Sashe 36
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kin ga Makiyya wallahi na gaji.. Na gaji da bin komai a sannu, ina kike so a zo ne? Ni fa na kasa gane miki." Mom ta faɗa da iya gaskiyarta. Ajiyar zuciya Aunty Makiyy ta sauke sannan tace
"Shi kenan next week ai dai zan dawo koh? Ina dawowa gidan zan fara zuwa se mu yi maganar.." Ta ɗan dakata a nan. Kamar jira Mom take yi se kuwa ta soma ƙoƙarin magana. Katseta Aunt Makiyy ta yi da faɗin
"Don Allah kar ki ce a'ah.. Ki ce toh kawai." Tsaki Mom ta ja sannan tace
"Na ji." Daga haka ta katse wayar, tana jin haushin kanta da ya shigar da Makiyyan cikin wannan lamarin. Da ta san za ta kawo mata wasa tun farko da ba ta sakota ba. A karo na biyu ta sake jan wani tsakin tana miƙewa dan shigewa bedroom ɗinta. Sallamar da ta ji daga bakin ƙofa ita ce ta sanyata dakatawa. Ta kalli me sallamar cike da mamaki. A nutse a kuma ɗarare Didi dake sanye cikin wata doguwar rigar atamfa da mayafi wadatacce, ta yi matuƙar kyau, ta ƙaraso cikin ɗakin ta zube a ƙasa cikin sanyin murya tace
"Barka da wannan lokaci.."
"Tashi tashi tashi.." Mom ta faɗa tana ɗaga hannunta alamar ta miƙe, ranta dake a ɓace ya sanya fuskar nan tata ta sake haɗewa waje ɗaya. Cikin lokaci ƙanƙani Didi ta ji jikinta ya ɗauki rawa, dama Allah ma ya gani a tsorace take tun kafin ta shigo ɗakin, yanzu kuma da ta shigo se ta ida tsoracewa, se dai duk da haka hakan be hanata miƙewa ɗin ba kamar yanda Mom ɗin ta buƙata. Kanta na a ƙasa ne tana tsoron jin abin da ze fito daga bakin Mom ɗin. Kamar kuwa Mom ɗin ta san me take jira se cewa ta yi
"Me ya kawo ki ɗakin nan? Waye ya aiko ki? Gulma da kinibibi ya kawo ki? Toh wuce ki tafi tun kafin raina ya kammala ɓaci na ci miki mutuncin da ba a taɓa yi miki ba. Fice min daga nan.." ta yi maganar cikin ɗaga murya tana nuna mata hanya. Da ƙyar Didi ta ɗaga ƙafafunta ta soma takawa dan ficewa daga ɗakin cike da sarewa da lamarin cikin gidan nan. Miji ba kirki, haka uwar mijin ma ba kirki. Ba ta san lokacin da ta ji wasu hawaye masu ɗumi sun zubo mata a kan kuncinta ba. Se ta kasa tsayar dasu kawai ta barsu suna zubar tana jiyo lokacin da Mom ke faɗin
"Shashashar banza er gidan talakawa.." Ta runtse idanunta tana jin yanda jikinta ke sanyi, zuciyarta na sake ƙuntata da kalaman Mom ɗin.
"Daughter.." Ta ji an faɗa dab da za ta wuce sashensu. Se ta ɗaga jajayen idanunta daidai lokacin da take share hawayen fuskarta ta kalli Mommah. Da sauri ta ƙarasa tana faɗin
"Subhanallahi.. kuka kuma?" Mommah ta faɗa tana riƙota. Se ta ji kamar Amminta ce, hakan ne ya sanyata faɗawa jikinta ta fashe da kuka. Ko Mommahn ba ta tambaya ba ta riga ta fahimci abin da ya faru, hakan ne ya sanyata rungume Didin cikin rarrashi tace
"Ki yi haƙuri ki yi shiru kin ji? Komai ze zo ƙarshe In Sha Allah.." Ta yi maganar tana ɗan shafa bayan Didin alamar rarrashi. Kasa shirun ta yi, har se da ta yi me isarta sannan ta koma sauke ajiyar zuciya. Se a lokacin ta tashi daga jikin Mommahn tana kan sheshsheƙa saboda kukan da ta yi. Kafin Mommahn tace komai wayarta dake hannunta ta soma ruri. Se ta kalli me kiran sannan ta ɗaga. A nutse ta yi sallama, Daddy ya amsa sallamar tata yana ɗorawa da
"Kin sanarwa da yarinyar ne?"
