsuma yake ,
Da kyar ya samu wayar ta shiga , sai dai ko da aka ɗauka waƙar Barmani Mai-coge ce kawai take fitowa tarwai ta cikin wayar sai kuma iska irin na hanya ,
 Ya dunga "Alo , Alo , Alo ,
Bai ji muryar kowa ba , ya kashe ya sake ƙira nan ma an ɗaga amma "Alo, Alo , kawai ake cewa daga ɗaya ɓangaren , duk maganar da yake yi ba'a jinsa ,
Haka ya dunga ƙira cikin gigita tsawon lokaci ba'a ɗagawa daga baya ma daina shiga wayar tayi , cikin tashin hankali ya ɗago kansa , sai dai duk mutanen da suke tare a wajen ya tarar babu ko guda sun watse, sai fa Yakaka da take durƙushe a ƙasa tana hawaye sai kuma Hajja da take tsaye ta rafka tagumi idanunta da guntayen ƙwalla ,
Rasa wanda zai sake tunkara yayi , dan haka suka jiyo gida idan banda kuka babu abunda Yakaka take yi , jin cewa Falmata ta hau hanya mai tattare da hatsarin Æ´an Boko Haram , ya kaÉ—a Æ´an hanjinta ,
Zuciyarta ta cika da tsoron sake rasa ƙanwarta , Youssouf ma tunda suka dawo gida kai tsaye sashinsa ya shiga yana sake gwada ƙiran layin Ahmadou gayu , sai dai har chajin wayarsa ta kai ga sauƙa bai samu nasarar sake samun layin ba ,
Ajiye wayar yayi lokacin da wasu hawaye masu zafin gaske suka sauƙo masa a karo na biyu cikin tarihin rayuwar girmansa , yayi kuka .
***
Su Falmata sun kwana a wani ƙaramin gari dake yankin zinder kusa da garin Diffa , anan suka yada zango , cikin motar ita ta kwana yayin da sauran mazan suka fita ba tare da ta san ina suka yi ba .
Asubar fari bayan tayi Sallah , suka sake damƙar hanya , tafiyar yini guda ta kai su ga kaiwa ƙarshen yankin diffa ta gabashi , inda suka sau hanya tare da nausawa cikin daji ,
Gudun da motar take alhalin kan tuddai da kwari ne yasa motar take buga tsalle lokaci zuwa lokaci , da hakan yasa cikin falmata ya wani irin riƙewa tare da fara yin ciwo , ga buguwar da jikinta yake yi da motar , gami da warin sigari da bata san yaushe ya gauraye motar ba yana ƙoƙarin sanyata haraswa .
Duk da bata gani sosai ta fahimci dare yayi saboda duhu da ya mamaye É—an guntun hasken da idanun ta suke iya gani , ya zama dilum bata ganin kome .
Sun kai kimanin awanni biyu a daji suna wannan gudun kafin ta ji motar ta tsagaita gudu , ta tsaya a hankali ,
Hasken da ya dallare mata idanu mai ƙarfi ne da yasa ba shiri ta jaa hijabin ta ya rufe mata idanu , gami da runtse idanun .
Tana jin lokacin da duk na cikin motar suka fita harda shi direban , a hankali ta buÉ—e idanunta ta cikin motar tana iya ganin mutanen wajen dusu-dusu da taimakon hasken wasu manyan dogayen tociloli da suke hannuwan wasu gungun mutane ,
Abunda ya bata mamaki bai wuce ji da tayi sun juya harshe cikin yarenta ba na kanuri , tar-tar suke magana da Ahmadou gayu da sauran mutanen cikin motar da tunda tafiya ta haÉ—a su bata ji sun cika hira ba ko da kuwa a tsakaninsu ne , bare har ta fahimci yare su É—aya ..
Ba sosai ta kai ga Fahimtar maganganun su ba , har kawo lokacin da suka ƙaraso wajen motar , da hausa Ahmadou gayu yace ta fito za'a ɗau saƙo daga ƙarƙashin kujerar da take ,
Cikin sauri ta ziro ƙafar ta waje ta fito , cikin rashin sa'a ta gurɗe ta kusa faɗuwa ,
'yarinya ki kula ,
Cewar Ahmadou ,
Muryarta na Æ´ar rawa tace
"Baba inada matsalar ido bana gani idan dare yayi wajen babu ramuka ko ?
Da zaƙuwa ta fara cin abincin bayan ta juya baya daga mutanen da suke wajen ,
Tas ta cinye tuwon , ta É—an sha kunun gyaÉ—a da É—anyar shinkafa da yake fari sol shima ba'a cika sugar ba .
Kamar yadda Ahmadou gayu yace su yi guzuri bayan ta gama cin abincin sau kuma ta sayi gasasshen nama da ruwan roba biyu bata jinkirta ba koma mota , nan ta samu duk kowa ya dawo ita É—aya ake jira dan haka tana shiga , Gayu ya danna totur suka sake É—aukar hanya .
