← Book details Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 252 OF 269

Sashe 252

Mafari Hargitsin Rayuwa Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Wata waftar da Sofi ta kawo mata ya sa ta daka tsalle ta tsallaka kan gadon ta hau ta tsaya..

"Zan kashe ki Yakaka na ga abunda zai faru ba dai kin gwada min naci ba ? Kin nuna a dole Mijina naki ne ko ? To sai na kashe ki kamar yadda na sha alwashi.

Daga can kuka Falmata ta sa ta yunƙura da ƙyar ta miƙe jikin ta na rawa ta miƙawa Hajja wayar da duk abunda Sofi take cewa a kunnuwan su muryar ta na rawa tace "Hajja , Hajja kin ji wai Sofi za ta kashe min Yakaka wallahi kuma za ta iya dan Allah ki bata hakuri Hajja.

Karɓar wayar Hajja tayi ta shiga cewa "alo 'Alo babba uwar Mama ba wa mahaukaciyar kishiyar ta ki wayar dan ƙunduƙurin ubata yau ji min tsinannana? Kishi hauka ne?

Jin shiru yasa Falmata ta sake rikicewa da muryar da take gaf da fara kuka tace ,

"Yakaka , Yakaka Dan Allah kiyi magana , Yakaka ki gudu dan Allah kar ta kashe ki..

"Ke jaa can ar kishiyar za ta guduwa ? Zancen banza ma kenan ,mugun nufi ai baya kashe ɗan barewa Babba uwar Mama zage ki taushe bakin akuyar wofi ki ɗaga ta sama ki doka ta da ƙasa kika yadda kika gudu ni da ke ne , nace ki zage ƙwanji 'yar nan ki kwaci 'yancin ki ta isa ne ma ta kashe ki ? Naushe ta a ƙahon zuci nace.

Hajja ta furta hakan har tana kaiwa iska duka tana cije baki cike da jin wani irin takaici na rufe ta .

Daga can kokawa tuƙuru ta sarƙe tsakanin Yakaka da Sofi da take neman shaƙe Yakaka amma ta kasa samun galaba abun mamaki wani irin ƙarfi ta tarar Yakakan na da shi da ko kusa ba ta yi zaton sa ba dan haka bata ankara ba ta tunkuɗa ta baya bata yi aune ba tayi baya ba shiri daɓas ta zauna da manyan mazauna ta akan wata ƙwalbar turaren da ta faɗo sanadin kokuwar da suke nan take kwalbar tace fusss! Ta fashe a take ta soki ɗuwawun ta.

Lokaci ɗaya wani irin raɗaɗi ya ratsa mata ƙwaƙwalwa da yasa ta saki ihu kafin ta dawo hayyacin ta Yakaka da daman matsera take nema ta tsallaƙe ta da gudu ta fice daga ɗakin bata tsaya ba ta buɗe ƙofar falon ta fita daga ita sai kayan jikin ta ƙafar ta ko takalmi babu sai fa wayar ta da take riƙe ƙam a hannun ta .

Sofi wacce bata saurari azabar da mazaunan ta ke mata ba ta fito gaba gaɗi tana ganin ƙofar falon a buɗe ta fahimci Yakaka ta fice a gidan abunda daman take so kenan .

Dan haka ta tura ƙofar falon da ƙarfi ba tare da ta kulle ba ta juya ta hau sama saboda raɗaɗin da take ji a mazaunan ta tana son ta duba irin raunin da ta ji.

Yakaka wacce take tsaye daga harabar gidan ta hango rufo ƙofar da Sofi tayi dan haka a galabaice ta samu waje daga gefe ta zauna baki ɗaya bugun zuciyar ta ba dai-dai yake ba .

Sofi ta kulle mata ƙofa ta bar ta a waje da tazarar tsakain ta da titi bai wani cika nisa ba sauran mutanen da suke makwaftaka duk za su iya ganin ta haka babu mayafin kirki wannan wane irin rayuwa ce take yi ?

Kiran wayar ta da aka yi yasa ta duba fuskar wayar sunan Hajja ta gani dan haka ta É—auka tana É—agawa daga can Falmata da ta kasa zaune ta kasa tsaye ta ce "Yakaka ke ce ? Bata mi ki kome ba ko.? D''

"Falmata ni ce eh na samu na gudo ki....'

"Kika gudu ? Gudu fa kika ce ?

Hajja take tambayar ta daga can kafin Yakaka ta ce wani abu Hajja ta karɓe wayar daga hannun Falmata tana cigaba da cewa

"Ke wacce irin Solobiya ce ? Kishiyar ke bin ki kina rugawa da gudu dan ragwanta da mutuwar zuciya kenan ko me ? Bakya tsayawa ki nuna mata banbancin ƙwarin jikin tsohuwa da na yarinya ? Wai ko ba wannan fantekar matar ta babban likita me jemammiyar fuskar nan ba ce ? Yanzu ita kike gudu ? Ita kike tsayawa tana cashe miki haka ba ki rama ba ? to wallahi kin rako mata 'yar nan ah lalle fa kina ina yanzu ?

A sanyaye Yakaka tace "ina waje harabar gidan Hajja ta koro ni wallahi tsoro nake ta ɗau wuƙa ta soka min dan haka ta ce min wai wallahi za ta kashe ni kuma ni wallahi bana son tashin hankali Hajja ni fa ko musu na fatar baki ciwon kai yake saka ni bare danbe hajja....

"A ah ai fa lalle abun nayi ne wai an biyawa bazaura Hajji , na gani na kuma shaida haka waliyya to kina jina ko ?

"Ba dai ita ta ce 'yar iska bace? Zata hana ki rawar gaban hantsi ke da gidan Mijin ki da ke kuma ta same ki solobiya kike biye mata ?

