← Book details Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 226 OF 269

Sashe 226

Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Baki ɗaya fuskarta tayi jaa a take tana huci tayi ƙasa da murya kafin tace " To akuya sarkin naci ana ƙorar ki kina daɗa naniƙewa , shugabar 'yan rashin zuciya Miji bai damu da ke ba sai ke ce ke neman sa jarababba , to ƙwalelen ki ke da Doctor sai gani sai hange daga nesa-nesa dan kuwa zaman ki kenan a inda kike 'yar .....

Ƙit !

Ta ji Yakaka ta katse ƙiran ,

Daɓas ta zauna a bakin gadon baki ɗaya ranta ya cunkushe har wani raɗaɗi take ji a hancin ta kamar ta shaƙi barkono ," wannan jarababbiyar yarinyar watau har ƙiran Mijinta take yi ?

" Sofi waye ya ƙira ni naji kamar kin ɗaga wayar ?

Da sauri ta waiga kafin ta miƙe tsaye ta ƙarasa zuwa gaban shi inda yake tsaye yana goge kansa da towel ,

Tana zuwa ta karɓi towel ɗin ta shiga goge masa jiki , bata yarda sun haɗa ido ba fuskar ta babu walwala tace , " Akuya ce ta ƙira ka ? 🙄

"Akuya fa ?

Ya tambaye ta yana duban ta da mamaki ,

Cike da bagararwa ta kai hannun ta ƙirjin sa tana ɗan tsikarin sa tace " eh dan kukan akuya nake ta ji tunda na ɗaga wayar ina Hello , Hello , Hello . Ba'a cewa kome sai Kukan Akuya .

Jawota yayi ya haɗe tsakanin su , yana kallon cikin tsakar idon ta yace " Sofi baki fa da kirki a wasu lokutan nasan daga Office ne aka ƙirani , Ni yanzu muje ki bani abinci na ci yunwa nake Ji ina son na fita akwai wani waje muhimmi da nake son zuwa yau .

Kicin-kicin tayi da fuska jin cewar zai fita yasa ta sake jin tasowar ɓacin rai da ya ɗan fara lafa mata sanadin haɗuwar fatar jikin su .

Bai kula ɓacin ran ta ba yayi shirin sa cikin wani yadi mai ɗan nawi ruwan zuma ya fesa turare tare da ɗaura agogon sa sai lokacin ya juyo ya dube ta da take zaune a bakin gado ta kumbura suntum .

Fushinta bai wani taɓa masa rai ba yace " mu je ki bani abincin ba daɗewa zan yi ba zan dawo nima so nake na huta yau ɗaya .

Bayan ya ɗan cac-cakali Omelet da kidney Sauce ya ɗan kurɓi ruwan tea ya miƙe a gurguje ya mata sallama yana barin gidan .

Da fitar sa ta yi jaɓar ' akan kujera tunanin ƙiran wayar sa da Yakaka tayi ya bata tsoro , ita da ta saki baki ta zauna malumman ta sun ce mata an yiwa Yakaka da Hamza farraƙu to tayaya Yakaka ta iya samun damar ƙiran sa ? Kada dai ace asirin nan bai ci ta ba ?

Wani irin huci take yi lokaci guda ta tashi da gudu ta hau sama ɗakin ta ta shige laluben wayar ta , ya zama dole ta sabunta aikin ta .😂

***

Doctor Hamza kuwa yana fitowa hankali kwance ya dai-daita motar sa akan titi unguwar su Malama Maryam ya tasamma da bata kasance ɓaƙuwar unguwa a wajen sa ba , ya sha kai sofiya gidan ƙawar ta Samira .

Tsawon sati biyu da yayi yana bin duk wasu Matakai daki-daki domin tabbatar da zancen da Suleiman ya sanar da shi game da Yakaka gaskiya ne ko ba gaskiya ba ? Duk da cewa yana da tabbacin Suleiman ɗin ba zai masa ƙarya ba amma yana da buƙatar samun ƙwararan hujjoji ko dan ya wanke zargin ta daga ransa da hakan shine kaɗai zai ba shi damar samun nutsuwa tare da ita da zai iya rungumar ta hannu bibbiyu , tun usul ƙaunar ta bata tunbuƙe ba daga ransa girgiɗi kawai tayi da a yanzu kuma ta dawo ta tsaya chak da ƙafafun ta ta kuma shiga kaiwa duk wasu gaɓɓan jikin sa mamaya .

ASSALAMU ALAIƘUM MASU KARATU .

Da fatan duku kuna lafiya ? Sakamakon saƙonnin da nayi ta amsa daga masoya masu karatu kan taƙaice ƙarshen MHR da wasu ke ƙorafi wasu kuma suka nemi Alfarmar na ɗan sake jaan zaren labarin nayi dalla-dalla ko da kuwa ban yi filla-filla ba , hakan yasa na karɓi ƙorafi na kuma ɗan jaa kaɗan ba mai yawa ba da nan gaba kaɗan mu kan iya rufe bangon littafin mu adana shi Insha Allah

A ƙarshe ina godiya sosai da sosai ga dukkanin makaranta MHR na fili da na ɓoye daɗa nasan na ɓoyen sun ninka na filin yawa "ghosts readers barkar mu dai ina gaisuwa fa 😜❤nasan kuna tare da ni domin ina ganin inuwar ku , ko da kuwa baku bani tukuici ba .

Nagode.    [2/3, 9:34 PM] +234 803 083 8792: Mafari
( Hargitsin Rayuwa )

Umm'muaz

50

Lokacin da Doctor Hamza ya isa unguwar su Malama Maryam dai-dai layi da gidan da Doctor Suleiman ya kwatanta masa sai ya ga ashe ma ya taɓa sanin gidan duk kuwa da cewa da dare ya taɓa zuwa amma bai manta da yarinyar da ya taɓa taimakawa ba a wani dare ana ruwan sama babu shakka a ƙofar wannan gidan ya sauƙe ta .

