Sashe 99
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Hala ba ki ji abin da Mommah ta faɗa ba?.." Ƙwanƙwasa ƙofar da aka yi shi ne ya dakatar da ita daga maganar da ta soma. Baba Atine ta shigo ta sanar da su saƙon Mommah a kan su fito za a yi dinner. Amsawa suka yi da "toh" Didi ba ta sake cewa komai ba ta miƙe cike da fatan Lulun ta ƙyaleta. Se kuwa ba tace mata komai ba, se ɗaukar mayafin abayar jikinsu da suka yi suka yafa sannan suka fice daga ɗakin. Daidai lokacin da suka fito daga ɗakin ya yi daidai da lokacin da Gwani da Bad Man suka shigo cikin ɗakin. Haka kuma ya yi daidai da lokacin da Iftihal ta fito daga cikin ɗakin da yanzu ita kaɗai ce a ciki, saboda en uwanta da suka tafi saura ita ɗaya da za ta koma ranar da su Mommah za su je gidan. Cikin jin daɗin ganinsu ta tafi da sauri cikin iyayi tace
"Sannunku da zuwa en uwa." Ta faɗa tana murmushi.
"Yawwah." Suka amsa kusan a tare.
"Mu je koh?" Ta faɗa kamar ita ce me gidan. Suna fara takawa ta yi yanda ta yi ta jera da Gwani. Kallan juna Lulu da Didi suka yi kafin suka maida dubansu gaba ba tare da sun ce komai ba. Se suka cigaba da takawa daidai lokacin da Iftihal ta ja kujerar kusa da wadda ta ga Gwani ya riƙe da alama a ita ze zauna. Se dai shi ba abin da yake nufi kenan ba, ya janyota ne dan Lulu ta zauna, se dai kuma har yanzu yana jin kunyar Mommah, wasu abubuwan dole ya dinga haƙura har su bar gabanta. Kafin ma ya gama tunanin da yake ya lura da Iftihal da ke ƙoƙarin zama a kusa da kujerar da ya riƙe ɗin. Kawai se ya zauna a kan kujerar yana ɗaga kansa ya kalli su Lulu da suka kusa ƙarasowa. Daidai lokacin da ya kalleta ya yi daidai da lokacin da ita ma ta kalle shi, ya sakar mata murmushi yana lumshe idanunsa cikin nata. Janye idanunta ta yi tana ɗan rufe idanunta kafin ta buɗe suka cigaba da tafiya. Tun tahowarsu ya kafeta da idanun nan nasa. Tun daga nesa ta tabbatar da lallai yana cikin ɗakin kuma kallanta yake yi. Dan kuwa idanunsa na da matuƙar tasirin da in dai ze kalleta se ta ji hakan, duk kuma se ya saka ta rasa sukuni. Sake gaisar da Mommah Gwani da Bad Man suka yi, ta amsa cikin kulawa. Ita da kanta ta shiga serving na kowa.
"Mommah kawo na.." Tun kafin Didi ta ƙarasa Mommah ta katseta da faɗin
"Yi zamanki Daughter.. babu damuwa." Se ta koma ta zauna. Se da Mommah ta gama da kowa sannan ta koma ta zauna. Se a lokacin sannan kowa ya ja abincin ya fara ci. Se dai ban da Bad Man, da ko kallan abincin be yi ba, se zubawa Didi ido da ya yi. Abin da Mommah ta faɗa ɗazu kawai shi yake tunawa. Maganganun da suka hana shi sukuni kenan, har ya kasa nutsuwa. Yanzu ma kiran nan ma Mommah yq ɗauka wani abun ne, se da suka zo sannan ya ji hankalinsa ya kwanta, da ya fahimci maganar ba a kan Didi ba ce. Gyara zama ya yi yana ɗora hannayensa a kan dinning ɗin kafin ya ɗora tafin hannunsa a haɓarsa. So yake Mommah ta haƙura, ta yadda da shi ta kuma ba shi matarsa dan wallahi ya yi nadama. Kwata kwata ta kasa sukuni, se gyara zama kawai da take yi. Ita kam ta ga ta kanta. Wai yaushe ya yi wannan muguwar chanjawar? Se kace wanda aka chanja? Gaba ɗaya ya zama wani iri. A hankali kuma se abin da Mommah ta faɗa mata ɗazun a ɗaki suka shiga dawo mata. Kenan da gaske yanzun yana sonta? Yana sonta sosai? Irin son da har za ta iya amfani da shi wajen sauya shi?