"A'ah yanzu dai nake shirin faɗa mata." Gyara zamansa Daddy ya yi a inda yake zaune yace
"Areef baya cikin gidan nan sun fita da Kaseem.. saboda haka ki sanar da ita ta shirya driver ze kaita idan ya so in ya dawo se ya je ya ɗaukota."
"Toh shi kenan Rankayadaɗe.." ta ƙare da murmushi a kan fuskarta. Daga haka ta ajje wayar ta maida dubanta kan Didi tace
"Maza ki ke ki shirya yanzu za a zo s ɗauke ki ki ke ki duba 'yar uwakki.." Da sauri ta kalli Mommah jin abin da tace. Gane mamakin da ya bayyana a kan fuskarta ya sanya Mommah yin murmushi dan kawar mata da wani tunanin tace
"Ko ba kya son zuwa?" Ba ta san lokacin da wani murmushi ya ƙwace mata ba, duk da har lokacin da ragowar kukan da be tafi ba. Hakan kuma da ta yi ba ƙaramin kyau ta yi ba. Se ta kai hannunta kan bakinta cikin matuƙar farin ciki tace
"Mommah da gaske?"
"Ƙwarai kuwa.." Mommah ta faɗa tana murmushi. Ba ta san lokacin da ta rungume Mommahn ba cike da maɗaukakin farin ciki muryarta na er rawa ta furta
"Na gode sosai Mommah.." ta yi maganar tsantsar farin cikinta na bayyana har cikin muryarta. Murmushi Mommah ta yi tana jin daɗin yanda ta saka Didin cikin farin ciki.
.. Da sauri da sauri ta shiga shiryawa tana ji kamar ta yi tsintsuwa ta ganta a wajen er uwar tata. Dan tunda Mommahn ta faɗa mata maganar zuwan nata wajen Lulu ta manta da damuwar da Mom ta sanya mata. Cikin wata doguwar rigar abaya ta shirya da wadataccen mayafinta. Ko tsayawa ta shafa wani abun kasawa ta yi se fitowa da ta yi inda Mommah ke jiranta da ta yi. Toh da yake ɗazun da ta fito daga wanka se da ta gyara fuskarta ya sanya har yanzun fuskar tata a gyare take tsaff kamar wadda ta zauna ta shafe awanni tana ƙyalƙyaleta. Nan kuwa banda kwalli, powder da lip gloss babu abin da ta shafa. Amma haka ta fito ta yi wani mugun kyau kamar ka saceta ka gudu.
Har wajen motar da za ta kaita Mommah ta rakata. Se da ta shiga mota sannan Mommah ta ɗora hannunta a kan glass ɗin ɓangaren da take
"A gaida min da ita.." Murmushi Didi ta yi tace
"Tohm.." Cikin ranta tana jin wata irin soyayyar Mommahn, mata me kirki da sanin ya kamata. Se a lokacin sannan Mommah ta soma takawa dan barin wajen, sannan drivern ya ja motar suka bar wajen. Tunda suka fara tafiya bakinta ya ƙi rufuwa, ta kasa dena murmushi, ta kasa dena zumuɗi. Duk da a mota suke amma ji take kamar ba ya sauri, kamar ta fita daga cikin motar ta yi gudu ta isa wajen er uwarta. A haka dai har suka ƙaraso asibitin. Da mamaki take kallan asibitin, a ranta tana tunanin waye ba shi da lafiya? Tuna babu wanda ze iya ba ta amsar ya sanyata yin shiru tana cigaba da bin asibitin da kallo. A daidai lokacin da Drivern ya yi parking Gwani ya ƙaraso inda suke. Da sauri ta saka hannunta ta buɗe murfin motar tana kallan Drivern dan jiran ƙarin bayani. Daidai lokacin da ta hango Gwani kenan, se ta yi shiru kawai har ya ƙaraso inda take. Se a lokacin ta iya buɗe baki tace
"Barka da wannan lokacin Ya mu'allim.."
