Sashe 247
Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da sauri Doctor Hamza ya katse ta lokacin da yake sakin hannun Yakaka yace "Sofia na jima ban ji daddaɗan girki irin wannan ba ba domin Amnee kar ta hukunta ni ba zan ce ma ban taɓa cin basise mai daɗin wannan ba Sofi ki koyi girki ke ma zan ji iri..
Taɓe baki Sofia tayi tana hararar bayan Yakaka wacce ta riga ta juya tana barin wajen zuwa ɗaki kafin ta dawo da ganin ta kan Doctor Hamza .
Fuskar sa a É—aure yace "na faÉ—a miki ki daina neman fitina hakan ba kome zai jawo miki ba illa raini yarinyar nan dai a haife ma kin kusa haihuwar ta.
Kamar an soke ta da tsinin mashi haka Sofia ta ji , "ita zai ce ta haifi Yakaka ?
ƙanƙance ido tayi zata fara jaraba yayi wucewar sa cikin ɗaga taku yana barin falon ran sa cike taf da jin haushin korar masa Wafaa da tayi bata bari sun yi sallama ta masa rakiya ba .
Ta jima a tsaye a wajen tana rarrashin zuciyar ta da take ingizata akan ta je ta yiwa Yakaka dukan tsiya idan ya dawo ya ga banbancin shekarun a zahirance '
Sai dai ɗaya ɓarin zuciyar ta da yake cike da tsoron abun da hakan zai jawo ya hana ta aikatawa.
Sai da ta furzar da wata iska mai zafi sannan ta juya ta nufi É—akin da take É—aure Sam .
Yana kwance magashiyan kamar gawa , ƙafar ta tasa ta haure shi amma bai motsa ba " Dan ubanka kai ma ka tashi haka kaje kayi aikin da na kawo ka domin yi , ni inaga wannan maganin ma kamar ya maka ƙarfi yau ba zan baka shi ba .
Yakaka wacce har ta shiga wanka ta tuno da abincin ta na rana da ta ɓoye a kitchen cikin dabarar da take son yi , dan haka ta ɗaura towel ta zura hijabin ta ta murɗa ƙofar ta fito sai da tayi dube-dube ta samu tabbacin Sofia bata nan sannan da sassarfa ta tafi kitchen ta ɗauko sauran Basise da pancake da ta juye a warmer ta rufe ta nufo ɗaki.
zuwan ta tsakiyar falon yazo dai-dai da fitowar Sofia jaye da karen ta da yake ta turjewa yana wani É—an kuka .
Kallon-kallo suka yi a tsorace Yakaka ta jaa baya tana neman hanyar gudu cikin daƙiƙu kaɗan Sofia ta fahimci abunda Yakaka take shirin yi .
Dan haka ta zaburo bayan ta saki karen, da ganin haka Yakaka ta zuba a guje ta faɗa ɗaki da bata nesa da shi sosai tana shiga ta dire warmer ta danna ƙofar ta murza key bayan ta kulle ta zare shi daga jikin ƙofar dai-dai da ƙarasowar Sofia .
Wani irin duka Sofia ta kaiwa ƙofar kamar wacce ta sha giya ta shiga ƙundume-ƙundumen zagi tana cewa sai ta ga bayan Yakaka .
Yakaka wacce take jingine da jikin ƙofar daga ƙasa da ta zame ta zauna ji tayi hawaye na sauƙa a idanun ta wacce irin masifa ce wannan ?
"Ai kin kulle ƙofa a banza ki jira zan nuna miki iyakar ki zan nuna miki cewa nan gidana ne da baki isa min shamaƙi da wani ɓangare a cikin sa ba.
Tana jin lokacin da ta juya ta bar wajen bayan ta gama faɗin haka , ajiyar zuciya tayi ta miƙe tana ɗauke warmer ɗin daga wajen ta ajiye a gefen gado ,
Duk da ran ta na mata ciwo da irin yadda take rayuwar rashin Æ´anci amma ta ji daÉ—i da yau Sofia ba zata samu nasarar turo mata kare kamar yadda ta É—au alwashi ba ita daman ko babu kare a gidan ma yinin falo ba nata bane muddin Sofi na shawagi a gidan .
Wanka ta shiga ta ƙarasa ta kusa fitowa ta ji kamar an buɗe ƙofar an shigo ta ɗan kasa kunne bata ji motsi ba sai dai ƙarar rufe ƙofar da ta sake ji yasa a tsorace ta ɗauraye jikin ta ta fito .
