Sashe 116
Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
bai taɓa son ta ba , kawai amfani yayi da jahilcin ta ya ribaci gangar jikin ta ya yasar da ita tare da cikin da yayi mata , wani irin yanayi mai ƙarfi da kaifi ta ji yana keta zuciyar ta a game da shi , hannun ta ta kai ta tattaro bakin hijabin ta ta riƙe tare da cije gefen leɓen ta na ƙasa da ya zo daidai da zubowar hawayen ta da yake nuni da mummunan ƘULLACIN da tayi masa .... !!!!!!
[9/3, 10:13 PM] +234 806 122 1116: Fikrah writers association
MAFARI
( Hargitsin Rayuwa )
umm'muaz
31
Ba ƙaramin kaɗuwa Youssouf ya yi ba lokacin da Maimartaba yake shaida masa zancen auren sa da Siyama , da har an riga an miƙa dukiyar auren ta ga mahaifin ta dake niamey , za'a yi ɗaurin auren sa da ƴan matan duk biyu a rana guda kamar yadda ya buƙata ,
Ya jima a zaune gaban Maimartaba yana jin yadda zuciyar sa take cunkushewa da tarin takaici ,
Ba tun yau ba ya gama lura da take-taken yarinyar , shi yasa sam baya sakar mata fuska ashe bai sani ba har tayi girman da zata iya yin tsaurin ido irin haka a matsayin ta na mace ta doshi iyayen sa da buƙatar son a haɗa su aure ? Babu shakka zata ɗanɗani kuɗar ta a hannun sa , sai tayi danasanin wannan mummunan shisshigi da tayi ta kutso kan ta cikin rayuwar sa da take a hargitse a halin yanzu ,
Ganin shirun sa ya tsawaita ba tare da ya amsa da amincewar auren ba , ya sa me maimartaba yin gyaran murya
 Da fatan ba zaka bijirewa oumarnin mu ba ? Bisa ga wannan haɗi da munka yi na amre tsakanin ka da ƴar ouwar ka , saboda ba muyi haka ba face sai da munka hango tarin alkhaire tare da dacewa sannan munka so ƙulla igiyar amre a tsakankanin ku , wannan ɗiya ɗiyar ƴar uwa ta ce , kai ma kuma ƴar ouwa take gare ka , ina yi maka oumarni ka karɓi amren nan da hannu biyu da ikon Allah gaba kai zaka yi farin ciki .
Kalmar 'Umarni, ta daƙile dukkanin wani yunƙuri da zai iya yi , domin shi ɗin me yawan biyayya ne ga iyayen sa , haɗi da sanin da yayi a yanzu shi me tarin laifuka ne , wanda yake neman wata kafa ko yaya ne da zai iya faranta ran iyayen sa ta dalilin ta, ko domin su iya masa uzuri a duk ranar da laifukan sa suka bayyana a gare su , su duba irin faranta mu su da yayi su sassauta masa hukunci ,
Cikin harhaɗa kalmomin da suke suɓcewa daga harshen sa saboda kaifin su da yake iya ji ya furta ,
Na Amince , Allah shi ƙara girma da ɗaukaka .
Da murmushi bisa fuskar sa yace
Madallah da kai , Allah shi maka Albarka , Ya Albarkaci zuri'ar ka , Allah shi yi katanga tsakanin ka da miƙiya , kana iya tafiya ka fara shiri doumin nan da sati biyu da ranar tayi dai-dai da gomma ga watan gobe ake ɗaurin amre .
Godiya yayi ya miƙe yana barin shigifar sarki , kai tsaye gidan da zai tarar da Tafeeda ya nufa ,
Cikin sa'a ya same shi dawowar sa kenan daga aiki da sanyin la'asar ,
Babu walwala a fuskar sa ya samu wajen zama bisa kujerun shan iska ,
 Ɗan ouwa ka kuwa san me ke shirin farouwa gare ni ?
Maida ganin sa yayi kan sa , bayan ya miƙa masa sassanyan lemun da ya tsiyayo masa a kofin gilashi ,
Sanar da ni É—an ouwa
Wai amren mataye biyu a rana gouda , kuma amre tare da yarinyar nan siyama da ko ƙamnar duban ta bana yi , shin baka yi tounanin akwai wani dalili da ya sa maimartaba haɗa min amren mataye biyu a rana gouda ba ?
