← Book details Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 221 OF 269

Sashe 221

Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

" Saratu ki dakata daga waÉ—annan maganganu naki marasa tushe da makama , shi wawa bai san zuru ba sai ya tsinka , ki sani cewa duk wasu kaidi da makirce-makice hadi da ja'iba da ta'annakin da kike bibiyata da zuri'a ta da shi ina sane , ina sane nasan kome tun kafin yau , na yi miki shiru ne saboda nasan shi munahinci dodo shike , muguntar mutum kuma ita ke kawo hallakar sa har inda yayi zaune yana kitsa sharri, sannan akwai ranar da hadari zai taso tare da guguwar da zata wargaza mugaye .

Cikin tsakar idanun Hajiya Mama da ta tsare ta da ido ta kai duba suka yi musayan kallo ,
ÆŠan guntun murmushi tayi kafin ta cigaba da cewa ,

"Saratu kika ce akwai aibu cikin tsantsame zuri'a ? To ai rashin tsantsame zuri'a yasa kin ka kawo matsayin da kike bisan sa a yau , rashin tsantsame zuri'a yasa kin ka zama muguwar uwa mai kitsa sharri , Matar kirki 'yar Nasaba da ita Miji ke fariya yana ado da ita tamkar rigar silki , amma Annamimiya mai haɗa bakin wuta a tsakal gida ita ke saka shi cikin ɗimuwa ta dauwamar masa da shiga kunya da baƙin-cikin da har abada zai kasa samun farin-ciki da ita .

" Ya isa Hajiya Safiyya dan na tako na zou shiyar ki ba shi zai baki damar da za ki ci mutunci na ba , Hajiya Safiyya babu yadda za ki iya da ni , banbancin nasaba da ki ka É—au shekaru kina É—aga shi sama kina tutiya da shi bai isa ya sauya mana daidaituwar matsayi ba a cikin gidan nan kuma ko kin ki ko kin so Inkiya ta ita ce Gimbiya Matar Sarki .

Tana huci ta miƙe tsaye ta fara taku tace " na zo nan ne dan na sanar da ke ki sa a gaugauta sakar min ɗa ya dawo saboda ina da masaniyar ke kika sa aka cigaba da garƙame shi ba tare da ya aikata laifin kome ba .

A tsakanin kwanakin da suka biyo baya Bilal da Ubbo tare da Maigidan ta suka tafi india , washegarin tafiyar su kuma Tafeeda shima ya juyo , saboda yanayin aikin sa da bazai bar shi ya cigaba da zama ba a can .

Bayan an gama zaman fada da Maimartaba ya tsawatar akan hana cigaba da batun abunda ya faru da Youssoufa , aka fuskanci abunda ya shafi fada da al'amuran ta kaÉ—ai ,

A daren ranar misalin ƙarfe takwas saƙon ƙira daga Maimartaba ya riski Tafeeda , babu ɓata lokaci ya cimma turakar Maimartaba ƙarƙashin jagorancin jakadiya .

Bayan ganawar da bata wuce mintoci talatin ba Maimartaba ya masa iznin tafiys bayan ya samu duk wasu bayanan da yake son samu daga wajen sa .

Duk da cewa Hajiya Mama ce take da turaka a ranar amma kasantuwar buƙatar ganawa da Hajiya Safiya ya taso yasa Maimartaba aika jakadiya ta masa ƙiran Hajiya Umma .

Lokacin da saƙon ƙiran ya samu Hajiya Umma tayi mamakin Ƙiran nasa sai kuma ta cika da fargabar ko dai wani lamarin ya afku ?

Batun da Maimartaba ya zo mata da shi a lokacin da ta isa turakar sa ya busar mata da maƙwallato , da wani irin yanayi cikin muryar ta tace ,

" Ranka ya dade amma sai nake ganin rashin dacewar Yarima ya cigaba da riƙon amren ɗiyar nan ta Nigeria , wacce ba'a ma kai ga sanin matsayi da tushen ta ba , Ranka ya dade a duba wannan lamarin ayi duba da yadda wannan ɗiya ta agades tazo da ha'inci ita wacce ma take da tsarkin Nasaba ɗiyar girma , ina ga kouma ita wannan da take tsintattar mage a yadda labari ya iske mu ko a can Nigeria basu da wata nasabar da za'a iya haɗa jini da su , ba'a ma san dangin su ba 'Yan Gudun Hijira ne kaddarar rayuwa tare da maƙirci irin na maƙiyan mu ne kawai ya haɗo kasantuwar su tare da ɗan mu me zai hana kawai a raba wannan Amren ?

Cikin tsanaki Maimartaba yake kallon ta har ta gama zantukan ta tayi shiru ,
"Safiyya , ya ƙira sunan ta yana gyara zaman gilashin ƙara karfin gani idon sa .

" Na'am , ranka ya dade ta amsa tana mai kaucewa haÉ—uwar idanun su , cigaba yayi da cewa
"Yanzou ashe abunda ya faru bai isa zamar miki ishara ba ? Bai isa miki nuni da cewa kyaun nasaba bai nuni da kyaun ɗabi'a da cikar mutuntaka ba ? Bai isa sanar da ke cewa halin ƙwarai baiwa ce da ubangiji ka iya bayarwa ga bayinsa tsakanin talakawa da masu kuɗi , masu mulki da bayun su Iyaye kouma su taya wajen ƙarin gyaruwar halayya da taimakon gwargadon irin kyaun tarbiyyar da suka yiwa ɗiyan su .

"Nasaba ba ita ke tsalkake mutum daga aikata halin banza ba , shi halin Mutum mallakin sa ne daga lokacin faruwar halittar sa da bai da wata alaƙa da wata Nasaba ko ni'imar rayuwar da zai zo ya taras nan duniya .