***
Biyamuradi Youssouf tare da Yakaka da Hajja babu inda basu nemi Falmata ba a tsuƙin unguwar suna haɗawa da cigiya , basu haɗu da ko wanda yace musu ya gan ta ba ,
Iyakar gigita Yakaka ta shige ta , hawaye da gumin zafin rana sun haɗar mata , tsoronta ɗaya ne kada Falmata ta yanke hukuncin tafiya yawan duniya , kamar yadda ita tayi , ta san halin Falmata sarai , tana da zafin rai idan har aka taɓo ta .
Tun a jiyan yadda tayi mata daman ya bata tsoro , sai dai bata yi tunanin zata iya yanke É—anyen hukunci irin haka ba , meyasa Falmata zata yi mata haka ? Meyasa baza ta yafe mata ba ?
Zuwa ƙarfe goma na safe sun gama cire rai da ganin ta , haɗuwa suka yi a falon kowannen su ya yi jugum ,
Youssouf ya É—ago kansa yana yiwa Yakaka kallon da yafi kama da harara ,
" Ina sake faɗi miki muddin ke kin ka ɓoye ta , ki fiddo ta kafin na kai ga sani da kaina,
A zuciye Yakaka ta katse shi ,
" Ka daina faɗa min maganar da bata da tushe , Falmata ƙanwa ta ce tare ka gan mu idan har ni ban ce sai ka nemo Falmata ba kai baka isa kace na sace ta ba Dan Allah ka barni na ji da damuwa ta .
"Kuyi haÆ™uri ku duka , lamarin ba na sa'in'sa bane mu ji da tashin hankalin da muke ciki , Babban soja ko za'a kai cigiya kafar watsa labarai ?? Abun yafi kama da sace ta aka yi idan ba haka ba ina UwarÉ—akina ta san gari bare har ta fita da kan ta , to ta tafi ina ? Ita da ba lafiyar ido da ta jiki ta cika ba , O Allah gamu gareka , ka iyar muna.Â
  Hajja ta ƙarasa zancen ta tana sake rafka tagumi
Tamkar an tsikareta Yakaka ta miƙe tana cewa
"muje tasha , tashar da ake hawa motar barin gari , wataƙila Falmata ta tafi Nigeria ne ,
Cikin ƴan mintoci suka cimma tasha , gurin da ake lodin fasinjan zuwa Nigeria suka nufa , suka tarar mafiyawan motoci sun riga sun tafi sai ɗaya ce bata kai ga tafiya ba ita ma mutane biyu ake jira ,
Babu Falmata a cikin su , dan haka Youssouf ya dunga bin Æ´an kamashon yana nuna musu hoton Falmata dake fuskar wayarsa tare da tambayar ko ta hau motar zuwa Nigeria ?
Kowa yace bai ganta a tashar ba , zuwa lokacin duk wani firgici da tashin hankali sun zana kansu ɓaro-ɓaro a fuskar sa da tayi jaa , jijiyoyin kansa kuma suka bayyana ruɗu-ruɗu , a sarari ya furta
" Fatima ina kin ka tafi ??
Dattijon ɗan kamashon da ya sa Falmata a motar Mallam Ahmadou shine ya ƙaraso gaban Youssouf da yake tsaye riƙe da kunkumin sa , sai duban gabas da yamma yake cikin rashin samun madafa,
" ance kun taho ne neman watta É—iya ko ta tai Nigeria kou ?
Cikin sarewa Youssouf ya amsa da "eh , yana share gumin goshin sa ,
"itta ce wata 'yar baƙa kakkaura mai matsakaicin tsawo tana da zanen barebari a fuskar ta ?
Youssouf da Yakaka a tare suka yi rige-rigen amsa masa da cewa "ita ce , tana ina ?
  Youssouf ya dora da nuna masa hoton Falmata domin ƙarin tabbatarwa, ya karɓi wayar bayan ya kashe idanu ya ƙure mata kallo , miƙawa Youssouf wayar yayi da yake ta bin sa da kallo cikin zaƙuwa ,
"Babu shakka itta ce wannan ta zou nan da gefen Alfijir, tana biÉ—ar motar zouwar jahar Borno Nigeria dagga nan kai tsaye , nan nayi mata togaciyar kan nisan dake tsakanin Niame....
  "Baba ina take yanzou ? Ta tahi ne ko kuwa tana ina ?
A kaikaice dattijon ya dubi Youssouf da ya katse masa hanzari , ya ɓantari goron sa kafin yace
 " ta taihi tun motar farko dagga nan kai tsaye zouwa Borno ta yankin diffa zasu ɓulla Nigeria zuwa yanzu wataƙila sun kusan cimma sandamun Maraɗi , ai Ahmadou gayu zaƙaƙurin direba ne ,
 " nufin ka dagga nan Fatima ta tai Borno ta yankin Diffa ? Yankin da yake cike da hatsarin ƴan tawayen Boko Haram suna kama mutane suna garkuwa da su bayan sun kashe wasu ? Bodar da take a rufe , sai ta ɓarauniyar hanya ake bi ? Shine kun ka turata baku hanata tafiya ba , ba kuyi yi la'akari da ƙarancin shekaru gami da rauninta na ɗiya macce ba ?