"Barka dai.." Gwani ya amsa da hakan.
"Lulu ce ba ta da lafiya?" Ta yi tambayar fuskarta babu yabo babu fallasa dan ta ƙagu ta ji abin da ya kawota asibitin.
"Ehh zazzaɓi ne kawai.. Babu wani damuwa.. Mu je.." ya yi maganar yana soma takawa. Da sauri ta bi bayansa cike da zumuɗin son ganin er uwarta. Se dai duk wannan zumuɗin da take tunda ta gansu a asibiti ya ragu, duk se ta ji jikinta ya yi sanyi.
Lulu na zaune a kan gadon da abinci a gefenta se ɓata rai take, tunda ta ji zuwan Ammi asibitin tana bacci yanzu kuma ta fita wai za ta dawo a cewarsu. Ita dai ta musu shiru dan kowa ma haushinsa take ji, har shi kansa Little dake kusa da ita.
"Afaaf ki damu ki ci ko yaya ne kin ji? Ki yi haƙuri Ammin naki ai za ta dawo.. Kiranta aka yi a waya shi ya sa ta fita." Ummeey ta sake maimaita mata hakan. Se kawai ta kuma riƙe plate ɗin tana cigaba da tura baki ba tare da ta kalli Ummeeyn ba. Da sallama Gwani dake gaba ya shigo cikin ɗakin Didi na biye a bayansa idanunta a kan gadon marasa lafiyar dan ganin wanda ba shi da lafiyar da zuciyarta ke ta azalzalarta. Cikin sakannin da basu wuce 3 ba idanunta suka sauka a kan Lulu da kuma Little dake kusa da ita, ba ta san lokacin da ta tafi a guje ba tana faɗin
"Lulu.." Ɗago idanunta da Lulu za ta yi se suka sauka a kan fuskar Didin. Mantawa ma ta yi da ba ta da lafiya, ba ta san inda abincin ya yi bq ita dai ta san ta miƙe a kan ƙafafunta ta riga Didin zuwa inda gadon yake. Rungume junansu suka yi a tsakiyar ɗakin kusan lokaci guda suka fashe da kuka. Little dake gefensu shi ma kukan ya soma ganin da ya yi en uwansa na kuka. Da sauri suka yi ƙasa suna saka shi a tsakiya suka rungume junansu cikin matuƙar kewa da ƙaunar junansu. Sun kai wajen minti 1 a haka kafin suka saki junansu suka koma kan gadon. Se a lokacin sannan Didi ta iya gaishe da Ummeey dake kallansu cike da burgewa, musamman da ta ga kamannin nasu sakk da sakk ne kamar an tsaga kara. Ta amsa mata cike da fara'a tana tambayarta lafiyarta.
"Alhamdulillah.." Didi ta amsa da hakan.
"Toh madallah.. bari na ɗan fita." Ummeey ta yi maganar lokacin da ta fara takawa dan ficewa daga ɗakin, sanin da ta yi za su buƙaci yin hira a tsakaninsu. Aikuwa hakan take dan kuwa tana fita suka shiga hirar yaushe gamo.
.. Cikin rashin fahimta yace
"Ban gane ba Dad?"
"Ina nufin ka ɗauki mota ka je ka ɗauko matarka.."
"Dad.." ya sake faɗa cike da mamaki.