Abun da ta gani yasa numfashin ta yin gargada 'Sam ne Sofia ta sake kawo mata shi kenan tana da makullin É—akin ? Yau ma so take tayi yini makamancin na jiya ?
Wani irin daskarewa take ji zuciyar ta na yi tsanar Sofi na ratsa kowanne lungu da saƙo na ran ta "sofia wace irin Azzaluma ce haka ? Da gaske idan bata bar gidan ba watarana Sofi zata kashe ta .
Kallon karen take yi tana jin yadda bugun zuciyar ta ke sauyawa tamkar jinin jikinta ya tsinke .
Laɓɓan ta na karkarwa ta fara jaan ayoyi tana yin baya-baya ta koma cikin banɗakin ta rufo ƙofar , sai kawai ta fashe da kuka ,ita tun da ta san kan ta a matsayin mutum babu wani abun da take jin tsoro sama da kare ,
Bata son kare ta yadda ko da takun ƙafar sa ta gani a cikin ƙasa sai ta ji bugun zuciyar ta ya sauya Allah ya ratayawa ruhin ta tsoron kare .
Ta jima a zaune cikin banÉ—akin tana tunanin mafita "shin haka zata zauna kullum Sofi na azabtar da ita ta hanyar turo mata kare ? Ba zata iya ba domin watarana zuciyar ta zata gaza jurewa tsoron da take shiga sanadin haka sai ta mutu .
"To kuma idan ta faɗa me zai biyo baya watakila Sofi ta kashe ta da wuƙa da kuma ta san ba wanda zai san ita ta kashe ta domin daga jiya zuwa yau ta hango wani lamari tattare da Sofi da ya zarce mugunta sai dai a ƙira shi rashin imani.
" Wai kuma da gaske Yaya Dacta bai san da kare ba a gidan ? Anya gaskiya ne ?
Tunanin ta ya katse lokacin da ta ji karen na wani irin kuka ciki-ciki kamar gurnani , can kuma ta ji yayi shiru sai ta ɗan matsa kaɗan ta leƙa ta ƙafar makulli inda ta bar shi a kwance a can ta hango shi ya yada kai gefe .
Ta koma ta zauna tana tunanin yau kuma baya tsalle-tsallen ?
Har azahar tana cikin banɗaki har gyangyaɗi tayi ta farka lokacin ma ana ta sallah , ta sake leƙawa ga mamakin ta har yanzu fa Sam a inda yake anan yake kwance .
Shiru tayi tana nazarin sa da ta ƙura ido sosai sai ta ga kamar ma bacci yake .
yunwar da take ƙwaƙwular ta ita ta tunasar da ita cewa fa lokacin cin abincin ta na rana yana ƙoƙarin wucewa .
Tunanin da ya ɗarsu mata a rai a dai-dai lokacin ya sa tayi wani ɗan zullo tana dafe ƙirji a fili tace "wallahi bazan iya fita ba watakila idon sa biyu .
Can bayan kamar mintoci talatin da ta gama nazarin Sam ta haƙaƙe bacci yake yi sai ta buɗe ƙofar a hankali ta fito saɗaf-saɗaf ta nufi inda ta ajiye abincin ta kafin ta ɗauka sai da ta buɗe ƙaramin fridge da yake ɗakin ta ɗau ruwan roba mai sanyi guda ɗaya .
Tana juyawa kamar ance masa ya miƙe kawai sai ganin sa tayi akan ƙafafun sa huɗu yana kallon ta .
Wani irin ihu ta sa tana sakin ruwan hannun ta da warmer ɗin ta tarwatse a ƙasa da hakan yasa Sam ya dako tsalle yana zuwa a yunwace yasa bakin sa akan Basisen ya fara lasa yana haɗawa da pancake yana cinyewa bai ko bi ta kan Yakaka ba wacce tayi suman tsaye tana jira ta ji shi a kan ta yana kachal-chala mata tsoƙar jiki da faratan sa .
Wani irin riƙe jikin ta tayi har yatsun ta na shiga cikin carfet ɗin da yake shimfiɗe a ƙasa ji da tayi yana lasar rumfar ƙafar ta da basisen ya zuba akai a lokaci ɗaya wani irin tsoro mai haɗe da raɗaɗi ya ratsa tun daga ƙafar ta har ƙwaƙwalwar ta ta saki wani irin ihu da ya ratsa baki ɗayan gidan .
Numfashin ta kuma ya shiga ƙoƙarin barin jikin ta .