Wani irin raruma ya kaiwa Dattijon kafin ya ankara ya É—ago shi , cewa yake ,
 "ko waye direban kayi ƙiransa maza ya dawo da matata , kadda ya yarda ya jefa rayuwarta ga wannan mummunan hatsarin da kai da shi da zuri'ar ku baki ɗaya sai na ɗaure ku muddin wani mummunan abu ya afku ga matata ,
Da kyar mutane suka ɓanɓare hannuwan Youssouf daga wuyan dattijon nan da kawo lokacin numfashin sa ya fara ƙaƙarewa ,
Da ban baki gami da lallashi jama'a suka danni Youssouf ya nutsu aka nemo number Ahamdou gayu aka bashi ya shiga ƙira jikinsa sai tsuma yake ,
Da kyar ya samu wayar ta shiga , sai dai ko da aka ɗauka waƙar Barmani Mai-coge ce kawai take fitowa tarwai ta cikin wayar sai kuma iska irin na hanya ,
 Ya dunga "Alo , Alo , Alo ,
Bai ji muryar kowa ba , ya kashe ya sake ƙira nan ma an ɗaga amma "Alo, Alo , kawai ake cewa daga ɗaya ɓangaren , duk maganar da yake yi ba'a jinsa ,
Haka ya dunga ƙira cikin gigita tsawon lokaci ba'a ɗagawa daga baya ma daina shiga wayar tayi , cikin tashin hankali ya ɗago kansa , sai dai duk mutanen da suke tare a wajen ya tarar babu ko guda sun watse, sai fa Yakaka da take durƙushe a ƙasa tana hawaye sai kuma Hajja da take tsaye ta rafka tagumi idanunta da guntayen ƙwalla ,
Rasa wanda zai sake tunkara yayi , dan haka suka jiyo gida idan banda kuka babu abunda Yakaka take yi , jin cewa Falmata ta hau hanya mai tattare da hatsarin Æ´an Boko Haram , ya kaÉ—a Æ´an hanjinta ,
Zuciyarta ta cika da tsoron sake rasa ƙanwarta , Youssouf ma tunda suka dawo gida kai tsaye sashinsa ya shiga yana sake gwada ƙiran layin Ahmadou gayu , sai dai har chajin wayarsa ta kai ga sauƙa bai samu nasarar sake samun layin ba ,
Ajiye wayar yayi lokacin da wasu hawaye masu zafin gaske suka sauƙo masa a karo na biyu cikin tarihin rayuwar girmansa , yayi kuka .
***
Su Falmata sun kwana a wani ƙaramin gari dake yankin zinder kusa da garin Diffa , anan suka yada zango , cikin motar ita ta kwana yayin da sauran mazan suka fita ba tare da ta san ina suka yi ba .
Asubar fari bayan tayi Sallah , suka sake damƙar hanya , tafiyar yini guda ta kai su ga kaiwa ƙarshen yankin diffa ta gabashi , inda suka sau hanya tare da nausawa cikin daji ,
Gudun da motar take alhalin kan tuddai da kwari ne yasa motar take buga tsalle lokaci zuwa lokaci , da hakan yasa cikin falmata ya wani irin riƙewa tare da fara yin ciwo , ga buguwar da jikinta yake yi da motar , gami da warin sigari da bata san yaushe ya gauraye motar ba yana ƙoƙarin sanyata haraswa .
Duk da bata gani sosai ta fahimci dare yayi saboda duhu da ya mamaye É—an guntun hasken da idanun ta suke iya gani , ya zama dilum bata ganin kome .
Sun kai kimanin awanni biyu a daji suna wannan gudun kafin ta ji motar ta tsagaita gudu , ta tsaya a hankali ,
Hasken da ya dallare mata idanu mai ƙarfi ne da yasa ba shiri ta jaa hijabin ta ya rufe mata idanu , gami da runtse idanun .
Tana jin lokacin da duk na cikin motar suka fita harda shi direban , a hankali ta buÉ—e idanunta ta cikin motar tana iya ganin mutanen wajen dusu-dusu da taimakon hasken wasu manyan dogayen tociloli da suke hannuwan wasu gungun mutane ,
Abunda ya bata mamaki bai wuce ji da tayi sun juya harshe cikin yarenta ba na kanuri , tar-tar suke magana da Ahmadou gayu da sauran mutanen cikin motar da tunda tafiya ta haÉ—a su bata ji sun cika hira ba ko da kuwa a tsakaninsu ne , bare har ta fahimci yare su É—aya ..
Ba sosai ta kai ga Fahimtar maganganun su ba , har kawo lokacin da suka ƙaraso wajen motar , da hausa Ahmadou gayu yace ta fito za'a ɗau saƙo daga ƙarƙashin kujerar da take ,
Cikin sauri ta ziro ƙafar ta waje ta fito , cikin rashin sa'a ta gurɗe ta kusa faɗuwa ,
'yarinya ki kula ,
Cewar Ahmadou ,
Muryarta na Æ´ar rawa tace
"Baba inada matsalar ido bana gani idan dare yayi wajen babu ramuka ko ?