"Afrah lafiya kuwa?" Mommah da ta lura da ita ta faɗi haka. Kamar za ta yi kuka tace
"Mommah.." Se kuma ta yi shiru ba tace komai ba. Ganin Mommah na shirin kallansa ne ya sanya shi gyara zamansa ya basar. Se a lokacin Didi ta sauke numfashi. Ita kam har yanzu ba ta san ta ina za ta fara ba. Se take jin tsoron yin abin da Mommahn tace mata ta yi saboda gudun ɓacin rana. Kar ta je ba yanda Mommahn ke tunani ba ne ita kuma ta zo ta zaƙe. Se dai ko ma mene ne za ta yi ƙoƙarin yin hakan ko ma me ze biyo baya. A hankali ya kai hannunsa ze ɗauki ruwan da ke ajje kusa da plate nasa. Iftihal ta yi saurin riƙewa tana faɗin
"Haba.. bari na taimaka maka.." Ta yi maganar cikin muryarta da tafi kama da tsantsar iyayi a cikinta. Cokalin da Lulu ke amfani da shi cikin abincin da ke gabanta tana caccakawa kawai ba tare da ta kai ko loma ɗaya ba ne ta dakatar lokacin da ta ji abin da Iftihal ɗin ta faɗa. Haka nan kawai ta ji tana son ganin da wanda take. Ba ma ita kaɗai ba hatta Mommah da Didi se da suka ɗaga kai suka kalleta. Daidai lokacin da ta ɗaga idanun nata se suka sauka a kan Iftihal lokacin da take tsiyaya ruwa cikin wani glass cup. Se ta kasa ɗauke idanunta daga kanta. Har zuwa lokacin da Iftihal ta miƙawa Gwani kofin tana faɗin
"Ga shi.." Ta ƙare tana binsa da wani kallo lokaci ɗaya kuma tana sakar masa wani tattausan murmushi..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO76*
____ Kaasa ɗauke idanunta Lulu ta yi, se ta ji tana son gani ze karɓa ne ko kuwa ya ya? Hannu Gwani ya miƙa ya karɓa bayan ya ɗan yi wani yaƙe saboda murmushin da ya ga tana sakar masa kar ya yarfata.
"Na gode.." Ya yi maganar a nutse. Wani sabon murmushin ta sake saki tana wani buɗe baki tace
"Ahh me ye na godiya kuma Yayana?" Ta ƙarasa maganar tana ɗaukar cokali ta soma cin abincin, murmushi ya ƙi barin fuskarta. Da alama za ta yi nasara a wannan wasan. Yanzu dai duk wani burinta shi ne ta samu numbersa ta ƙarasa ragowar aikin ko da a gida ne. Ba ta san lokacin da ta sauke idanunta da sauri ba tana jin yanda zuciyarta ta shiga harbawa. A hankali kuma bugun zuciyarta ya soma saituwa, mamaki na kamata. Me ye musabbabin hakan? Tun da ta sauke idanunta ƙasa har suka gama dinner ba ta sake ɗagowa ba. Duk kuwa da tana jin magana sama sama amma ta kasa ɗaga idanunta. Duk yana lura da ita, hatta abincin da ba ta ci ba duk yana lura da ita. Be kawo komai a ransa ba, ya ɗauka ko abincin ne be mata ba.
"Afaaf me za a dafa miki?" Mommah ta tambaya tana kallanta. Se a lokacin sannan ta ɗaga kai ta kalleta ta girgiza kai kafin tace
"Na ƙoshi."
"Ya za ki ce kin ƙoshi? Me kika ci?"
"Ba komai amma na ƙoshi."
"Ba ki isa ba.. Je ki ɗaki zuwa an jima zan aiko kiranki." Kamar jira take, ta tura kujerar da take kai baya ta miƙe ta wuce ɗaki ba tare da ta kalli kowa ba. Binta da kallo Gwani ya yi yana mamakin abin da ya chanjata haka cikin ƙanƙanin lokaci.
.. Washegari tun safe Mommah ta ɗauki Lulu da Didi suka fice daga gidan, ba su suka dawo ba se wajen ƙarfe 3. Daidai lokacin da suke ƙoƙarin shiga sashen Mommah Gwani da Bad suka ƙaraso.
