← Book details Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 198 OF 269

Sashe 198

Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

" Nagoude ƙamnata kouma Matata , ya furta hakan yana sumbatar kan ta ,

    Idanunta ta runtse da hakan ya bawa ƙwallar dake cike a gurbin idanunta damar zubowa , tana sauƙa akan kirjin sa .

Kanta take tausayawa yadda zuciyarta ta afu ga son maso wani irin haka , ta san zafi da raɗaɗin rashin abun so dan haka take tausaya masa babu shakka ita bata da makaman yaƙin tunkarar ko wacece wannan Fatima da ake ta ƙiƙi-ƙaƙa akan ta da ta sanya Mijinta ya ɗimauce tare da jan ɗamarar yaƙi da duk wasu masu son shiga tsakanin sa da Abar son sa , labarin kome da ya faru tuni ya iske ta ta bakin Ubbo ,

Da tundaga lokacin tayi kuka tare da jimaminta ta har ta kusa faɗuwa jinya da taimakon Mai aikinta Rakiya da ta riƙa tamkar ƙawar shawarwarin ta , ta samu dawowar nutsuwar ta da Rakiya tayi ta bata shawarwari masu inganci tare da kwantar mata da hankali .

" Baban Yumna mu tai ka ci abincin ,

  " Bani jin Yunwa yanzou sai ko anjima kaɗan ,

  Bata ƙara cewa da shi kome ba ta miƙe , tana barin ɗakin , zuciyarta baza ta juri ganin sa haka cikin ciwon son wata daban ba .

Haka Youssouf ya ɗebe awanni cikin yanayi na bacci-bacci ido biyu , ( yayi likimo😂 )

Zuwa gefen la'asar ya sake yin wanka tare da shiri ya tafi Masallaci.

***

Nan ya cigaba da zama yana addu'o'i tare da karatun Alkur'ani har zuwa shigowar lokacin Sallar magariba , da idarwar sa ɗan sako ya zo masa cewa Maimartaba yana son ganinsa a can turakar sa ta ganawa da baƙi .

Da azama ya miƙe ƙarƙashin jagorar ɗan aiken suka cimma turakar Maimartaba , inda ya tarar da shi , shi kaɗai .

Bayan sun sake gaisawa yayi shiru a zaune , daga ƙasa gaban kujerar da Maimartaba yake zaune ,

An ɗauki lokaci Maimartaba yana kallon shi baice da shi ƙala ba , yana nazarin tashin hankalin da ya bayyana a suffar sa , sai bayan wasu ƴan mintoci yayi gyaran murya
  "Youssoufa , ya ƙira sunan sa ,
   "Na'am ranka shi daɗe , yace yana sake ƙan-ƙan da kai ,
   "Matso kussa Youssouf ka samrari abounda zan ce da kai ,

Da sauri ya muskuɗa ya dawo kusa sosai da ƙafafun Maimartaba,

Cikin muryar da take cike da ilhama tare da tarin ilmi maimartaba yace ,"Youssoufa  sa'ad da Ubangiji ya tsawatar maka ka mai da hankali sosai, ka kuma yarda da gargaɗinsa, Ubangiji yana tsawatar wa waɗanda yake ƙauna. Kamar yadda mahaifi yakan tsawatar wa ɗan da yake fa'ariya da shi,

"Kada ka zurfafa wajen biyewa tunani tunane-tunanenka mafarin rai ne kansa, ka kiyaye su abin mallakarka ne mafi daraja,

"Kada ka faɗi kowane abu da yake ba na gaskiya ba, kada wani abu ya haɗa ka da ƙarya, ko maganganun ruɗarwa, ka duba gaba sosai gabanka gaɗi, ba tsoro ka tabbata ka san abin da kake yi, duk abin da kake yi kuma zai zama daidai ,

Idan har kayi haka ? ba za ka ji tsoro, sa'ad da kake kwance a gadonka ba, za ka yi ta sharar barci a dukan dare, ba za ka damu da masifar da za ta auko farat É—aya ba, irin wadda takan auka wa mugaye kamar hadiri , Ubangiji zai kiyaye ka. Ba zai bari ka faÉ—a cikin tarko ba

jinkirtawa yayi ya nisa tare da gyara zama , ya kai dubansa ga Youssouf wanda  fuskarsa tayi jaa idanun sa suka ciki-ciki .

Ya cigaba da cewa ,

" Kada ka yadda Mazinaciya ta sake ruɗar ka , kada kayi duba ga ƙilbasar ta ko kuwa daɗi na daga kalmomin hilatar da suke kan harshenta.

   "Leɓunan matar wani, mai yiwuwa ne, su yi zaƙi kamar zuma, sumbace-sumbacenta kuma su fi man zaitun taushi , amma ka sani bayan an gama , duka ba abin da za ta bar maka sai baƙin ciki, da azaba , za ta gangara da kai zuwa lahira, hanyar da take bi hanyar mutuwa ce ba a kan hanyar rai take ba, tana ragaita nesa da hanyar, amma kai ba ka ankara ba ,

" kayi nesa da zina Youssoufa kada ka yarda ka sake kusanta kan ka da zina Idan kuwa ka ƙi girmamawar da ake yi maka za ta zama ta waɗansu , mazinata ba kome bane su face walaƙantattu ababen walaƙantarwa ,
    
      "Ka iya rungumar wuta a ƙirjinka sa'an nan ka ce ba za ta ƙone tufafinka ba? Ka iya tafiya a kan garwashi sa'an nan ka ce ƙafafunka ba za su ƙone ba? Haka yake da mutumin da ya kwana da matar wani , duk wanda ya aikata wannan, zai sha wahala .