Kasancewar ana haramar sallar Azahar a lokacin dan haka a masallacin da yake kusa da gidan nan yayi Sallah .

Bayan ya idar sai ya matsa ya miƙawa Liman hannu suka yi musabaha , nuni ya yi masa kafin ya ɗora masa bayanin gidan da ya zo , to amma kasancewar an sanar da shi matar tana da aure ya zama dole sai da iznin Mijinta zai gana da ita , tunda ba sanin juna suka taɓa yi ba dan haka yake son sanin Mijin ta da farko , a zahiri wata buƙata ce ta son samun wasu bayanai daga bakin Matar da ake ƙira Malama Maryam yasa shi tasowa musamman domin ganawa da ita .

Dan jim liman yayi yana sake nazarin Doctor Hamza , kafin yace " bawan Allah lafiya dai ko ? Ba dai wani al'amari bane marar daÉ—i ya auku da har yasa kake neman Malama Maryam ?

Da sauri Doctor Hamza ya girgiza kai kafin yace ' ah ah ba wani abu bane marar kyau , kawai tambayoyi nake so nayi mata akan wata É—alibar ta da ta koyar wacce aka ce daga baya ta zama kamar 'yar ta saboda kusanci da ta samu da ita , sunan yarinyar Amina .

Shiru Liman ya sake yi kafin yace 'Kana nufin Amina Mustapha Dilmari yarinya 'yar Maiduguri ?

" ita fa Malam .

"Allah sarki yarinyar kirki ce ai Amina , ta koma can garin su a halin yanzu har an aurar da ita sati biyu da suka wuce , Malama Maryam da kake nema ai Mata ta ce , kuma ita ce Malamar Amina tsawon shekaru Shida da suka yi tare , bari na shiga gida sai nayi mata bayani na haÉ—a ku , amma kafin nan zan so jin ko kai wane ne ? Kuma daga ina kake ?

Cike da jin daɗin ganin sauƙaƙuwar lamura Doctor Hamza yace " Malam ai ni ne Mijin Amina bayan haka kuma ni wan ta ne da muke 'ya'yan mata biyu .

" Masha Allah ka ce babban baƙo ne da mu , to Bismillah mana mu shiga daga cikin Falona kafin na yi mata magana .

Ganawar Doctor Hamza tare da Malama Maryam ya zo masa da wani irin sauyi mai girma da yake sauraren bayanan da take yi  masa game da baki ɗayan rayuwar da Yakaka tayi tare da ita har ma da wanda tayi gidan uwarɗakin ta samy baby da a farko su kayi zaton yayar ta ce , kafin daga baya lokacin da ta faɗa musu haƙiƙanin gaskiyar kome game da ita ,su gane cewa basu da wata alaƙa ta 'yan uwantaka .

" alaƙar ta da Samy Baby da duk irin Yaudarar da tayi mata . har yadda daga baya Samy baby take son tilasta ta shiga harkar banza amma ta ƙi yarda da hakan shine ya kawo sanadin komawar ta Maiduguri .

Nisawa Malama Maryam tayi tana murmushi ta cigaba da cewa " Abu mafi daÉ—i da yasa nake yin Alfahari da Amina shine jajircewar ta wajen neman ilmin addini fiye da na boko , Amina ta fara karatun addini bata kai ga sanin ayoyi bakwai na Suratul-Fatiha ba amma sai ga shi cikin shekaru shidda da Yarjewar Allah ta samu cikakkiyar kyakkyawar Haddar izif talatin .

" bata san yadda ake yin cikakkiyar Alwala ba a shekaru shidda baya a yanzu Amina daga kan farillai , sunnoni da mustahabbai har makruhi na alwala ta sani , haka kuma sharuɗɗan Sallar ta sun inganta ta kuma san yadda zata yi gyara ga Sallar ta idan ta ɓaci.

" Amina ta san baƙi , ta iya karatu da rubutun Arabic ta kuma samu tarin ilmi daga littatafan addini da hadisai masu inganci dan haka ta san dukkanin haƙoƙin Ubangiji dake kan ta .

" Alhamdulillah shine kawai abunda zance da Allah ya rataya min nawin tallafa mata ta hanyar samu ilmin addini , ya kuma bani ikon koyarda ita tare da ni da sauran Malaman da ta É—au ilmi a wajen su , nagodewa Allah da kafin barin ta wajena ta fita daga duhun jahilci .

"Halaye da É—abi'un Amina mafi rinjayen su masu kyau ne ababen koyi , tundaga lokacin da tasan irin tarin zunubin da yake cikin kuskuren da tayi na baya bata sake kwatanta aikata makamancin sa ba , tayi kyakkyawan tuba da irin sa ake son duk wani mumuni ya yi .

" babu shakka kayi sa'ar Mata , Allah ya ɗorar da zaman lafiya a tsakanin ku, a ƙarshe shawarata shine kayi ƙoƙarin ganin ta samu cigaban karatun ta na addini kamar yadda ta ke fata a koyaushe watarana ta haddace Alkur'ani Mai girma Dan Allah ka bata dama ka taya ta wajen samun cikar burin ta irin Amina sune Al'umma suke amfana da su .

" Ya Rabb lakal-Hamdu ,  Alhamdulillah , Masha Allah .

Doctor Hamza yake furta haka fuskar sa É—auke da wani irin annuri na farin-ciki , har wani irin zillo yake ji zuciyar sa na yi masa .
Chapter 226 · 0% Book details