  Ɗan guntun murmushi tafeeda yayi
Banda abun ka Yarima shin amren mataye biyu a rana gouda ba gata bane ?
  Ita siyama ai duk inda ake neman macen amre ta zarta ,
 Maimartaba bashi da sani kan kome wataƙila hasashe ne yayi irin nasu na manya ya sanya shi yi maka gatan amra maka mataye biyu a rana gouda ,
Juyar da kan sa gefe yayi yana jin yadda ran sa ke sake ɓaci , kan batun auren , ga kuma ya lura Tafeeda ba shi da niyyar taya shi jimami , shi ina zai kai mata har uku a shekarun nan nasa ??
 Â
Kurɓar lemun sa tafeeda yake yi yana satar kallon youssouf da yayi tagumi hannu biyu ya nisa cikin tunani ,
  So yake ya masa tambaya game da al'amuran sa na ƙasar nigeria , ɗiyar sa da take can , ƙaƙa ya ƙarƙare da barin ta a chan ? Hannun wa ya baro ta ? Sai dai rashin son tuno masa da ita ya sanya shi haɗiye tambayoyin sa , ga zaton sa Biyamuradi yayi amfani da shawarwarin sa , ya baro duk wasu kuskuren da ya aikata a inda ya aikata su !
Farin cikin da Siyama ta tsinci kan ta cikin sa bai misaltuwa , domin duk wani da ke mu'amala ta kusa ko ta nesa da ita zai iya shaida farin cikin tare da walwalar da ke tare da ita , da ɗai bata taɓa farin ciki me yawan haka ba cikin rayuwar ta ,
  Ƙulluwar aure a tsakanin ta da Youssouf wani abu ne da tayi shekaru tana mafarkin sa a bacci ko a farke , bata taɓa zaton zata samu damar mallaƙar sa a matsayin miji a sauƙaƙe haka ba , a kuma daidai lokacin da take zaton ya sulluɓe mata zai zama malakin wata ba ita ba , duk tunanin ta na bata sai wani nisan shekaru wataƙila idan da rabo suyi aure , ga haɓakar farin cikin ta ashe tabbatuwar mafarkin ta zuwa gaske yana kurkusa , ashe tare zasu mallake shi ita da wacce take tunanin ta fita sa'a , ashe sa'ar na gare ne su biyu ,?
Bata ji ko É—ar ba akan sanin da tayi auren su auren haÉ—in iyaye ne , tare da sanin da take da shi akan irin tsanar da shi yake gwada mata , ta ji ta gani ta amince ta kuma shirya yin zaman aure da shi da gasken gaske , cikin kowanne irin hali , tana jin son da ita take masa zai ishe su rayuwa ita da shi ,
  Soyayyar sa ga gimbiya maimouna bata razana ta , illa kishi da ke nuƙurƙusa ran ta , dan haka ta sha alwashin ko da ƙaƙa , sai sun raba soyayyar youssouf biyu ita da maimouna kamar yadda zasu mallake shi a matsayin miji su biyu a lokaci guda , idan ya so ita na ta kason soyayyar idan ya so ya zubda a rariya , bata da damuwa son da take yi masa ya ishe su , .
Shiri take ka'in da na'in ubbo tana taya ta haiƙan , gefe guda hajiya umma na bada ta ta gudummawar a matsayin siyama na ɗiya a gare ta , ɗiyar da ta goya tayi rainon ta tun tana tsumman goyo ,
Lokacin da gnala take sanar da gimbiya maimuna dangantakar dake tsakanin youssouf da siyama har ma da zantukan da ta ji siyama na tattaunawa da ubbo , bata wani ɗau batun da muhimmanci ba , saboda wasu dalilai nata da take ganin ko da ace zai aure su su biyun ita bata jin hakan zai dame ta , burin ta ɗaya tal , shine ta samu nasarar aiwatar da ƙudurin da zai sa ta aure shi .