Ba zata iya sanin iyakar daɗewar da tayi ba kawai dai ta ji wani irin sanyi yana ratsa rumfar ƙafar ta da yasa ta buɗe ido a hankali .
Abunda ta gani ya matuƙar bata mamaki lokaci ɗaya da shiga sabon ruɗani .
Sam ne ta yake ta faman jido robar ruwan sanyi daga cikin fridge a bakin sa yana zuwa yana É—ora mata a jiki tamkar wanda aka sa shi yana yi yana kaÉ—a jela.
Tsam tayi tana kallon sa da idanun ta da suka rine jazur , sai da ya jido ruwan cikin fridge É—in kaf sannan ya dawo gaban ta ya tsugunna yana kallon ta tamkar mai jiran ta masa wani umarnin Sai zaro harshe yake yana lallago .
Kallon sa Yakaka tayi ta kawar da idanun ta zuwa lokacin har ta kai maƙura a tsoro alhalin babu mai ceton ta ba kuma wajen tsira dan haka ta fara dawowa cikin hankalin ta .
Tun tana tunanin zai bazamo kan ta har dai ta fahimci baya wani yunkuri na cutar da ita da ya wuce banga-banga da yayi a gaban ta dan haka a hankali ta kai hannu ta ɗau ɗaya daga cikin ruwan da ya jera mata bayan ta gama jujjuya robar ruwan a hannu ta ta ɓalle murfin ta sha ruwan da ɗan yawa kafin ta sauƙe gorar .
Mamakin ta ya ƙaru lokacin da ya sake kai fuskar sa ya daɗa turo mata wata gorar ruwan kusa da ƙafar ta .
Tana kallon sa ta kai hannu ta É—auka , sai ta ga yayi baya ya kwanta shirim! daga nesa kaÉ—an da ita .
Wata ɓoyayyar ajiyar zuciya tayi tana jin 'yar guntuwar nutsuwa na shigar ta sai ta gyara zaman ta da bata san yaushe ma ta zaunan ba ta miƙe kafafun ta da suka mata tsami saboda daɗewa da tayi a durkushe .
Cikin siririyar muryar ta ta fara yin karatun Alqur'ani bayan ta jingina kan ta da jikin gado.
Wata irin nutsuwa ce mai girma ta mamaye ta da ta lura hatta Sam shi ma ya samu kwatankwacin nutsuwar domin kwance yayi shiru ya kwantar da kunnuwan sa lanbar lokaci-lokaci yana kaÉ—a jelar sa .
Taɓe baki Sofia tayi tana hararar bayan Yakaka wacce ta riga ta juya tana barin wajen zuwa ɗaki kafin ta dawo da ganin ta kan Doctor Hamza .
Fuskar sa a É—aure yace "na faÉ—a miki ki daina neman fitina hakan ba kome zai jawo miki ba illa raini yarinyar nan dai a haife ma kin kusa haihuwar ta.
Kamar an soke ta da tsinin mashi haka Sofia ta ji , "ita zai ce ta haifi Yakaka ?
ƙanƙance ido tayi zata fara jaraba yayi wucewar sa cikin ɗaga taku yana barin falon ran sa cike taf da jin haushin korar masa Wafaa da tayi bata bari sun yi sallama ta masa rakiya ba .
Ta jima a tsaye a wajen tana rarrashin zuciyar ta da take ingizata akan ta je ta yiwa Yakaka dukan tsiya idan ya dawo ya ga banbancin shekarun a zahirance '
Sai dai ɗaya ɓarin zuciyar ta da yake cike da tsoron abun da hakan zai jawo ya hana ta aikatawa.
Sai da ta furzar da wata iska mai zafi sannan ta juya ta nufi É—akin da take É—aure Sam .
Yana kwance magashiyan kamar gawa , ƙafar ta tasa ta haure shi amma bai motsa ba " Dan ubanka kai ma ka tashi haka kaje kayi aikin da na kawo ka domin yi , ni inaga wannan maganin ma kamar ya maka ƙarfi yau ba zan baka shi ba .
Yakaka wacce har ta shiga wanka ta tuno da abincin ta na rana da ta ɓoye a kitchen cikin dabarar da take son yi , dan haka ta ɗaura towel ta zura hijabin ta ta murɗa ƙofar ta fito sai da tayi dube-dube ta samu tabbacin Sofia bata nan sannan da sassarfa ta tafi kitchen ta ɗauko sauran Basise da pancake da ta juye a warmer ta rufe ta nufo ɗaki.
zuwan ta tsakiyar falon yazo dai-dai da fitowar Sofia jaye da karen ta da yake ta turjewa yana wani É—an kuka .
