Sashe 13
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Mom.." ya faɗa da ɗan kaushi cikin muryarsa. Ajiyar zuciya Mom ta sauke, tana ganin kallan da Bad ɗin ke binta da shi tace
"Dalili ne ya sanya ni hakan. Shin ba ka ji me nace ba? Ba ka ji abin da Daddynka ya faɗa ba?"
"Whatever he said ba problem ɗina ba ne Mom. Ina so ne kawai na yi abin da ya dace. Ku kuma sake fahimtar ba a min abu se lokacin da nake so.." ya ƙare yana furzar da iska daga bakinsa me zafi, fuskarsa ta wani cakuɗe da ɓacin rai, haka zalika ko cikin muryarsa ma tana nuna ɓacin ran da yake ciki.
"Na sani Son. Daddy be kyauta mana ba, but za mu magance matsalar nan a hankali ba cikin gaggawa ba. Ni dai so nake ka tuna abin da ya faɗa, idan dai har ka saketa toh ni ma ze sake ni.."
"Daddy..?" Ya faɗa cike da mamaki. Se ta jinjina kai tace
"Ƙwarai kuwa.. Amma fa ka sani ba faɗin hakan da ya yi ne ze sanyaka zama da yarinyar ba, a'ah nan da en kwanaki ƙalilan zan fito da wata dabarar da ze sa ka saketa ba tare da kowa ya zargi wani ba." Shiru kawai ya yi mata, duk da ya ji abin da ta faɗa ɗin. Se lumshe lumsassun idanunsa kawai da ya yi yana jin yanda Daddyn ke ƙoƙarin sake manna masa ciwon kai da wannan aika_aikar da ya masa. Jin ya yi shiru ne ta fahimci ya ji abin da ta faɗa, ya kuma gamsu da hakan, dan haka tace
"Toh ka tashi ka je sashen kamar yanda yace maka saboda tsaro.." Se a lokacin ya buɗe idanun nasa, ya kalli Mom. Ya buɗe bakinsa da ƙyar yace
"Sashe..?"
"Ehh fa, duk dan ka da ya fahimci wani abun ne fa.."
"No.. ba zan je ba." Ya faɗa yana gyara zamansa. Cikin lallashi Mom ta nemi gefensa ta zauna, se da ta yi ƙasa da murya sannan ta soma faɗin
"Ka san.."
"Pls Mom ba zan je ba.." ya sake faɗa a karo na biyu yana ƙoƙarin miƙewa.
"Na fita se na dawo.." ya faɗa dan ya fahimci ita ma Mom ɗin so take ta fusata shi, bayan na Daddy.
"Pls Boy.. idan ka yi hakan fa za ka cire ni ne daga zargi.. Kuma ba ina nufin ku zauna ɗaki ɗaya ba, a'ah.. Allah ma ya kiyaye.. Kawai dai za ka nemi ɗaki ne cikin part ɗin ka zauna, saboda ko da maganar sakin ce ta tashi babu wanda ze yi wani zargi, ko a ce ni ce na zugaka." Ta ƙare cikin rarrashi cike da fatan ya amincewa maganar tata. Can ƙasan maƙoshi ya furta
"Naa.. ji" yana ficewa daga ɗakin.
... Ya ƙara wajen awa ɗaya a wajen suna cigaba da hira da Ummeey. Ita kuma tana cigaba da aikinta, har zuwa lokacin da ta gama ƙosai da kunu, se ta sami flask ɗinsu me kyau da kuma wani silver cup ta zuba kunu da ƙosan. Ta kalli Gwani dake kusa da ita tace
"Maza je ka kaiwa ɗiyata ta karya. Allah ya sa dai ban barta da yunwa ba.." Murmushi kawai ya yi a ransa yana mamakin hali irin na Lulu, tabbas da ita wata mutuniyar arziƙi ce se yace ta yi dacen sirika ainun. Ko a yanzu kaɗai se Ummeeyn ta birge shi, se yake ji ina ma a ce Lulun mutuniyar kirki ce, wadda ta san darajar mutane musamman ma manyan da suka haifeta.