Dan haka ko da yake kame-kamen sanar da ita batun auren sa da siyamar yana bin ta da kalaman rarrashi , kwantar da murya tayi ta dunga zuba masa sassanyan rikicin da ya sake ɗaga darajar ta a idanun sa tare da sake dilmiyar da shi cikin ƙaunar ta ,
   Ya dunga jin yayi sa'ar samun nutsattsiyar mace kuma me haƙuri, wacce mace ce a zamanin yanzu da za'a yiwa kishiya gab da lokacin auren ta , a kuma haɗa su aure rana guda , ba'a yi danbarwa da ita ba ? Ƙwarai ƙwarai maimouna ta ƙara ƙima a idanun sa ,
Samun haɗin kan ta farad ɗaya ya lafa guguwar ƙin auren a cikin ran sa , sai ya samu nutsuwar fuskantar shirye-shiryen auren tare da cigaba da zarya wajen sabon gurin aikin sa da aka tura shi Dosso , inda zai zama shugaban soji na baki ɗayan yankin na jahar Dosso ,
Tafkeken gida aka mallaka masa tare da motocin hawa biyu , ƙari da tarin hadimai sojoji tun daga kan masu gadi , direba , har zuwa kan me girki .
Tsakanin jahar Maraɗi da jahar Dosso babu tazara me yawa , dan haka lokacin da yake da samun tabbacin wajen zama a dosso , sai yayi niyyar bayan bikin su , zai dawo da gimbiya maimouna nan gidan sa na dosso , kusa da shi , ita kuwa siyama ta cigaba da zama can a maraɗi , tunda ita ta zaɓi auren cikin gida sai ta samu matabbata a cikin gidan , !
Sai dai yana sanar da hajiya umma niyyar sa , a take ya ga sauyin fuskar ta ,
   Abu guda ta ce da shi .
Kome tsanani kayi ƙoƙarin kwatanta adalci tsakankanin matayen da Allah ya baka amanar riƙon amren su , kar ka kuskura ka karkata ga ɗaya daga cikin su , saboda gujewa fushin Allah da azabar sa ka kiyaye , siyama da maimouna duk su biyun matan amren ka ne .
*****
Tun farkon satin aka fara gudanar da shagulgula da wasannin daga bangaren masarautar maraÉ—i har da ta Agades wanda suke da tarin wasannani da al'adun gargajiya fiye da na maraÉ—i , haÉ—i da shiri sosai da suka yi na bikin kasantuwar kowa ya san gimbiya maimouna É—iyar gata ce ta sosai ,
[9/3, 10:13 PM] +234 806 122 1116: Fikrah writers association
MAFARI
( Hargitsin Rayuwa )
umm'muaz
31
Ba ƙaramin kaɗuwa Youssouf ya yi ba lokacin da Maimartaba yake shaida masa zancen auren sa da Siyama , da har an riga an miƙa dukiyar auren ta ga mahaifin ta dake niamey , za'a yi ɗaurin auren sa da ƴan matan duk biyu a rana guda kamar yadda ya buƙata ,
Ya jima a zaune gaban Maimartaba yana jin yadda zuciyar sa take cunkushewa da tarin takaici ,
Ba tun yau ba ya gama lura da take-taken yarinyar , shi yasa sam baya sakar mata fuska ashe bai sani ba har tayi girman da zata iya yin tsaurin ido irin haka a matsayin ta na mace ta doshi iyayen sa da buƙatar son a haɗa su aure ? Babu shakka zata ɗanɗani kuɗar ta a hannun sa , sai tayi danasanin wannan mummunan shisshigi da tayi ta kutso kan ta cikin rayuwar sa da take a hargitse a halin yanzu ,
Ganin shirun sa ya tsawaita ba tare da ya amsa da amincewar auren ba , ya sa me maimartaba yin gyaran murya
 Da fatan ba zaka bijirewa oumarnin mu ba ? Bisa ga wannan haɗi da munka yi na amre tsakanin ka da ƴar ouwar ka , saboda ba muyi haka ba face sai da munka hango tarin alkhaire tare da dacewa sannan munka so ƙulla igiyar amre a tsakankanin ku , wannan ɗiya ɗiyar ƴar uwa ta ce , kai ma kuma ƴar ouwa take gare ka , ina yi maka oumarni ka karɓi amren nan da hannu biyu da ikon Allah gaba kai zaka yi farin ciki .