" Domin ɗiyar Nasaba tayi zalunci bai nufin ɗiyar ƙananun mutane tayi fiye da munin abunda ta aikata mai yiwuwa ne ita ɗiyar talakawan ta bayar da mamaki wajen zuwa da ɗabi'u mafiya kyau wajen ƙwaiƙwayo , wannan ɓangare ne na baiwar Ubangiji kamar yadda na shaida miki , dan haka umarni nake bayarwa kan a tai a zo da ɗiyar da Youssoufa ke amre dagga Nigeria ta kasance ƙarƙashin kulawar mu kafin dawowar Mijinta hakan shine zai nuna cikar ƙima da darajar mu , sam ba dattaku irin namu bane mu bar ɗiyar mutane dauke da amren ɗan mu can a ƙasar su batare da sanin halin da take ciki ba , ba'a kuma sanar da ita halin da Mijinta ke a ciki ba da hakkinta ne ta sani .

Hajiya Safiyya da tayi zugum tana jin sabon damuwa na mamayar ta Allah ya sani bata son cigaba da kasancewar yarinyar nan a matsayin surukar ta ita da son ran ta ne Siyama kaɗai ce zata cigaba da zama a matsayin matar auren Youssoufa , ta ƙuta sannan tace ,
" Ranka ya daÉ—e a halin da Youssoufa yake ciki yanzou babu tabbacin ko yana son cigaba da zama da yarinyar nan tunda ka ga kou Siyama ai....

" Safiyya ta ban san ki da gardama ba kar kuma ki sakayo ta cikin ɗabi'un ki a yanzou , Youssoufa yana son matar sa duk kouma tunane-tunanen da kike yi kiyi watsi da su domin zai zo miki da saɓanin su , dan haka kamar yadda nace a shirya tafiya a zaɓi mutanen da suka dace cikin matayen da zasu tai Nigeria dole ya zama da na jiki ne sosai zasu yi tahiyar nan , sannan a tanadi kome da ya dace domin zouwa tahowa da ita , a yi kome cikin girma idan ta iso a mata masauƙi a sashin ki kussa da ke daɗa ita ɗin ai ɗiya ce Mai girma a wajen mu , Waziri shi zai jagoranci tafiyar tare da shi da Ɗan Malikin Maradi da wasu zaɓɓaɓu amintattun fada.

Kallon ba yadda zan yi Hajiya Umma take bin Maimartaba da shi har ya gama jawabinsa da cikin muryarsa ta fahimci a tsaurare yayi maganar cike da sautin umarta dan haka bata da wani zaɓi sai yin yadda yace , sai ta miƙe a hankali bayan ta ce " Ranka ya dade da yardar Allah yadda kace haka za'a yi .

MAIDUGURI-NIGERIA .

Fatima , ta ji ya ƙira sunan ta can a ƙasan maƙoshi ,
"Na'am ta amsa tana ɗago kan ta da ta kwantar a ƙirjin sa ,

" Ranar da duk za ki haihu tare zamu yi naƙuda kiyi rabi nima nayi rabi kin ji ko ?

Murmushi mai sauti tayi tana mayar da kanta ta kwantar "Daman ana yin haka ? Ta tambaye shi ,
"Nima ban sani ba Fatima , sabbada duk É—iyana biyu bana wajen lokacin haihuwar su , amma wannan ya furta hakan lokacin da yake kai hannun sa marar ta ya shafa , "tare zamu yi haihuwar sa , É—iyana ko É—ana zasu safko a hannuna idan macce ce kin san sunan wa zan sanya mata ?
A hankali ta girgiza kai yace, "Rahamatullah , sabadda haɗuwata da Mahaifiyar ta Rahama ce mai girma Allah shi yi min , Idan kouma ɗa Namiji ne ?, shiru yayi kaɗan , da yasa ta ɗago kan ta tana leƙen fuskar sa , wani irin farin-ciki kalamansa suka ɗarsa a ran ta ," dagaske yake ita tamkar Rahama ce a wajen sa ?
Sumbatar goshin ta yayi a hankali yace " na bar miki zaɓi Fatima ke za kiyi masa zaɓin sunan , wanne suna za ki sa masa ?

Hannun ta da yake kan ruwan jikin sa ta matsar ta lalubi hannun sa ta haɗe tafukan su waje guda kafin ta sarƙe ƴan yatsunsu cikin na juna kamar mai raɗa tace " Babana .

Hannun Yakaka da ta ji ya taɓa fuskar ta shiyasa tayi firgit tana kirkiro murmushin yaƙe , ganin ta ta mayar inda wasu ma'aurata dake zaune suke ta zuba soyayyar su Mijin sai tarairayar matar sa wacce take ɗauke da ƙaramin ciki yake yi kamar zai tayata ɗaukar cikin ita kuma sai zuba shagwaba take tana daɗa narke masa , wayam ta ga basa nan da alama sun shiga wajen likita .

tun zuwan su Asibitin da yau zata fara awu da Yakaka tare da Amnee suka rako ta Amnee ita tayi duk wasu kai kawon da bai cika wahala ba kasancewar Asibitin private ne yasa nan da nan ta buɗe mata file tare da biyan duk wasu kuɗaɗen da aka buƙata sannan aka turo su gurin likitan da zai dunga ganin ta .

mata Uku kawai suka tarar da a wajen , biyun tare suke da Mazajen su sai ita da wata mata wacce da gani ba haihuwar fari bace sune kaÉ—ai ba mazajen su a wajen .
Chapter 221 · 0% Book details