← Book details Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 209 OF 269

Sashe 209

Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

   Ɗago da kan sa yayi ya dubi iyayen sa , yanayin da ya gani a kan fuskokin su,  su duka biyu ya razana shi musamman ma Amnee dake masa wani kallo mai kama da harara , da sauri ya mayar da kansa ƙasa kafin muryarsa cikin rashin amo sosai ta fito ,
       " Na'amince Baba , Na Amince Baa .

Daga haka yayi shiru yana jin wani irin ɓacin-rai da ya taho masa tare da Amincewa auren yarinyar da ta gama yawon ta shekara da shekaru dan kawai tana ƴar uwar sa ,

Daga sama ya tsinkayo muryar Prof yana cigaba da cewa ,
   " To Alhamdulillah Allah ya maka Albarka , ya baka 'ya'yan da zasu maka biyayya fiye da yadda ka min , Ubangiji Allah ya jiɓanci lamarin ka ya raba ka da sharrin duniya, Allah ya sa Albarka a zaman ku ya baku zuri'a masu yawa da Albarka , ka faranta min rai sosai .

Ya nisa lokacin da Amnee wacce haƙoranta ke washe tana ƴar dariyar dake nuni da zallar farin-cikin da take ciki take amsa addu'o'in sa ya cigaba da cewa ,
  " za'a haɗa auren naku da na Rahima ayi shi duk a rana ɗaya dan a rage hidima idan ya so ko bayan sati guda ne idan ka samar mata muhallin da ya dace da ta zauna a can Abujan kusa da kai sai ka taho ka ɗauke ta hakan yayi ko ?
  Yace yana mayar da ganin sa kan Amnee , wacce ta gyaɗa kai da sauri da maɗaukakin fara'a a fuskar ta tace , "Yayi sosai ma Baa Alaji , cikin sati uku masu zuwa ai su zainab sa iya zuwa Dubai yiwa takwarata kayan ɗaki .

Da wani irin bahagon yanayi Doctor hamza ya É—ago yana kallon su ,

Khaalty Rahima da duk hankalinta ke kan sa ta yi gyaran murya kaɗan , cikin ƙanƙan da kai tace ,
  "Yaa ka min izni nayi magana wannan karon a matsayina na innar ango madadin uwa ,
   Murmushi Prof yayi , "An miki izni , yace

" Yaya Dan Allah a mana alfarma , bayan an ɗaura auren a bamu ko da watanni biyu ne ya kammala shirin sa , kamar samar da wajen zama a tsanake , ya kuma sanar da uwargidan sa cikin kwanciyar rai ,  ya ɗan samu ya dai-daita lamuransa ,tunda nawi ne zai ƙaru masa kar a tsawwala yafi kyau yayi kome cikin lumana tunda indai ta zama matar sa ai kome ya kammala .

Cike da amincewa Prof yace , " To shikenan tunda kun nemi wannan Alfarmar an muku , amma ya tabbar kafin cikar watanni biyun ya kammala duk wasu shirye-shirye tunda É—an naki ai Babban likita ne albashin sa ya kai wani mizani amma duk da haka na É—auke mar nawin sadaki da duk wasu hidindumu da suka shafi biki na shi hidimar shine ya samar mata da muhalli mai kyau tare da É—aura aniyar kulawa da duk wasu hakoki nata da suke kan shi daga ranar da zata shiga gidan sa har zuwa ranar da mutuwa zata É—auki É—ayan su , kaji ko ?
  Ya ƙarasa zancen yana juya akalar tambayar sa ga Hamza ,
  " Gyaɗa kai yayi nagode Baa Allah ya ƙara girma ya furta hakan yana miƙewa yayi hanyar ficewa daga falon , Khaalty Rahima ma godiyar tayi musu sosai kamar zata zubda ƙwalla dan farin-cikin gatan da ake shirin yiwa ƴar ta ,

Tafe yake baya sanin ina yake ajiye ƙafar sa ,  Jacket ɗin sa riƙe a hannun sa saboda zafi da yake ji yana damunsa kota'ina cikin jikin sa tsabar tashin hankali , abunda ya faru yanzu a falon Baa so yake ace wani rarraunan mafarki ne daga cikin jerin shuɗaɗɗun mafarkan da ya dunga yi a shekarun baya , domin tuntuni ya wanke tabbatuwa hakan daga zuciya da tunanin sa .

Har ya kusa sashin sa ya tsinkayo muryar Khaalty Rahima tana ƙiran sa , juyowa yayi yana ƙirkiro wani rarraunan murmushi ya ɗora a fuskar sa ,
  Ta ƙaraso idanun ta akan fuskar sa tana nazarin sa , muryar ta cike da nutsuwa tace
   " Hamza kada fa ka damu kan ka wajen yin duk wasu hidindimu ko da gidan da zata zauna ɗin ma ka kama muku mai sauƙi idan ma ba hali ko ɗaki guda sai a bata a cikin gidan da kuke zaune nasan 'yata safiya ba zata ƙi ba , idan kuma duk hakan bata samu ba , zan sa Ukhtee ta roƙi Yaya ko anan sashin naka na gidan nan ai sai a barta tayi zaman ta ba ma sai ta tafi can Abujan ba , shi zaman aure ai bautar Ubangiji ce wurin Mace da Namiji baki ɗaya .