Kalmar 'Umarni, ta daƙile dukkanin wani yunƙuri da zai iya yi , domin shi ɗin me yawan biyayya ne ga iyayen sa , haɗi da sanin da yayi a yanzu shi me tarin laifuka ne , wanda yake neman wata kafa ko yaya ne da zai iya faranta ran iyayen sa ta dalilin ta, ko domin su iya masa uzuri a duk ranar da laifukan sa suka bayyana a gare su , su duba irin faranta mu su da yayi su sassauta masa hukunci ,
Cikin harhaɗa kalmomin da suke suɓcewa daga harshen sa saboda kaifin su da yake iya ji ya furta ,
Na Amince , Allah shi ƙara girma da ɗaukaka .
Da murmushi bisa fuskar sa yace
Madallah da kai , Allah shi maka Albarka , Ya Albarkaci zuri'ar ka , Allah shi yi katanga tsakanin ka da miƙiya , kana iya tafiya ka fara shiri doumin nan da sati biyu da ranar tayi dai-dai da gomma ga watan gobe ake ɗaurin amre .
Godiya yayi ya miƙe yana barin shigifar sarki , kai tsaye gidan da zai tarar da Tafeeda ya nufa ,
Cikin sa'a ya same shi dawowar sa kenan daga aiki da sanyin la'asar ,
Babu walwala a fuskar sa ya samu wajen zama bisa kujerun shan iska ,
 Ɗan ouwa ka kuwa san me ke shirin farouwa gare ni ?
Maida ganin sa yayi kan sa , bayan ya miƙa masa sassanyan lemun da ya tsiyayo masa a kofin gilashi ,
Sanar da ni É—an ouwa
Wai amren mataye biyu a rana gouda , kuma amre tare da yarinyar nan siyama da ko ƙamnar duban ta bana yi , shin baka yi tounanin akwai wani dalili da ya sa maimartaba haɗa min amren mataye biyu a rana gouda ba ?
  Ɗan guntun murmushi tafeeda yayi
Banda abun ka Yarima shin amren mataye biyu a rana gouda ba gata bane ?
  Ita siyama ai duk inda ake neman macen amre ta zarta ,
 Maimartaba bashi da sani kan kome wataƙila hasashe ne yayi irin nasu na manya ya sanya shi yi maka gatan amra maka mataye biyu a rana gouda ,
Juyar da kan sa gefe yayi yana jin yadda ran sa ke sake ɓaci , kan batun auren , ga kuma ya lura Tafeeda ba shi da niyyar taya shi jimami , shi ina zai kai mata har uku a shekarun nan nasa ??
 Â
Kurɓar lemun sa tafeeda yake yi yana satar kallon youssouf da yayi tagumi hannu biyu ya nisa cikin tunani ,
  So yake ya masa tambaya game da al'amuran sa na ƙasar nigeria , ɗiyar sa da take can , ƙaƙa ya ƙarƙare da barin ta a chan ? Hannun wa ya baro ta ? Sai dai rashin son tuno masa da ita ya sanya shi haɗiye tambayoyin sa , ga zaton sa Biyamuradi yayi amfani da shawarwarin sa , ya baro duk wasu kuskuren da ya aikata a inda ya aikata su !
Farin cikin da Siyama ta tsinci kan ta cikin sa bai misaltuwa , domin duk wani da ke mu'amala ta kusa ko ta nesa da ita zai iya shaida farin cikin tare da walwalar da ke tare da ita , da ɗai bata taɓa farin ciki me yawan haka ba cikin rayuwar ta ,
  Ƙulluwar aure a tsakanin ta da Youssouf wani abu ne da tayi shekaru tana mafarkin sa a bacci ko a farke , bata taɓa zaton zata samu damar mallaƙar sa a matsayin miji a sauƙaƙe haka ba , a kuma daidai lokacin da take zaton ya sulluɓe mata zai zama malakin wata ba ita ba , duk tunanin ta na bata sai wani nisan shekaru wataƙila idan da rabo suyi aure , ga haɓakar farin cikin ta ashe tabbatuwar mafarkin ta zuwa gaske yana kurkusa , ashe tare zasu mallake shi ita da wacce take tunanin ta fita sa'a , ashe sa'ar na gare ne su biyu ,?