"I mean what i said.." Daddy ya katse shi da faɗin hakan. Cigaba ya yi da kallan Daddyn kamar ba ze ce komai ba se kuma yace
"Shi kenan next week ai dai zan dawo koh? Ina dawowa gidan zan fara zuwa se mu yi maganar.." Ta ɗan dakata a nan. Kamar jira Mom take yi se kuwa ta soma ƙoƙarin magana. Katseta Aunt Makiyy ta yi da faɗin
"Don Allah kar ki ce a'ah.. Ki ce toh kawai." Tsaki Mom ta ja sannan tace
"Na ji." Daga haka ta katse wayar, tana jin haushin kanta da ya shigar da Makiyyan cikin wannan lamarin. Da ta san za ta kawo mata wasa tun farko da ba ta sakota ba. A karo na biyu ta sake jan wani tsakin tana miƙewa dan shigewa bedroom ɗinta. Sallamar da ta ji daga bakin ƙofa ita ce ta sanyata dakatawa. Ta kalli me sallamar cike da mamaki. A nutse a kuma ɗarare Didi dake sanye cikin wata doguwar rigar atamfa da mayafi wadatacce, ta yi matuƙar kyau, ta ƙaraso cikin ɗakin ta zube a ƙasa cikin sanyin murya tace
"Barka da wannan lokaci.."
"Tashi tashi tashi.." Mom ta faɗa tana ɗaga hannunta alamar ta miƙe, ranta dake a ɓace ya sanya fuskar nan tata ta sake haɗewa waje ɗaya. Cikin lokaci ƙanƙani Didi ta ji jikinta ya ɗauki rawa, dama Allah ma ya gani a tsorace take tun kafin ta shigo ɗakin, yanzu kuma da ta shigo se ta ida tsoracewa, se dai duk da haka hakan be hanata miƙewa ɗin ba kamar yanda Mom ɗin ta buƙata. Kanta na a ƙasa ne tana tsoron jin abin da ze fito daga bakin Mom ɗin. Kamar kuwa Mom ɗin ta san me take jira se cewa ta yi
"Me ya kawo ki ɗakin nan? Waye ya aiko ki? Gulma da kinibibi ya kawo ki? Toh wuce ki tafi tun kafin raina ya kammala ɓaci na ci miki mutuncin da ba a taɓa yi miki ba. Fice min daga nan.." ta yi maganar cikin ɗaga murya tana nuna mata hanya. Da ƙyar Didi ta ɗaga ƙafafunta ta soma takawa dan ficewa daga ɗakin cike da sarewa da lamarin cikin gidan nan. Miji ba kirki, haka uwar mijin ma ba kirki. Ba ta san lokacin da ta ji wasu hawaye masu ɗumi sun zubo mata a kan kuncinta ba. Se ta kasa tsayar dasu kawai ta barsu suna zubar tana jiyo lokacin da Mom ke faɗin
"Shashashar banza er gidan talakawa.." Ta runtse idanunta tana jin yanda jikinta ke sanyi, zuciyarta na sake ƙuntata da kalaman Mom ɗin.
"Daughter.." Ta ji an faɗa dab da za ta wuce sashensu. Se ta ɗaga jajayen idanunta daidai lokacin da take share hawayen fuskarta ta kalli Mommah. Da sauri ta ƙarasa tana faɗin
"Subhanallahi.. kuka kuma?" Mommah ta faɗa tana riƙota. Se ta ji kamar Amminta ce, hakan ne ya sanyata faɗawa jikinta ta fashe da kuka. Ko Mommahn ba ta tambaya ba ta riga ta fahimci abin da ya faru, hakan ne ya sanyata rungume Didin cikin rarrashi tace
"Ki yi haƙuri ki yi shiru kin ji? Komai ze zo ƙarshe In Sha Allah.." Ta yi maganar tana ɗan shafa bayan Didin alamar rarrashi. Kasa shirun ta yi, har se da ta yi me isarta sannan ta koma sauke ajiyar zuciya. Se a lokacin ta tashi daga jikin Mommahn tana kan sheshsheƙa saboda kukan da ta yi. Kafin Mommahn tace komai wayarta dake hannunta ta soma ruri. Se ta kalli me kiran sannan ta ɗaga. A nutse ta yi sallama, Daddy ya amsa sallamar tata yana ɗorawa da
"Kin sanarwa da yarinyar ne?"
