Sashe 137
Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
 Umma zan tafi bakin aiki doumin an ƙira ni daga niamey bisa ga wani aiki na gouggawa da ya taso ,
Aiki ? Ba an baka houtu ba na tsawon sati gouda ?
Umma aikin mu na kare rayuka da dukiyoyin al'umma ne koyaushe ana iya ƙiran mu kuma a kowanne yanayi da lokaci , !
Shiru tayi tana nazarin sa , kafin ta jefo masa tambayar da ta sanya shi É—ago kai
Tare da siyama zaku tafi kou ?
Shiru yayi kafin ya tattaro ƙarfin halin da ya yi masa saura
   Niamey zan tafi ba dosso ba Umma , idan na dawo daga niamey zamu tafi dosso tare.
bata jaa ba tayi masa addu'o'i kamar yadda ta saba tare da ƴan nasihohi , ƙarshe ta sake tunasar da shi girman nawin da ke kan sa a yanzu , !
****
Tunda ya hau kujerar zaman sa a jirgin da zai É—aga da shi zuwa niamey ya zurfafa cikin tunani daki-daki ,
Da hantsi ya samu isa ƙofar gidan , kan layin shiru , da yake unguwar babu yawan mutane , ya cire ƙuɗin me taxi ya biya shi , ƙarasawa yayi jikin ƙofar gidan ya ƙwanƙwasa
Hajja wacce take tsakiyar sharar ƴar harabar gidan ta saurara da kyau ta tabbatar cewa gidan nasu ake bugu , ta ajiye tsintsiyar ta ƙaraso jikin ƙofar ta tambaya wanene ??
Hajja ni ne ,
  Ta shaida muryar sa dan haka ta zare sakatar ƙofar ya samu shigowa gidan , sai fara'a take masa tana lale marhabin da shi ,
  Shiga ciki Babban soja bari na ƙarasa ture ɗan wajen nan zan zo mu gaisa , sannu ka sha doguwar tafiye ince kwana kayi a hanya ?
Murmushi yayi ba tare da ya amsa mata ba ya sanya kai cikin gidan ,
Ƙiiii
  Ƙarar turo ƙofar sa ta sanya ta ɗago kan ta ta dubi sashin da ta ji motsi ,
  Hajja sannu da aiki !
Tace cikin Æ´ar muryar ta ,
Bai amsa ba saboda baki ɗaya hankalin sa da idanun sa na ga fuskar mama wacce take jingine da jikin falmata akan cinyar ta , su duk biyun suna fuskantar ,
Taku ya fara yi yana jin yadda shauƙin son ta ke ɗibar shi , da sassarfa ya ƙarasa gaban su ya tsugunna gami da kai hannun sa ya kama ƴan kafafun ta da suke sanye da ƴar safa ya sunkuyo da fuskar sa ya sumbata yana me rufe idanun sa da jin yadda ƙaunar ta ke sake ratsa shi tare da wata nutsuwa ta musamman , me yake ƙauna irin ta tsakanin ɗa da iyaye ƙarfi tare da tsafta ??.
Lokacin da ya É—ago kan sa falmata ta kawo hannunwan ta duk biyu ta É—ora akan fuskar sa , a hankali tayi yawo da hannuwan ta tana shafar fuskar sa da idanun sa ke rufe ,
Tamkar wuta ta jaa ta ta janye hannuwan ta da sauri , tana É—auke mama ta É—ora kan kafaÉ—ar ta ,
 Da farko tayi zaton hajja ce ta shigo, sanin cewa daga ita sai hajja a gidan .
Wa-waye ne ? Tace tana ƙoƙarin miƙewa ,
 Â
  Koma ki zauna Fatima ni ne ,
Ya kai hannu yana ƙoƙarin karɓar mama ,
Ta gane muryar sa dan haka ta sakar masa mama a hankali , tana dai-daita numfashin ta da firgici ya sa shi hargitsewa ,
Yana karɓar ta yayi mazauni akan ɗaya daga cikin kujerun wajen ba tare da ya janye idanun sa daga kan ta ba ya shiga sumbatar kumatu zuwa goshin ta ,
Bai ko ji gaisuwar da falmata wacce ta zauna daga ƙasa a gefe take yi masa ba ,
  ita ma shiru tayi ganin bai amsa ba
Shigowar hajja ya sanya shi rungume mama a jikin sa suna gaisawa shi da hajja ,
   Soja garin nan na ku kuwa ya karɓe ka , ka ga yadda kayi fes da kai kana ƙyallin fuska sai ka ce sabon ango ? Ah lalle miyar umma da zaƙi ta sa kayi shar da kai duk wannan hautsinewar sojin sun kau , ke Fatima kin kuwa gaishe da maigidan naki ??