  Tausayin ta ya kama shi , bai bar murmushin da yake yi ba yace " kar ki damu Khaalty yadda duk Baa ya ce haka za'a yi inshaAllah babu abunda zai gagara ,

  Murmushi tayi , sannan ta cigaba da cewa , "Nagode, Nagode , yadda ka rufa min asiri kaima Allah ya rufa maka, ya baka 'ya'yan da zasu maka fiye da abunda kayi ga iyayen ka , nagode nag...

Hannunta ya riƙo ," haba Khaalty godiyar me kike min haka , ai ni...
  Da sauri ta katse shi , tana cewa "Godiyar kome ma , ka yi kome da yakamata nayi ta gode ma Hamza Allah ya ma Albarka ,

  " Amin ya amsa yana sakin hannun ta ya juya ya nufi sashin sa ,

A hanya komawa ciki Khaalty Rahima da Amnee suka haÉ—u , cike da farin-ciki suka rungume juna ba sai bakunan su sun furtawa junan su ba babu makawa sun san zucoyoyin su cike suke da farin-cikin faruwar wannan lamari.

" Baa Alaji yace a tambayi takwarata ita ma, ko ta amince ? Ko kuwa tana da wani wanda take so ya shirya yin aure , dan fa ba za'a mata dole ba ,

Ɗaure fuska Khaalty Rahima tayi , " wanne irin ma a nemi amincewar ta Ukhtee ? Shi namiji ma aka masa dole bare ita mace ?ai koma waye take so dole ta haƙura tunda Yaya ya yanke hukunci .

Murmushi Amnee tayi , " wa yace miki dole aka yiwa É—an ki ? Ba soyayya bace ya sa ya É—auko ta ya kawo ta gidan nan lokacin ma bai san ko suwaye su ba ? Ai kawai dan dai kaddara ta gifta tsakani badan haka ba da auren su ma zaki gan su ,

Ƴar fara'a Khaalty Rahima tayi , " duk da haka Ukhtee kin san fa irin aibun da yake tare da takwarar taki , ni gani nayi kamar an tauye shi da aka liƙa masa auren ta , kuma a yadda ma na lura yanzu ɗan nawa baya yi da takwarar taki ko da a baya ya nuna ra'ayin sa akan ta ,

Wucewa gaba Amnee tayi tana cewa " koma menene dai idan aka yi auren ai sa shirya kan su , so na gaskiya ai baya kankaruwa sai dai wani abu ya dusashe tasirin sa , ni bari naje na samu takwarata na shawo kanta ta amince ayi abun nan ranta na so , ba zan so ba a takuramin ita da auren dole ,

Ƴar ajiyar zuciya Khaalty Rahima tayi tana murmushi ta bi bayan Amnee zuciyar ta cike taf da ƙauna tare da farin-ciki marar misaltuwa da rabon ta da irin sa shekarun dayawa .

***

A É—aki Amnee ta tarar da su ukun suna gwada É—inkunan su , Falmata tana mitar burguza-burguzan riguna da siket É—in da telan ya yi mata , " mai sunan Mama dan Allah ki ga wannan siket É—in yadda ya min yawa ba ko fasali ni É—ai gaskiya a mayar ya rage min , naku ke da Yakaka cas-cas irin na Æ´an mata amma ni shine ya min haka siket kamar buhu ?
   Dariyar da tuntuni Yakaka take riƙewa ita ta ɓurtso kanta , cikin dariyar take cewa ,
   " Kai Falmata gaskiya ba'a iyar miki , ke kome aka miki bai yi ba, yanzu da matsattsu aka miki cewa za ki yi sun matse ki sun hana Baby sakewa yanzu kuma anyi wanda Baby zai wataya kince an miki buhu , Allah kana gani dai ,  ka shirya min Falmata ,

   " zunɓuro baki Falmata tayi dai-dai da shigowar Amnee da Mamar su ,
   " Maama kin ga ku faɗa musu su daina tsokana ta kullum Rahima da Yakaka basu da abun yi sai tsokana ta, yanzu ku ga irin ɗinki da suka kai aka min ,
ta É—aga siket É—in ta ,
"ku ga kuma nasu ,
tace tana ɗaukar siket ɗin Yakaka ta nuno , ta ɗora da cewa  " dan Allah Amnee za'a ce tela ɗaya ya ɗinka ? Nawa kamar wata gani garau , nasu kuma na yayi ?

  Karɓar kayan Amnee tayi tana ajiyesu gefe , tace " sun yi girma kam , kiyi haƙuri za'a mayar ya rage miki wannan ɗinki ai ko a Niger ayi wanda ya fi shi tsari bare anan Nigeria gidan cancara ɗinki ,

Ganin ta ta mayar kan Yakaka da take kallon su tana dariya da haƙori ,

   " Zo nan ki zauna takwara ta magana nake tafe da ita mai muhimmanci , duk ku nutsu ku bar shirmen nan ,
  Amne ta furta hakan lokacin da take zama a bakin gadon , tana yiwa Yakaka nuni da gefen ta kusa .

A nutse Yakaka ta taho kusa da ƙafafun Amnee ta zauna a ƙasa maimakon gefen ta da ta nuna mata ,

Cikin nazari Amnee tace ,
   "  Takwara akwai wanda kuke tare ne ? Ina nufin akwai wanda kuka yi wata magana ta aure da shi ??
Chapter 209 · 0% Book details