"A'ah yanzu dai nake shirin faɗa mata." Gyara zamansa Daddy ya yi a inda yake zaune yace
"Areef baya cikin gidan nan sun fita da Kaseem.. saboda haka ki sanar da ita ta shirya driver ze kaita idan ya so in ya dawo se ya je ya ɗaukota."
"Toh shi kenan Rankayadaɗe.." ta ƙare da murmushi a kan fuskarta. Daga haka ta ajje wayar ta maida dubanta kan Didi tace
"Maza ki ke ki shirya yanzu za a zo s ɗauke ki ki ke ki duba 'yar uwakki.." Da sauri ta kalli Mommah jin abin da tace. Gane mamakin da ya bayyana a kan fuskarta ya sanya Mommah yin murmushi dan kawar mata da wani tunanin tace
"Ko ba kya son zuwa?" Ba ta san lokacin da wani murmushi ya ƙwace mata ba, duk da har lokacin da ragowar kukan da be tafi ba. Hakan kuma da ta yi ba ƙaramin kyau ta yi ba. Se ta kai hannunta kan bakinta cikin matuƙar farin ciki tace
"Mommah da gaske?"
"Ƙwarai kuwa.." Mommah ta faɗa tana murmushi. Ba ta san lokacin da ta rungume Mommahn ba cike da maɗaukakin farin ciki muryarta na er rawa ta furta
"Na gode sosai Mommah.." ta yi maganar tsantsar farin cikinta na bayyana har cikin muryarta. Murmushi Mommah ta yi tana jin daɗin yanda ta saka Didin cikin farin ciki.
.. Da sauri da sauri ta shiga shiryawa tana ji kamar ta yi tsintsuwa ta ganta a wajen er uwar tata. Dan tunda Mommahn ta faɗa mata maganar zuwan nata wajen Lulu ta manta da damuwar da Mom ta sanya mata. Cikin wata doguwar rigar abaya ta shirya da wadataccen mayafinta. Ko tsayawa ta shafa wani abun kasawa ta yi se fitowa da ta yi inda Mommah ke jiranta da ta yi. Toh da yake ɗazun da ta fito daga wanka se da ta gyara fuskarta ya sanya har yanzun fuskar tata a gyare take tsaff kamar wadda ta zauna ta shafe awanni tana ƙyalƙyaleta. Nan kuwa banda kwalli, powder da lip gloss babu abin da ta shafa. Amma haka ta fito ta yi wani mugun kyau kamar ka saceta ka gudu.
Har wajen motar da za ta kaita Mommah ta rakata. Se da ta shiga mota sannan Mommah ta ɗora hannunta a kan glass ɗin ɓangaren da take
"A gaida min da ita.." Murmushi Didi ta yi tace
"Tohm.." Cikin ranta tana jin wata irin soyayyar Mommahn, mata me kirki da sanin ya kamata. Se a lokacin sannan Mommah ta soma takawa dan barin wajen, sannan drivern ya ja motar suka bar wajen. Tunda suka fara tafiya bakinta ya ƙi rufuwa, ta kasa dena murmushi, ta kasa dena zumuɗi. Duk da a mota suke amma ji take kamar ba ya sauri, kamar ta fita daga cikin motar ta yi gudu ta isa wajen er uwarta. A haka dai har suka ƙaraso asibitin. Da mamaki take kallan asibitin, a ranta tana tunanin waye ba shi da lafiya? Tuna babu wanda ze iya ba ta amsar ya sanyata yin shiru tana cigaba da bin asibitin da kallo. A daidai lokacin da Drivern ya yi parking Gwani ya ƙaraso inda suke. Da sauri ta saka hannunta ta buɗe murfin motar tana kallan Drivern dan jiran ƙarin bayani. Daidai lokacin da ta hango Gwani kenan, se ta yi shiru kawai har ya ƙaraso inda take. Se a lokacin ta iya buɗe baki tace
"Barka da wannan lokacin Ya mu'allim.."