Kallon-kallo suka yi a tsorace Yakaka ta jaa baya tana neman hanyar gudu cikin daƙiƙu kaɗan Sofia ta fahimci abunda Yakaka take shirin yi .
Dan haka ta zaburo bayan ta saki karen, da ganin haka Yakaka ta zuba a guje ta faɗa ɗaki da bata nesa da shi sosai tana shiga ta dire warmer ta danna ƙofar ta murza key bayan ta kulle ta zare shi daga jikin ƙofar dai-dai da ƙarasowar Sofia .
Wani irin duka Sofia ta kaiwa ƙofar kamar wacce ta sha giya ta shiga ƙundume-ƙundumen zagi tana cewa sai ta ga bayan Yakaka .
Yakaka wacce take jingine da jikin ƙofar daga ƙasa da ta zame ta zauna ji tayi hawaye na sauƙa a idanun ta wacce irin masifa ce wannan ?
"Ai kin kulle ƙofa a banza ki jira zan nuna miki iyakar ki zan nuna miki cewa nan gidana ne da baki isa min shamaƙi da wani ɓangare a cikin sa ba.
Tana jin lokacin da ta juya ta bar wajen bayan ta gama faɗin haka , ajiyar zuciya tayi ta miƙe tana ɗauke warmer ɗin daga wajen ta ajiye a gefen gado ,
Duk da ran ta na mata ciwo da irin yadda take rayuwar rashin Æ´anci amma ta ji daÉ—i da yau Sofia ba zata samu nasarar turo mata kare kamar yadda ta É—au alwashi ba ita daman ko babu kare a gidan ma yinin falo ba nata bane muddin Sofi na shawagi a gidan .
Wanka ta shiga ta ƙarasa ta kusa fitowa ta ji kamar an buɗe ƙofar an shigo ta ɗan kasa kunne bata ji motsi ba sai dai ƙarar rufe ƙofar da ta sake ji yasa a tsorace ta ɗauraye jikin ta ta fito .
Abun da ta gani yasa numfashin ta yin gargada 'Sam ne Sofia ta sake kawo mata shi kenan tana da makullin É—akin ? Yau ma so take tayi yini makamancin na jiya ?
Wani irin daskarewa take ji zuciyar ta na yi tsanar Sofi na ratsa kowanne lungu da saƙo na ran ta "sofia wace irin Azzaluma ce haka ? Da gaske idan bata bar gidan ba watarana Sofi zata kashe ta .
Kallon karen take yi tana jin yadda bugun zuciyar ta ke sauyawa tamkar jinin jikinta ya tsinke .
Laɓɓan ta na karkarwa ta fara jaan ayoyi tana yin baya-baya ta koma cikin banɗakin ta rufo ƙofar , sai kawai ta fashe da kuka ,ita tun da ta san kan ta a matsayin mutum babu wani abun da take jin tsoro sama da kare ,
Bata son kare ta yadda ko da takun ƙafar sa ta gani a cikin ƙasa sai ta ji bugun zuciyar ta ya sauya Allah ya ratayawa ruhin ta tsoron kare .
Ta jima a zaune cikin banÉ—akin tana tunanin mafita "shin haka zata zauna kullum Sofi na azabtar da ita ta hanyar turo mata kare ? Ba zata iya ba domin watarana zuciyar ta zata gaza jurewa tsoron da take shiga sanadin haka sai ta mutu .
"To kuma idan ta faɗa me zai biyo baya watakila Sofi ta kashe ta da wuƙa da kuma ta san ba wanda zai san ita ta kashe ta domin daga jiya zuwa yau ta hango wani lamari tattare da Sofi da ya zarce mugunta sai dai a ƙira shi rashin imani.
" Wai kuma da gaske Yaya Dacta bai san da kare ba a gidan ? Anya gaskiya ne ?
Tunanin ta ya katse lokacin da ta ji karen na wani irin kuka ciki-ciki kamar gurnani , can kuma ta ji yayi shiru sai ta ɗan matsa kaɗan ta leƙa ta ƙafar makulli inda ta bar shi a kwance a can ta hango shi ya yada kai gefe .
Ta koma ta zauna tana tunanin yau kuma baya tsalle-tsallen ?
Har azahar tana cikin banɗaki har gyangyaɗi tayi ta farka lokacin ma ana ta sallah , ta sake leƙawa ga mamakin ta har yanzu fa Sam a inda yake anan yake kwance .