"Sannunku da zuwa Mommah.." Suka haɗa baki wajen faɗar hakan.
"Yawwah sannunku dai.." Ta amsa da murmushi tana kallansu. Tuni Didi da Lulu sun yi gaba dan sun gaisa da safe. Ita ma Mommah bin bayan nasu ta yi, kafin su Gwani ma suka rufa mata baya. Shi dai Bad a ɗarare yake kar ya je Mommahn tace ya juya, be sani ba damar da aka ba shi ko iya ta jiya ce kawai. Se be ji Mommahn tace komai ba har suka isa palournta.
"Afaaf tsaya ki gaisa da mijinki.. Ke kuma Afrah wuce mu tafi.." Mommah ta yi maganar tana kama hannun Didi suka wuce ɗaki. Kamar wani dolo haka ya bisu da kallo. Ya ɗan runtse idanunsa yana buɗewa a lokaci guda. Shi kam jikinsa gaba ɗaya ya yi sanyi da lamarin. Be san girman laifin da ya aikata babba ba ne se Mommah ta masa abu. Duk soyayyar da take masa ajeta gefe take ta masa abin da ta ga dama. A nutse ya juya ya kalli Gwani yace muryarsa kamar wanda ya ƙware
"Se ka fito." Be jira yace komai ba ya fice daga ɗakin, be kuma nufi ko ina ba se wajen motarsa, ya hau ya fice daga gidan.
"Mu je ki zauna koh?" Gwani ya faɗa yana kallan Lulu. Se a lokacin sannan ta ɗaga ƙafafunta kamar me jin tsoron ƙasa ta shiga takawa. Kan kujera ta zauna har lokacin ba tace komai ba. Shi ma neman waje ya yi ya zauna a gefenta, se dai in da ya san ze din ga ganinta.
"Ki na lafiya?" Tambayar da ya soma mata kenan. A hankali ta ɗan ɗaga kanta ta kalle shi, daidai lokacin da yake kallanta, se idanunsu suka shige cikin na juna. Maimakon a da da daga zarar sun haɗa ido za ta ɗauke nata, yanzu se ta kasa janyewa. Se kace wadda take son karanto wani abun cikin idanunsa. Sun kai wajen minti 1 a haka kafin Lulu ta sauke kai da sauri. Ajiyar zuciya ya sauke yana lumshe idanunsa, ya daɗe be mata irin wannan kallon ba. Yau ɗin da ya mata shi se yake jinsa zam zam. A hankali ya ɗan matsa kusa da ita, ya ɗan rage tazarar dake tsakaninsu. Ya saka hannunsa ya ɗan janye rigar jikinta kafin ya ɗora hannunsa a kan cikinta yace
"Sannunku da zuwa en uwa." Ta faɗa tana murmushi.
"Yawwah." Suka amsa kusan a tare.
"Mu je koh?" Ta faɗa kamar ita ce me gidan. Suna fara takawa ta yi yanda ta yi ta jera da Gwani. Kallan juna Lulu da Didi suka yi kafin suka maida dubansu gaba ba tare da sun ce komai ba. Se suka cigaba da takawa daidai lokacin da Iftihal ta ja kujerar kusa da wadda ta ga Gwani ya riƙe da alama a ita ze zauna. Se dai shi ba abin da yake nufi kenan ba, ya janyota ne dan Lulu ta zauna, se dai kuma har yanzu yana jin kunyar Mommah, wasu abubuwan dole ya dinga haƙura har su bar gabanta. Kafin ma ya gama tunanin da yake ya lura da Iftihal da ke ƙoƙarin zama a kusa da kujerar da ya riƙe ɗin. Kawai se ya zauna a kan kujerar yana ɗaga kansa ya kalli su Lulu da suka kusa ƙarasowa. Daidai lokacin da ya kalleta ya yi daidai da lokacin da ita ma ta kalle shi, ya sakar mata murmushi yana lumshe idanunsa cikin nata. Janye idanunta ta yi tana ɗan rufe idanunta kafin ta buɗe suka cigaba da tafiya. Tun tahowarsu ya kafeta da idanun nan nasa. Tun daga nesa ta tabbatar da lallai yana cikin ɗakin kuma kallanta yake yi. Dan kuwa idanunsa na da matuƙar tasirin da in dai ze kalleta se ta ji hakan, duk kuma se ya saka ta rasa sukuni. Sake gaisar da Mommah Gwani da Bad Man suka yi, ta amsa cikin kulawa. Ita da kanta ta shiga serving na kowa.