Na gaishe shi hajja ,
To ban ga kin kawo masa ruwa ba , ?
Zata miƙe ya dakatar da ita ƙyale ta hajja ita da take da larura baza ta iya aike ba !
Ƴar dariya hajja tayi
Zata iya Babban soja ai matar ta ka ba dama akwai lura da kaifin ƙwaƙwalwa saurin gane waje ne da ita , ka ga dai ba mu rufa wata guda ba a gidan nan amma ta haddace kusan muhallin kome da kome da yake cikin gidan nan ,
ita da kan ta take zuwa ta É—au ruwa a firiza ko ta je kitchen ta haÉ—a madarar mama , kullum addu'a nake mata Allah shi kawo mata waraka .
ÆŠan murmushi yayi yana duban falmata wacce ta koma ta zauna ta juyar da kan ta gefe ,
Kalaman hajja sun tuno masa da abunda ya so mantawa , watau kai falmata asibiti tare da samar mata gurbin karatu ,
Ya zama dole yayi duk wani abunda zai iya yi gurin kyautata rayuwar falmata ko domin ya samu girman laifin sa ya ragu a wajen Allah .
Hajja ku shirya zamou tafi babban hospitalisé a duba lafiyar idanun fatima yanzu. !
  To to yanzu kuwa , falmata tashi ki shirya bari nima na ɗan kintsa , !
Niamey national hospitalisé nan suka je , inda basu wani ɗau dogon lokaci ba suka ga ƙwararren ophthalmologist , bayan haske-hasken da tarin tambayoyin da yayi mata akan idanun nata , a ɗakin gwaje-gwaje .
Suka dawo ofishin sa inda youssouf ke jiran su , bayani ya soma yi masa daki-daki
A sakamakon binciken da nayi a zahiri ban hango wata cuta ba a idanun nata sai dai raunin ƙwayar idanun nata watau ainahin jijiyoyin idanun suna da rauni , a tambayoyin da nayi mata nayi ƙoƙarin sanin tayaya ta fara samun rashin gani ko da shi aka haife ta ? amma sai ta shaida min bata da masaniya akan mafarin samuwar rashin gsnin ta ,
A takaice cikin binciken da muka gudanar da kuma sakamakon amsoshin da ta bayar yayin yi mata gwaji da akwai yiyuwar dawowar wani kaso daga cikin ganin ta idan har za'a samu ƙwararrun kayayyakin aikin da zasu taimaka wajen dawo da ganin nata ,
Sai dai a halin yanzu bamu da waɗannan kayayyakin a nan gida niger da sauran ƙasashe masu tasowa , sai a manyan ƙasashen duniya da suka yi fice wajen samun ingantattun asibitoci masu isasssun kayayyakin aiki tare da ƙwararrun likitoci ,
Dan haka a yanzu abunda zamu iya yi mata kaɗai shine zamu bata magungunan da zasu iya taimakawa wajen bada kariya ga idanun nata daga kamuwa da wasu cututtukan da zasu iya kassara sauran ƙarfin jijiyar idanun da kuma hana idanun yin ciwo ƙaiƙayi da zubar ruwa ,
  Da fatan kun fahimce ni ?
Mun fahimta Doctor mun goude zamu dawou gare ka idan buƙatar neman taimakou game da asibitin da ya kamata a kai ta a wata ƙasar ya tasou mun goude ƙwarai Madallah .
Washegarin ranar Biyamuradi bai zauna ba , ya shiga binciken makarantar makafi me kyau da yake son ya kai falmata ta fara karatu kafin lokacin da zai sake yunƙuri me ƙarfi akan lafiyar idanun nata a karo na biyu .