"Zan fa ɗauka na kai da kaina.." Ummeey ta katse shi da faɗin hakan. Se ya miƙe kawai yana sake yin murmushin, dan be ma san abin da ze ce ba. Ya ɗauki flask da cup ɗin ya wuce zuwa ɗakin nasa. Kamar ko da yaushe, yanzu ma haka da sallama a kan laɓɓansa ya shiga cikin ɗakin. Tana zaune a kan gadon ta rafka wani uban tagumi kamar wadda aka yiwa mutuwa. Fuskar nan kamar za ta kaiwa na kusa da ita duka. Ta cika ta yi famm, ƙiris take jira ta fashe. Kai tsaye inda take ɗin ya isa. Ya ajje su a gefenta kana ya sake ɗaukar abun buƙata ya fice daga ɗakin. Har ya gama abin da yake yi ba ta ɗago ta kalle shi ba, saboda yanda zuciyarta ke mata zafi, musamman a yanzun da tafi sarewa da zuwan Mami fiye da ɗazu. Ɗaga ido ta yi ta kalli abin da ya ajje ɗin, ta taɓe baki tana faɗin
"Allah ya kiyaye ni cin abincin gidan nan.. Ko mutuwa zan yi ba zan ci ba har se na koma gidanmu." Ta faɗa tana murguɗa baki kamar da wani a kusa da ita. Cigaba da zama ta yi, ba tare da ta bi ta kan abincin ba. Zuwa can dai da ta gaji se ta miƙe zaune kawai cikin nemarwa kanta mafita. Wayarsa da ta gani ajje ya sanyata ƙarasawa da sauri ta ɗauka ta duba lokaci. Ganin yanda lokaci ya ja ne ya sanyata maida wayar inda take, zuwa yanzu kam ta gama saddaƙarwa Mami ba zuwa za ta yi ba. Dan haka se kawai ta gyara zaman hijab ɗinta ta soma takawa dan barin ɗakin. Kafin ta ƙarasa fitowa daga ɗakin ta tsaya ta kalli gidan, ta sake kallan gidan. Se ta yi gefe da kanta tana faɗin
"Tuff.." ta faɗa kawai irin a iskancen nan ba tare da ta zubda komai daga bakinta ba. Yau ɗin da ta sake ganin gidan nasu se ta ji haushinsa ya ƙaru a cikin ranta. Kenan me yake taƙama da shi da yake ji da kansa, izza kamar wani ɗan gidan sarauta bayan shi ɗin ba kowa ba ne? Se taƙama da kyau da duk en makarantar sun shaida amma banda ita, dan kuwa ita dai ba ta ga kyan da ake faɗa ba. Mutum se Addini kawai, da nuna shi ɗin wani ne. Toh yau dai ga ta a cikin gidansu, ga ta a cikin ɗakinsa, ba ta ga wani abu da ze sa ya dinga ɗaukar kansa daidai da ita ba. Kawai se ta sake taɓe baki tana ƙarasa fitowa daga cikin ɗakin. Daidai lokacin da Ummeey ta kwashe sharar da ta yi a inda ta gama girki, murmushi ya suɓuce mata sanda ta ga Lulun na fitowa daga cikin ɗakin.
"Kin gaji da zaman koh?" Ummeey ta faɗa tana kallanta. Da sauri Lulu ta ɗaga kai ta kalleta, dan ba ta yi tsammanin ganin kowa a wajen ba. Ganin murmushi ne har lokacin a fuskar Ummeey ya sanyata yin yaƙe kawai, wanda kana ganin fuskarta za ka fahimci hakan.