"Mommah kawo na.." Tun kafin Didi ta ƙarasa Mommah ta katseta da faɗin
"Yi zamanki Daughter.. babu damuwa." Se ta koma ta zauna. Se da Mommah ta gama da kowa sannan ta koma ta zauna. Se a lokacin sannan kowa ya ja abincin ya fara ci. Se dai ban da Bad Man, da ko kallan abincin be yi ba, se zubawa Didi ido da ya yi. Abin da Mommah ta faɗa ɗazu kawai shi yake tunawa. Maganganun da suka hana shi sukuni kenan, har ya kasa nutsuwa. Yanzu ma kiran nan ma Mommah yq ɗauka wani abun ne, se da suka zo sannan ya ji hankalinsa ya kwanta, da ya fahimci maganar ba a kan Didi ba ce. Gyara zama ya yi yana ɗora hannayensa a kan dinning ɗin kafin ya ɗora tafin hannunsa a haɓarsa. So yake Mommah ta haƙura, ta yadda da shi ta kuma ba shi matarsa dan wallahi ya yi nadama. Kwata kwata ta kasa sukuni, se gyara zama kawai da take yi. Ita kam ta ga ta kanta. Wai yaushe ya yi wannan muguwar chanjawar? Se kace wanda aka chanja? Gaba ɗaya ya zama wani iri. A hankali kuma se abin da Mommah ta faɗa mata ɗazun a ɗaki suka shiga dawo mata. Kenan da gaske yanzun yana sonta? Yana sonta sosai? Irin son da har za ta iya amfani da shi wajen sauya shi?
"Afrah lafiya kuwa?" Mommah da ta lura da ita ta faɗi haka. Kamar za ta yi kuka tace
"Mommah.." Se kuma ta yi shiru ba tace komai ba. Ganin Mommah na shirin kallansa ne ya sanya shi gyara zamansa ya basar. Se a lokacin Didi ta sauke numfashi. Ita kam har yanzu ba ta san ta ina za ta fara ba. Se take jin tsoron yin abin da Mommahn tace mata ta yi saboda gudun ɓacin rana. Kar ta je ba yanda Mommahn ke tunani ba ne ita kuma ta zo ta zaƙe. Se dai ko ma mene ne za ta yi ƙoƙarin yin hakan ko ma me ze biyo baya. A hankali ya kai hannunsa ze ɗauki ruwan da ke ajje kusa da plate nasa. Iftihal ta yi saurin riƙewa tana faɗin
"Haba.. bari na taimaka maka.." Ta yi maganar cikin muryarta da tafi kama da tsantsar iyayi a cikinta. Cokalin da Lulu ke amfani da shi cikin abincin da ke gabanta tana caccakawa kawai ba tare da ta kai ko loma ɗaya ba ne ta dakatar lokacin da ta ji abin da Iftihal ɗin ta faɗa. Haka nan kawai ta ji tana son ganin da wanda take. Ba ma ita kaɗai ba hatta Mommah da Didi se da suka ɗaga kai suka kalleta. Daidai lokacin da ta ɗaga idanun nata se suka sauka a kan Iftihal lokacin da take tsiyaya ruwa cikin wani glass cup. Se ta kasa ɗauke idanunta daga kanta. Har zuwa lokacin da Iftihal ta miƙawa Gwani kofin tana faɗin
"Ga shi.." Ta ƙare tana binsa da wani kallo lokaci ɗaya kuma tana sakar masa wani tattausan murmushi..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO76*
____ Kaasa ɗauke idanunta Lulu ta yi, se ta ji tana son gani ze karɓa ne ko kuwa ya ya? Hannu Gwani ya miƙa ya karɓa bayan ya ɗan yi wani yaƙe saboda murmushin da ya ga tana sakar masa kar ya yarfata.