Association Nationale Pour la promotion des aveuglés , nan ne inda ya ji gamsuwar sa akan ya kai falmata nan ta fara ɗaukar darasi , wacce jibiya ce ta koyar da makafi tare da basu tallafi me tushe daga ƙasar amurka , da ta tanadi ƙwararrun malaman makafi ,
Cikin sati guda yayi mata rajista da duk wasu abubuwan da ya kamata , ya samar mata da direba bayan ya sa an kawo masa ɗaya daga cikin motocin sa da suke maradi ya danƙa makullin ga hajja wacce take cike da farin cikin wannan cigaba da falmata zata samu a rayuwa .
Ranar da zai bar garin zuwa bakin aikin sa jahar dosso , ya yi musu sayayyar kayan abinci da abubuwan da zasu iya buƙata tare da ƴar ƙaramar waya me sauƙin amfani ya ba wa hajja bayan ya zuba mata lambobin sa a wayar ya adana ta su a ta shi wayar ,
Suna zaune a falo yana musu sallama akan yau zai koma bakin aikin sa , sai kuma zuwan ƙarshen wani watan zai komo
Godiya me tarin yawa hajja ta yi masa ,
  Ya amsa tare da waiwayawa sashin falmata da take ta faman lila mama akan ɗan lilon ta wanda baban ta ya sayo mata su tarkacen kayan wasan yara iri-iri har da wanda ya fi ƙarfin shekarun ta , tun daga kan lilon yara , kekunan koyon zama har zuwa ƴar mota ta yara da ƙananun kayan wasanni irin na ƴaƴan gata na sosai , bayan suturun da ya daɗa jibgo mata.
  Fatima baki da wata matsala kou ?
Shiru tayi tana É—an lila mama a hankali ,
 Falmata hala kin samu kurunta ? Kina jin Babban soja na magana kin yi shiru ? Uhum yau ni naga abunda ya shallake tunani na ,
   Babu kome kawai ina son unmh
  Uhum ina jin ki me kike so ??
A kaini makaranta
 Ai na sanya ki makaranta fatima sati me kamawa zaki fara zouwa ,!
Na islamiya ? Ina so a cigaba da koya min karatun addini ma ,!
Toh babu damouwa idan Allah ya yarda zan bincika a samu me koyar da ke na Islama ma ,
Akwai wata damouwa bayan wannan ?
Daman ka gaya musu zan dunga zuwa da mama makarantar ko ?
Aiki ? Ba an baka houtu ba na tsawon sati gouda ?
Umma aikin mu na kare rayuka da dukiyoyin al'umma ne koyaushe ana iya ƙiran mu kuma a kowanne yanayi da lokaci , !
Shiru tayi tana nazarin sa , kafin ta jefo masa tambayar da ta sanya shi É—ago kai
Tare da siyama zaku tafi kou ?
Shiru yayi kafin ya tattaro ƙarfin halin da ya yi masa saura
   Niamey zan tafi ba dosso ba Umma , idan na dawo daga niamey zamu tafi dosso tare.
bata jaa ba tayi masa addu'o'i kamar yadda ta saba tare da ƴan nasihohi , ƙarshe ta sake tunasar da shi girman nawin da ke kan sa a yanzu , !
****
Tunda ya hau kujerar zaman sa a jirgin da zai É—aga da shi zuwa niamey ya zurfafa cikin tunani daki-daki ,
Da hantsi ya samu isa ƙofar gidan , kan layin shiru , da yake unguwar babu yawan mutane , ya cire ƙuɗin me taxi ya biya shi , ƙarasawa yayi jikin ƙofar gidan ya ƙwanƙwasa
Hajja wacce take tsakiyar sharar ƴar harabar gidan ta saurara da kyau ta tabbatar cewa gidan nasu ake bugu , ta ajiye tsintsiyar ta ƙaraso jikin ƙofar ta tambaya wanene ??
Hajja ni ne ,
  Ta shaida muryar sa dan haka ta zare sakatar ƙofar ya samu shigowa gidan , sai fara'a take masa tana lale marhabin da shi ,
  Shiga ciki Babban soja bari na ƙarasa ture ɗan wajen nan zan zo mu gaisa , sannu ka sha doguwar tafiye ince kwana kayi a hanya ?
Murmushi yayi ba tare da ya amsa mata ba ya sanya kai cikin gidan ,
Ƙiiii
  Ƙarar turo ƙofar sa ta sanya ta ɗago kan ta ta dubi sashin da ta ji motsi ,
  Hajja sannu da aiki !