"Barka dai.." Gwani ya amsa da hakan.
"Lulu ce ba ta da lafiya?" Ta yi tambayar fuskarta babu yabo babu fallasa dan ta ƙagu ta ji abin da ya kawota asibitin.
"Ehh zazzaɓi ne kawai.. Babu wani damuwa.. Mu je.." ya yi maganar yana soma takawa. Da sauri ta bi bayansa cike da zumuɗin son ganin er uwarta. Se dai duk wannan zumuɗin da take tunda ta gansu a asibiti ya ragu, duk se ta ji jikinta ya yi sanyi.
Lulu na zaune a kan gadon da abinci a gefenta se ɓata rai take, tunda ta ji zuwan Ammi asibitin tana bacci yanzu kuma ta fita wai za ta dawo a cewarsu. Ita dai ta musu shiru dan kowa ma haushinsa take ji, har shi kansa Little dake kusa da ita.
"Afaaf ki damu ki ci ko yaya ne kin ji? Ki yi haƙuri Ammin naki ai za ta dawo.. Kiranta aka yi a waya shi ya sa ta fita." Ummeey ta sake maimaita mata hakan. Se kawai ta kuma riƙe plate ɗin tana cigaba da tura baki ba tare da ta kalli Ummeeyn ba. Da sallama Gwani dake gaba ya shigo cikin ɗakin Didi na biye a bayansa idanunta a kan gadon marasa lafiyar dan ganin wanda ba shi da lafiyar da zuciyarta ke ta azalzalarta. Cikin sakannin da basu wuce 3 ba idanunta suka sauka a kan Lulu da kuma Little dake kusa da ita, ba ta san lokacin da ta tafi a guje ba tana faɗin
"Lulu.." Ɗago idanunta da Lulu za ta yi se suka sauka a kan fuskar Didin. Mantawa ma ta yi da ba ta da lafiya, ba ta san inda abincin ya yi bq ita dai ta san ta miƙe a kan ƙafafunta ta riga Didin zuwa inda gadon yake. Rungume junansu suka yi a tsakiyar ɗakin kusan lokaci guda suka fashe da kuka. Little dake gefensu shi ma kukan ya soma ganin da ya yi en uwansa na kuka. Da sauri suka yi ƙasa suna saka shi a tsakiya suka rungume junansu cikin matuƙar kewa da ƙaunar junansu. Sun kai wajen minti 1 a haka kafin suka saki junansu suka koma kan gadon. Se a lokacin sannan Didi ta iya gaishe da Ummeey dake kallansu cike da burgewa, musamman da ta ga kamannin nasu sakk da sakk ne kamar an tsaga kara. Ta amsa mata cike da fara'a tana tambayarta lafiyarta.
"Alhamdulillah.." Didi ta amsa da hakan.
"Toh madallah.. bari na ɗan fita." Ummeey ta yi maganar lokacin da ta fara takawa dan ficewa daga ɗakin, sanin da ta yi za su buƙaci yin hira a tsakaninsu. Aikuwa hakan take dan kuwa tana fita suka shiga hirar yaushe gamo.
.. Cikin rashin fahimta yace
"Ban gane ba Dad?"
"Ina nufin ka ɗauki mota ka je ka ɗauko matarka.."
"Dad.." ya sake faɗa cike da mamaki.
"I mean what i said.." Daddy ya katse shi da faɗin hakan. Cigaba ya yi da kallan Daddyn kamar ba ze ce komai ba se kuma yace