"Mu je ki zauna a ciki kafin ki dawo.." Ummeey ta faɗa. Ji ta yi kamar ta rusa ihu, ko kuma ta zage ta juye kwandon rashin kirkin da ta kwaso, da kuma haushin rashin zuwan Mami da ya ƙara fusatata, take ji za ta iya yiwa duk wani na cikin gidan bore, ta yi musu da yaren da za su fi gane gida take so su maidata, ba za ta taɓa zama cikin gidan nan ba. Se dai yanda matar ta mata kwarjini ya sanyata kasa ƙoƙarin yin komai, se binta a baya da ta yi, duk da har lokacin zuciyarta tafasa take yi. Har ɗaki Ummeey ta kai Lulun, ta nemi waje ta zauna tana sake kallan cikin ɗakin. Ita har mamaki ma abin yake bata, yanda aka yi wanda ya tashi a gida kamar wannan ya kasance Gwani. Wanda a yanayinsa ko wani abun ƙaryarka ka iya fasalta muhallin da ya taso. Ta sake taɓe baki tana jin yanda zuciyarta ta sake yo kusa kusa. Fita Ummeey ta yi zuwa inda tukunyar girkinta take, ta zubowa Lulun dambun masarar da ta gama yinsa yanzun nan. Se da ta ɗebo mata ruwa a randa sannan ta shigo ɗakin ta ajje a gaban Lulun tace
"Ki ci kin ji ɗiyata.." Bin kwanon ta yi da kallo tana ji kamar ta yi fatali da shi, ita sam ba wannan ne a gabanta ba, burinta kawai ta ganta a gida. Ko ma ba a gida ba ne, ta dena ganinta cikin mutanen dake da alaƙa da Gwani.
"Na ƙoshi.." karo na farko kenan da ta yi magana. Murmushi Ummeey ta yi sannan tace
"A'ah fa.. ban yarda ba. Ki ci ko kaɗan ne idan ya so anjima se ki ƙara.."
"Allah na ƙoshi ni." Ta faɗa tana gyara zamanta. Jin Ummeeyn za ta sake cewa wani abu ya sanyata faɗin
"Na ci abinci ɗazu." Ta faɗa dan ba ta so Ummeeyn ta ƙara yi mata wata maganar a kan abincin, dan sake tunzurata take yi.
"Toh madallah.." Ummeey ta faɗa tana miƙewa dan ficewa daga ɗakin, wataƙila idan ta ga ba ta cikin ɗakin ta samu ta ci ko kaɗan ne. Runtse idanunta Lulu ta yi tana sauke numfashi da sauri da sauri. Haka ba dan ta so ba ta cigaba da zama cikin ɗakin kamar za ta rusa ihu.
Ya yi matuƙar mamaki lokacin da ya shiga ɗakin ya ga ba ta ciki. Mamaki ya kama shi, ka da dai a ce guduwa ta yi? Idan guduwa ta yi ina ta je kenan? Dan ya san dai ba za ta tunkari gida ba idan ta aikata wannan ɗanyen aiki. Ya ɗan fesar da iska daga bakinsa yana lumshe idanunsa. Shi kam ya haɗu da wahala, wannan wace irin mata ce? Miƙewa ya yi kuma da ɗan sauri kamar wanda ya tuna wani abu. Kai tsaye ɗakin Ummeey ya wuce.. A tsakar gida ya tarar da Ummeeyn tana kwashe kayan da ta gama wankesu ɗazu da safe. Da sauri ya ƙarasa ya karɓi kayan a hannunta yana faɗin
"Da kanki kuma Ummeey?"
"Babu komai Affan.. Ka dawo?" Ta faɗa da murmushi a kan fuskarta. Jinjina kai ya yi kana ya amsa da
"Ehh.."
"Ka kyauta da ka dawo yanzu ai.. Ka bar er mutane dama ita kaɗai? Ba ta saba ba se fitowa ta yi, yanzu haka tana ɗakina.."
"Dalili ne ya sanya ni hakan. Shin ba ka ji me nace ba? Ba ka ji abin da Daddynka ya faɗa ba?"