Tace cikin Æ´ar muryar ta ,
Bai amsa ba saboda baki ɗaya hankalin sa da idanun sa na ga fuskar mama wacce take jingine da jikin falmata akan cinyar ta , su duk biyun suna fuskantar ,
Taku ya fara yi yana jin yadda shauƙin son ta ke ɗibar shi , da sassarfa ya ƙarasa gaban su ya tsugunna gami da kai hannun sa ya kama ƴan kafafun ta da suke sanye da ƴar safa ya sunkuyo da fuskar sa ya sumbata yana me rufe idanun sa da jin yadda ƙaunar ta ke sake ratsa shi tare da wata nutsuwa ta musamman , me yake ƙauna irin ta tsakanin ɗa da iyaye ƙarfi tare da tsafta ??.
Lokacin da ya É—ago kan sa falmata ta kawo hannunwan ta duk biyu ta É—ora akan fuskar sa , a hankali tayi yawo da hannuwan ta tana shafar fuskar sa da idanun sa ke rufe ,
Tamkar wuta ta jaa ta ta janye hannuwan ta da sauri , tana É—auke mama ta É—ora kan kafaÉ—ar ta ,
 Da farko tayi zaton hajja ce ta shigo, sanin cewa daga ita sai hajja a gidan .
Wa-waye ne ? Tace tana ƙoƙarin miƙewa ,
 Â
  Koma ki zauna Fatima ni ne ,
Ya kai hannu yana ƙoƙarin karɓar mama ,
Ta gane muryar sa dan haka ta sakar masa mama a hankali , tana dai-daita numfashin ta da firgici ya sa shi hargitsewa ,
Yana karɓar ta yayi mazauni akan ɗaya daga cikin kujerun wajen ba tare da ya janye idanun sa daga kan ta ba ya shiga sumbatar kumatu zuwa goshin ta ,
Bai ko ji gaisuwar da falmata wacce ta zauna daga ƙasa a gefe take yi masa ba ,
  ita ma shiru tayi ganin bai amsa ba
Shigowar hajja ya sanya shi rungume mama a jikin sa suna gaisawa shi da hajja ,
   Soja garin nan na ku kuwa ya karɓe ka , ka ga yadda kayi fes da kai kana ƙyallin fuska sai ka ce sabon ango ? Ah lalle miyar umma da zaƙi ta sa kayi shar da kai duk wannan hautsinewar sojin sun kau , ke Fatima kin kuwa gaishe da maigidan naki ??
Na gaishe shi hajja ,
To ban ga kin kawo masa ruwa ba , ?
Zata miƙe ya dakatar da ita ƙyale ta hajja ita da take da larura baza ta iya aike ba !
Ƴar dariya hajja tayi
Zata iya Babban soja ai matar ta ka ba dama akwai lura da kaifin ƙwaƙwalwa saurin gane waje ne da ita , ka ga dai ba mu rufa wata guda ba a gidan nan amma ta haddace kusan muhallin kome da kome da yake cikin gidan nan ,
ita da kan ta take zuwa ta É—au ruwa a firiza ko ta je kitchen ta haÉ—a madarar mama , kullum addu'a nake mata Allah shi kawo mata waraka .
ÆŠan murmushi yayi yana duban falmata wacce ta koma ta zauna ta juyar da kan ta gefe ,
Kalaman hajja sun tuno masa da abunda ya so mantawa , watau kai falmata asibiti tare da samar mata gurbin karatu ,
Ya zama dole yayi duk wani abunda zai iya yi gurin kyautata rayuwar falmata ko domin ya samu girman laifin sa ya ragu a wajen Allah .
Hajja ku shirya zamou tafi babban hospitalisé a duba lafiyar idanun fatima yanzu. !
  To to yanzu kuwa , falmata tashi ki shirya bari nima na ɗan kintsa , !
Niamey national hospitalisé nan suka je , inda basu wani ɗau dogon lokaci ba suka ga ƙwararren ophthalmologist , bayan haske-hasken da tarin tambayoyin da yayi mata akan idanun nata , a ɗakin gwaje-gwaje .