"Hajja .....

"Yi min shiru 'yar nan barni da ita ke dai bin umarni ne na ki , ince dai can layi ta koro ki ?

"Eh Hajja .

"Da mutane a wajen ko kuwa ?

"Eh da mutane dai kaÉ—an .

"A yaya kika fito titin ?

Yakaka ta É—an yi jim ita fa bata cika son biyewa subaÉ—aÉ—in Hajja ba muryar Hajjan ta katse ta da ta ji tana sake cewa

"Nace da kayan arziki a jikin ki ko kuwa É—an diras ne a jikin naki ?

"Hajja da kaya a jikina .

"To yaga su

"Eh Hajja?

"Nace ki yage kayan ki musu mummunan yagu .

"Haba Hajja ya kuma za ki ce ta yaga kayan ta a waje fa take ?
Falmata ta furta hakan tana zaro ido da mamaki

" kar ki katse ni ki min shiru '.

"Babba uwar Mama kina jina?

"Ina jin ki Hajja ki saurareni da kyau 'yanci nake son taya miki ki kwato , shi maganin biri karen maguzawa dan haka duk abinda nace miki kiyi , kiyi kawai ina mai tabbatar miki daga yau bata sake chakumar ki da dambe bare har ta kora ki layi .

"Ince kina da layin wayar shi Hamzan ?

"Ina da shi Hajja

" You katse ƙiran nan ki ƙira shi ki tabbatar kina gunjin kuka za ki ƙira shi kice ya taho yanzu ga matar sa za ta kashe ki kina faɗin hakan idan kin tabbatar ya ji sai ki kashe wayar daga nan ki sake ƙira na.

Doctor Hamza ya gama round kenan misalin sha biyu saura ya ga ƙiran Yakaka , fuskar sa cike da annuri ya ɗaga ƙiran yana jin 'yar guntuwar gajiyar na barin jikin sa .

Sai dai me ? Muryar ta da ya ji cikin kuka ya sa zuciyar sa yin tsalle hankalin sa a tashe yake tambayar ta me ya faru ? Tana kuka ta fara masa bayani bai gama saurara ba ma ya katse wayar hankali tashe ya fara ƙoƙarin barin asibitin .

Yakaka tana sauƙe wayar ta ƙira Hajja da daman tsumayar ta take dan haka nan take ta ɗaga "na ƙira shi Hajja . Ta ce a sanyaye .

"Yauwa ta farka rigar ta ki ta waje-wajen wuyan sannan ta ƙasa ma ki yiwa zanin naki ko siket mummunan yagu ta wajejen cinyar kina jina ?

"Hajja dame zan ya ga ? ba zai ji daÉ—i ba idan ya gan ni haka jiki a buÉ—e a waje .

"Kin ci gidan ku ana son ƙwatar miki ƴanci kina gardama cewa nake fitinannar matar sa ta koro ki ? Yi maza ki yage kayan nan dan a kori gaba .

Ba yadda Yakaka ta iya haka ta ɗan yiwa kayan jikin ta rauni da ƙyar saboda ƙarfin su .

Hajja tana iya jin ƙarar ɓarkewar kayan tace "Yauwa to sai abu na gaba da kin dai-daici ya kusa zuwa ki cisge ɗankwalin kan ki ki yasar , kuka kuwa kar ki ƙaƙƙauta har sai kin ga nata hawayen ita ma ba dan kome nasa kiyi haka ba sai dan a kori gaba kin fahimta ko.?

"Naji Hajja .

"Madallah.

Ba'a rufa mintuna goma ba sai ga Doctor Hamza a guje da motar sa da Yakaka tana hango shi ta fara kukan da daman yana cin ran ta kan irin tozarcin da Sofi ke mata.

Ƙafafun sa kamar ba za su iya ɗaukar sa ba ya fito a motar idanun sa da suke bayyana tashin hankali akan ta yana bin duk saassan jikin ta da kallo .

Yana ƙarasowa Yakaka ta faɗa jikin sa shi ma ya riƙe ta gam da wani irin yanayi a muryar sa yace "wa ya mi ki haka ?

Tana shiƙar kuka tace "auntie Sofi .

Hannun ta kawai ya kama suka nufi ƙofar shiga gidan yana murɗawa ya ji ta a ɓude '

"Sofi Wacce take baje akan kujera tana zuƙar shisha daga ita sai 'yar doguwar rigar shan iska gefen ta Sam ne a kwance daga ƙasa ta tasa masa abincin sa a gaba yana ci .( irin ita Bosslady )

Lokacin da ta ɗago kan ta tayi zaton Yakaka ce sai kawai tayi ido huɗu da Doctor Hamza da yake tsaye yana mata wani irin kallo na tsana daga bayan sa kuwa Yakaka ce take rakuɓe .

Assalam Alaykum masu karatu da fatan alkhairi.

Ina dai neman afuwar ku yau da gobe ta fi ƙarfin wasa jiki kuma da jini .

Ina kaunar ku domin Allah.'

Nagode
[4/15, 8:07 PM] +234 706 503 6187: MAFARI
......... HARGITSIN RAYUWA

UMM' MUAZ

54

MAI RABON SHAN DUKA

Ganin irin mummunan kallon da Doctor Hamza yake yi mata bai karya guiwar Sofi ba da zai sa har ta gaza yin wani yunkuri kare kanta ba .

Dan kuwa zuruf ta miƙe bayan ɗan taƙaitatatcen tunanin da ya gifta mata da bata yi ƙasa a guiwa ba ta fara ƙoƙarin tattaro nata makaman yaƙin "ai ba zata bari Yakaka ta ci ta da yaƙi ba haka nan take .ta aiyana hakan a zuciyar ta

"Doctor ka ga'.....
Chapter 252 · 0% Book details