"kuma ai a yanzu ka gani , ka ga bala'in dake cikin zina , kome na tsanani da ya sabko maka ka sani cewa kankarane na daga zunuban ka ,zunuban mutum tarko ne, komar zunubinsa ce take kama shi , kayi gaugawar tuba ga Allah kafin lokaci shi ƙure maka .

   Zuwa lokacin hawayene ke sauƙa a idanun Youssouf , nadama marar iyaka ta sabko masa , daga can ya tsinkayi muryar Maimataba yana sake cewa ,
   " ina ka baro ɗiyar mutane da kake amre ?
    Muryarsa na rawa yace
   "ta tafi ƙasar su , kouma a yau Umma tai oumarni da na sau amren ta , zan sake ta Ranka shi daɗe ,

ÆŠan murmushi Maimartaba yayi kafin yace ,
    "mata sai abar su da lamarin su na ƙarancin hikima da tunani , anya ana gyaran ɓarna da ɓarna ?  Tafeeda ya gwada muna duk wasu shaidu na ɗaurin Amren ku , mun kuma gamsu da su ,

" dan haka baka sau amren matarka ba Youssouf ,  yi aminci ga matarka, ka ƙaunace ta , ka amro ta ne domin kana ƙaunar ta Alhalin kana da damar hakka , kai Mijin mataye ne ,

"Saboda haka ka yi farin ciki tare da matarka, ka yi murna da budurwa da ka auro, kyakkyawa mai kyan gani kamar barewa , ka bari kyanta ya ɗau hankalinka, daga ɗauke gani bisa matayen banza ,  Bari ƙaunarta ta kewaye ka , daga kwaɗayin macen titi , ƙwarai kana da damar haka ita halaliyar ka ce ,

  Wani irin sanyin daɗi ne ya fara tsartuwa a zuciyar Youssouf sai ya ɗago kansa kamar wani soko-soko yana duban Maimartaba da kokonto ko kunnuwansa gaskiya suka jiye masa ? 

  Ɗorawa Maimartaba yayi da cigaba da cewa ,

      " Amma ka tsahirta har abubuwa su dai-daita Mahaifiyarka kuma ta sabko daga fushin ta daga nan sai ka tafi ka zo da matar ka , mafi girman lamari a gaba ka tsaida adalci  a tsakanin Matayen ka babu shakka Allah yana farin-ciki da adalai .

   Youssouf a lokacin ji yayi kamar ya tashi ya sungumi Maimartaba ya shiga shilla shi sama yana chafewa saboda tsabar daɗi da zumuɗi ,

   " Nagode ranka shi daɗe, Nagode , nagode , nagode  kawai yake ta maimaitawa ,

  " Youssouf kada ka manta kalmomin da na furta su gare ka zasu inganta halinka, su zama kayan ado kamar kyakkyawan rawani a kanka, ko kyakkyawan abin wuya a wuyanka, don su ƙara maka kyau ,
    "Ban manta ba ranka shi daɗe , Allah shi saka da  Alheri Ranka shi daɗe ,

   Gyaɗa kai maimartaba yayi

" kana iya tafiya ga iyalin ka .

    " to na barka lafiya ranka ya dade mu kwana lafiya .

  Da tarin farin-ciki ya nufi sashin sa , da sassarfa ya shiga falon Siyama wacce ta ɗau kwalliya cikin ƙananun kaya riga da siket , jajaye da suka amshi fatar jikin ta mai matsakaicin haske.

Da mamakin ganin sa a shiyarta da daren nan , Alhalin kuma yau ɗakin Gimbiya yake kwana , ta miƙe tsaye tana masa sannu da zuwa ,
Da sassarfa ya taka ya isa gareta ya rungumeta tsam a jikinsa yana shaƙar ƙamshinta mai sanyin daɗi , shafa bayanta ya yi a kunnenta ya ce da ita , 
    " ki tayani farin-ciki ƙamnata Maimartaba ya yarda da aurena da Fatima , har ma ya min iznin nan ba da jimawa ba na tai na zo da itta , kwanan nan za ki ga ƙamnar ki .

Murmushin yaƙe tayi tana rintse ido , muryar ta da ɗan rawa tace ,
   " Alhamdulillah , Madallah da adali mai yawaita Adalci da kyautayi , nayi maka murna Biyamuraɗin maraɗawa ,
  Zare jikinta tayi tana ƙin haɗa ido da shi saboda ƙwallar da cika taf a ƙwarmin idanun ta tana daf da kwaranyowa .

  " mu tai ka ci abinci
  ta ce da shi tana jaan hannuwan sa ,

Tare suka ƙarasa gaban teburin cin abincin da yake cike taf da kayan cimaka na alfarma .

***

Zuwa lokacin Gimbiya Maimounatu ta kai maƙura wajen shaƙar baƙin-ciki , jin ya zo ya yini a gidan bai ko neme ta ba bayan irin laifin da ya aikata mai muni .

Ta kasa zama sai kai kawo take , gaba ɗaya yau mummunar zuciyar ta ta ƙeƙeshe ita ke jagorar ta ,

   Ko ƙwalliyar da ta saba yi domin taryarsa yau ta gaza , saƙa take da warwara , a ganin ta abunda yayi mata iyaka ne a cin fuska dan haka ta ɗau alwashin cimma manufarta a yau .

Duban ta ta mayar ga gnala wacce ita ce ta zo mata da labarin sake shigowar Yarima Youssouf gidan da sake shigar sa sashin Siyama .

  Da kaushin murya tace ,
   Gnala ,
   " na'am gimbiyar matar yari...
Chapter 198 · 0% Book details