Suka dawo ofishin sa inda youssouf ke jiran su , bayani ya soma yi masa daki-daki
A sakamakon binciken da nayi a zahiri ban hango wata cuta ba a idanun nata sai dai raunin ƙwayar idanun nata watau ainahin jijiyoyin idanun suna da rauni , a tambayoyin da nayi mata nayi ƙoƙarin sanin tayaya ta fara samun rashin gani ko da shi aka haife ta ? amma sai ta shaida min bata da masaniya akan mafarin samuwar rashin gsnin ta ,
A takaice cikin binciken da muka gudanar da kuma sakamakon amsoshin da ta bayar yayin yi mata gwaji da akwai yiyuwar dawowar wani kaso daga cikin ganin ta idan har za'a samu ƙwararrun kayayyakin aikin da zasu taimaka wajen dawo da ganin nata ,
Sai dai a halin yanzu bamu da waɗannan kayayyakin a nan gida niger da sauran ƙasashe masu tasowa , sai a manyan ƙasashen duniya da suka yi fice wajen samun ingantattun asibitoci masu isasssun kayayyakin aiki tare da ƙwararrun likitoci ,
Dan haka a yanzu abunda zamu iya yi mata kaɗai shine zamu bata magungunan da zasu iya taimakawa wajen bada kariya ga idanun nata daga kamuwa da wasu cututtukan da zasu iya kassara sauran ƙarfin jijiyar idanun da kuma hana idanun yin ciwo ƙaiƙayi da zubar ruwa ,
  Da fatan kun fahimce ni ?
Mun fahimta Doctor mun goude zamu dawou gare ka idan buƙatar neman taimakou game da asibitin da ya kamata a kai ta a wata ƙasar ya tasou mun goude ƙwarai Madallah .
Washegarin ranar Biyamuradi bai zauna ba , ya shiga binciken makarantar makafi me kyau da yake son ya kai falmata ta fara karatu kafin lokacin da zai sake yunƙuri me ƙarfi akan lafiyar idanun nata a karo na biyu .
Association Nationale Pour la promotion des aveuglés , nan ne inda ya ji gamsuwar sa akan ya kai falmata nan ta fara ɗaukar darasi , wacce jibiya ce ta koyar da makafi tare da basu tallafi me tushe daga ƙasar amurka , da ta tanadi ƙwararrun malaman makafi ,
Cikin sati guda yayi mata rajista da duk wasu abubuwan da ya kamata , ya samar mata da direba bayan ya sa an kawo masa ɗaya daga cikin motocin sa da suke maradi ya danƙa makullin ga hajja wacce take cike da farin cikin wannan cigaba da falmata zata samu a rayuwa .
Ranar da zai bar garin zuwa bakin aikin sa jahar dosso , ya yi musu sayayyar kayan abinci da abubuwan da zasu iya buƙata tare da ƴar ƙaramar waya me sauƙin amfani ya ba wa hajja bayan ya zuba mata lambobin sa a wayar ya adana ta su a ta shi wayar ,
Suna zaune a falo yana musu sallama akan yau zai koma bakin aikin sa , sai kuma zuwan ƙarshen wani watan zai komo
Godiya me tarin yawa hajja ta yi masa ,
  Ya amsa tare da waiwayawa sashin falmata da take ta faman lila mama akan ɗan lilon ta wanda baban ta ya sayo mata su tarkacen kayan wasan yara iri-iri har da wanda ya fi ƙarfin shekarun ta , tun daga kan lilon yara , kekunan koyon zama har zuwa ƴar mota ta yara da ƙananun kayan wasanni irin na ƴaƴan gata na sosai , bayan suturun da ya daɗa jibgo mata.
  Fatima baki da wata matsala kou ?
Shiru tayi tana É—an lila mama a hankali ,
 Falmata hala kin samu kurunta ? Kina jin Babban soja na magana kin yi shiru ? Uhum yau ni naga abunda ya shallake tunani na ,
   Babu kome kawai ina son unmh
  Uhum ina jin ki me kike so ??
A kaini makaranta
 Ai na sanya ki makaranta fatima sati me kamawa zaki fara zouwa ,!
Na islamiya ? Ina so a cigaba da koya min karatun addini ma ,!
Toh babu damouwa idan Allah ya yarda zan bincika a samu me koyar da ke na Islama ma ,
Akwai wata damouwa bayan wannan ?
Daman ka gaya musu zan dunga zuwa da mama makarantar ko ?