"Na gode.." Ya yi maganar a nutse. Wani sabon murmushin ta sake saki tana wani buɗe baki tace
"Ahh me ye na godiya kuma Yayana?" Ta ƙarasa maganar tana ɗaukar cokali ta soma cin abincin, murmushi ya ƙi barin fuskarta. Da alama za ta yi nasara a wannan wasan. Yanzu dai duk wani burinta shi ne ta samu numbersa ta ƙarasa ragowar aikin ko da a gida ne. Ba ta san lokacin da ta sauke idanunta da sauri ba tana jin yanda zuciyarta ta shiga harbawa. A hankali kuma bugun zuciyarta ya soma saituwa, mamaki na kamata. Me ye musabbabin hakan? Tun da ta sauke idanunta ƙasa har suka gama dinner ba ta sake ɗagowa ba. Duk kuwa da tana jin magana sama sama amma ta kasa ɗaga idanunta. Duk yana lura da ita, hatta abincin da ba ta ci ba duk yana lura da ita. Be kawo komai a ransa ba, ya ɗauka ko abincin ne be mata ba.
"Afaaf me za a dafa miki?" Mommah ta tambaya tana kallanta. Se a lokacin sannan ta ɗaga kai ta kalleta ta girgiza kai kafin tace
"Na ƙoshi."
"Ya za ki ce kin ƙoshi? Me kika ci?"
"Ba komai amma na ƙoshi."
"Ba ki isa ba.. Je ki ɗaki zuwa an jima zan aiko kiranki." Kamar jira take, ta tura kujerar da take kai baya ta miƙe ta wuce ɗaki ba tare da ta kalli kowa ba. Binta da kallo Gwani ya yi yana mamakin abin da ya chanjata haka cikin ƙanƙanin lokaci.
.. Washegari tun safe Mommah ta ɗauki Lulu da Didi suka fice daga gidan, ba su suka dawo ba se wajen ƙarfe 3. Daidai lokacin da suke ƙoƙarin shiga sashen Mommah Gwani da Bad suka ƙaraso.
"Sannunku da zuwa Mommah.." Suka haɗa baki wajen faɗar hakan.
"Yawwah sannunku dai.." Ta amsa da murmushi tana kallansu. Tuni Didi da Lulu sun yi gaba dan sun gaisa da safe. Ita ma Mommah bin bayan nasu ta yi, kafin su Gwani ma suka rufa mata baya. Shi dai Bad a ɗarare yake kar ya je Mommahn tace ya juya, be sani ba damar da aka ba shi ko iya ta jiya ce kawai. Se be ji Mommahn tace komai ba har suka isa palournta.
"Afaaf tsaya ki gaisa da mijinki.. Ke kuma Afrah wuce mu tafi.." Mommah ta yi maganar tana kama hannun Didi suka wuce ɗaki. Kamar wani dolo haka ya bisu da kallo. Ya ɗan runtse idanunsa yana buɗewa a lokaci guda. Shi kam jikinsa gaba ɗaya ya yi sanyi da lamarin. Be san girman laifin da ya aikata babba ba ne se Mommah ta masa abu. Duk soyayyar da take masa ajeta gefe take ta masa abin da ta ga dama. A nutse ya juya ya kalli Gwani yace muryarsa kamar wanda ya ƙware
"Se ka fito." Be jira yace komai ba ya fice daga ɗakin, be kuma nufi ko ina ba se wajen motarsa, ya hau ya fice daga gidan.
"Mu je ki zauna koh?" Gwani ya faɗa yana kallan Lulu. Se a lokacin sannan ta ɗaga ƙafafunta kamar me jin tsoron ƙasa ta shiga takawa. Kan kujera ta zauna har lokacin ba tace komai ba. Shi ma neman waje ya yi ya zauna a gefenta, se dai in da ya san ze din ga ganinta.
"Ki na lafiya?" Tambayar da ya soma mata kenan. A hankali ta ɗan ɗaga kanta ta kalle shi, daidai lokacin da yake kallanta, se idanunsu suka shige cikin na juna. Maimakon a da da daga zarar sun haɗa ido za ta ɗauke nata, yanzu se ta kasa janyewa. Se kace wadda take son karanto wani abun cikin idanunsa. Sun kai wajen minti 1 a haka kafin Lulu ta sauke kai da sauri. Ajiyar zuciya ya sauke yana lumshe idanunsa, ya daɗe be mata irin wannan kallon ba. Yau ɗin da ya mata shi se yake jinsa zam zam. A hankali ya ɗan matsa kusa da ita, ya ɗan rage tazarar dake tsakaninsu. Ya saka hannunsa ya ɗan janye rigar jikinta kafin ya ɗora hannunsa a kan cikinta yace