Shiru tayi tana nazarin sa da ta ƙura ido sosai sai ta ga kamar ma bacci yake .
yunwar da take ƙwaƙwular ta ita ta tunasar da ita cewa fa lokacin cin abincin ta na rana yana ƙoƙarin wucewa .
Tunanin da ya ɗarsu mata a rai a dai-dai lokacin ya sa tayi wani ɗan zullo tana dafe ƙirji a fili tace "wallahi bazan iya fita ba watakila idon sa biyu .
Can bayan kamar mintoci talatin da ta gama nazarin Sam ta haƙaƙe bacci yake yi sai ta buɗe ƙofar a hankali ta fito saɗaf-saɗaf ta nufi inda ta ajiye abincin ta kafin ta ɗauka sai da ta buɗe ƙaramin fridge da yake ɗakin ta ɗau ruwan roba mai sanyi guda ɗaya .
Tana juyawa kamar ance masa ya miƙe kawai sai ganin sa tayi akan ƙafafun sa huɗu yana kallon ta .
Wani irin ihu ta sa tana sakin ruwan hannun ta da warmer ɗin ta tarwatse a ƙasa da hakan yasa Sam ya dako tsalle yana zuwa a yunwace yasa bakin sa akan Basisen ya fara lasa yana haɗawa da pancake yana cinyewa bai ko bi ta kan Yakaka ba wacce tayi suman tsaye tana jira ta ji shi a kan ta yana kachal-chala mata tsoƙar jiki da faratan sa .
Wani irin riƙe jikin ta tayi har yatsun ta na shiga cikin carfet ɗin da yake shimfiɗe a ƙasa ji da tayi yana lasar rumfar ƙafar ta da basisen ya zuba akai a lokaci ɗaya wani irin tsoro mai haɗe da raɗaɗi ya ratsa tun daga ƙafar ta har ƙwaƙwalwar ta ta saki wani irin ihu da ya ratsa baki ɗayan gidan .
Numfashin ta kuma ya shiga ƙoƙarin barin jikin ta .
Ba zata iya sanin iyakar daɗewar da tayi ba kawai dai ta ji wani irin sanyi yana ratsa rumfar ƙafar ta da yasa ta buɗe ido a hankali .
Abunda ta gani ya matuƙar bata mamaki lokaci ɗaya da shiga sabon ruɗani .
Sam ne ta yake ta faman jido robar ruwan sanyi daga cikin fridge a bakin sa yana zuwa yana É—ora mata a jiki tamkar wanda aka sa shi yana yi yana kaÉ—a jela.
Tsam tayi tana kallon sa da idanun ta da suka rine jazur , sai da ya jido ruwan cikin fridge É—in kaf sannan ya dawo gaban ta ya tsugunna yana kallon ta tamkar mai jiran ta masa wani umarnin Sai zaro harshe yake yana lallago .
Kallon sa Yakaka tayi ta kawar da idanun ta zuwa lokacin har ta kai maƙura a tsoro alhalin babu mai ceton ta ba kuma wajen tsira dan haka ta fara dawowa cikin hankalin ta .
Tun tana tunanin zai bazamo kan ta har dai ta fahimci baya wani yunkuri na cutar da ita da ya wuce banga-banga da yayi a gaban ta dan haka a hankali ta kai hannu ta ɗau ɗaya daga cikin ruwan da ya jera mata bayan ta gama jujjuya robar ruwan a hannu ta ta ɓalle murfin ta sha ruwan da ɗan yawa kafin ta sauƙe gorar .
Mamakin ta ya ƙaru lokacin da ya sake kai fuskar sa ya daɗa turo mata wata gorar ruwan kusa da ƙafar ta .
Tana kallon sa ta kai hannu ta É—auka , sai ta ga yayi baya ya kwanta shirim! daga nesa kaÉ—an da ita .
Wata ɓoyayyar ajiyar zuciya tayi tana jin 'yar guntuwar nutsuwa na shigar ta sai ta gyara zaman ta da bata san yaushe ma ta zaunan ba ta miƙe kafafun ta da suka mata tsami saboda daɗewa da tayi a durkushe .
Cikin siririyar muryar ta ta fara yin karatun Alqur'ani bayan ta jingina kan ta da jikin gado.
Wata irin nutsuwa ce mai girma ta mamaye ta da ta lura hatta Sam shi ma ya samu kwatankwacin nutsuwar domin kwance yayi shiru ya kwantar da kunnuwan sa lanbar lokaci-lokaci yana kaÉ—a jelar sa .