Bata ji ko É—ar ba akan sanin da tayi auren su auren haÉ—in iyaye ne , tare da sanin da take da shi akan irin tsanar da shi yake gwada mata , ta ji ta gani ta amince ta kuma shirya yin zaman aure da shi da gasken gaske , cikin kowanne irin hali , tana jin son da ita take masa zai ishe su rayuwa ita da shi ,
  Soyayyar sa ga gimbiya maimouna bata razana ta , illa kishi da ke nuƙurƙusa ran ta , dan haka ta sha alwashin ko da ƙaƙa , sai sun raba soyayyar youssouf biyu ita da maimouna kamar yadda zasu mallake shi a matsayin miji su biyu a lokaci guda , idan ya so ita na ta kason soyayyar idan ya so ya zubda a rariya , bata da damuwa son da take yi masa ya ishe su , .
Shiri take ka'in da na'in ubbo tana taya ta haiƙan , gefe guda hajiya umma na bada ta ta gudummawar a matsayin siyama na ɗiya a gare ta , ɗiyar da ta goya tayi rainon ta tun tana tsumman goyo ,
Lokacin da gnala take sanar da gimbiya maimuna dangantakar dake tsakanin youssouf da siyama har ma da zantukan da ta ji siyama na tattaunawa da ubbo , bata wani ɗau batun da muhimmanci ba , saboda wasu dalilai nata da take ganin ko da ace zai aure su su biyun ita bata jin hakan zai dame ta , burin ta ɗaya tal , shine ta samu nasarar aiwatar da ƙudurin da zai sa ta aure shi .
Dan haka ko da yake kame-kamen sanar da ita batun auren sa da siyamar yana bin ta da kalaman rarrashi , kwantar da murya tayi ta dunga zuba masa sassanyan rikicin da ya sake ɗaga darajar ta a idanun sa tare da sake dilmiyar da shi cikin ƙaunar ta ,
   Ya dunga jin yayi sa'ar samun nutsattsiyar mace kuma me haƙuri, wacce mace ce a zamanin yanzu da za'a yiwa kishiya gab da lokacin auren ta , a kuma haɗa su aure rana guda , ba'a yi danbarwa da ita ba ? Ƙwarai ƙwarai maimouna ta ƙara ƙima a idanun sa ,
Samun haɗin kan ta farad ɗaya ya lafa guguwar ƙin auren a cikin ran sa , sai ya samu nutsuwar fuskantar shirye-shiryen auren tare da cigaba da zarya wajen sabon gurin aikin sa da aka tura shi Dosso , inda zai zama shugaban soji na baki ɗayan yankin na jahar Dosso ,
Tafkeken gida aka mallaka masa tare da motocin hawa biyu , ƙari da tarin hadimai sojoji tun daga kan masu gadi , direba , har zuwa kan me girki .
Tsakanin jahar Maraɗi da jahar Dosso babu tazara me yawa , dan haka lokacin da yake da samun tabbacin wajen zama a dosso , sai yayi niyyar bayan bikin su , zai dawo da gimbiya maimouna nan gidan sa na dosso , kusa da shi , ita kuwa siyama ta cigaba da zama can a maraɗi , tunda ita ta zaɓi auren cikin gida sai ta samu matabbata a cikin gidan , !
Sai dai yana sanar da hajiya umma niyyar sa , a take ya ga sauyin fuskar ta ,
   Abu guda ta ce da shi .
Kome tsanani kayi ƙoƙarin kwatanta adalci tsakankanin matayen da Allah ya baka amanar riƙon amren su , kar ka kuskura ka karkata ga ɗaya daga cikin su , saboda gujewa fushin Allah da azabar sa ka kiyaye , siyama da maimouna duk su biyun matan amren ka ne .
*****
Tun farkon satin aka fara gudanar da shagulgula da wasannin daga bangaren masarautar maraÉ—i har da ta Agades wanda suke da tarin wasannani da al'adun gargajiya fiye da na maraÉ—i , haÉ—i da shiri sosai da suka yi na bikin kasantuwar kowa ya san gimbiya maimouna É—iyar gata ce ta sosai ,