"Whatever he said ba problem ɗina ba ne Mom. Ina so ne kawai na yi abin da ya dace. Ku kuma sake fahimtar ba a min abu se lokacin da nake so.." ya ƙare yana furzar da iska daga bakinsa me zafi, fuskarsa ta wani cakuɗe da ɓacin rai, haka zalika ko cikin muryarsa ma tana nuna ɓacin ran da yake ciki.
"Na sani Son. Daddy be kyauta mana ba, but za mu magance matsalar nan a hankali ba cikin gaggawa ba. Ni dai so nake ka tuna abin da ya faɗa, idan dai har ka saketa toh ni ma ze sake ni.."
"Daddy..?" Ya faɗa cike da mamaki. Se ta jinjina kai tace
"Ƙwarai kuwa.. Amma fa ka sani ba faɗin hakan da ya yi ne ze sanyaka zama da yarinyar ba, a'ah nan da en kwanaki ƙalilan zan fito da wata dabarar da ze sa ka saketa ba tare da kowa ya zargi wani ba." Shiru kawai ya yi mata, duk da ya ji abin da ta faɗa ɗin. Se lumshe lumsassun idanunsa kawai da ya yi yana jin yanda Daddyn ke ƙoƙarin sake manna masa ciwon kai da wannan aika_aikar da ya masa. Jin ya yi shiru ne ta fahimci ya ji abin da ta faɗa, ya kuma gamsu da hakan, dan haka tace
"Toh ka tashi ka je sashen kamar yanda yace maka saboda tsaro.." Se a lokacin ya buɗe idanun nasa, ya kalli Mom. Ya buɗe bakinsa da ƙyar yace
"Sashe..?"
"Ehh fa, duk dan ka da ya fahimci wani abun ne fa.."
"No.. ba zan je ba." Ya faɗa yana gyara zamansa. Cikin lallashi Mom ta nemi gefensa ta zauna, se da ta yi ƙasa da murya sannan ta soma faɗin
"Ka san.."
"Pls Mom ba zan je ba.." ya sake faɗa a karo na biyu yana ƙoƙarin miƙewa.
"Na fita se na dawo.." ya faɗa dan ya fahimci ita ma Mom ɗin so take ta fusata shi, bayan na Daddy.
"Pls Boy.. idan ka yi hakan fa za ka cire ni ne daga zargi.. Kuma ba ina nufin ku zauna ɗaki ɗaya ba, a'ah.. Allah ma ya kiyaye.. Kawai dai za ka nemi ɗaki ne cikin part ɗin ka zauna, saboda ko da maganar sakin ce ta tashi babu wanda ze yi wani zargi, ko a ce ni ce na zugaka." Ta ƙare cikin rarrashi cike da fatan ya amincewa maganar tata. Can ƙasan maƙoshi ya furta
"Naa.. ji" yana ficewa daga ɗakin.
... Ya ƙara wajen awa ɗaya a wajen suna cigaba da hira da Ummeey. Ita kuma tana cigaba da aikinta, har zuwa lokacin da ta gama ƙosai da kunu, se ta sami flask ɗinsu me kyau da kuma wani silver cup ta zuba kunu da ƙosan. Ta kalli Gwani dake kusa da ita tace
"Maza je ka kaiwa ɗiyata ta karya. Allah ya sa dai ban barta da yunwa ba.." Murmushi kawai ya yi a ransa yana mamakin hali irin na Lulu, tabbas da ita wata mutuniyar arziƙi ce se yace ta yi dacen sirika ainun. Ko a yanzu kaɗai se Ummeeyn ta birge shi, se yake ji ina ma a ce Lulun mutuniyar kirki ce, wadda ta san darajar mutane musamman ma manyan da suka haifeta.
"Zan fa ɗauka na kai da kaina.." Ummeey ta katse shi da faɗin hakan. Se ya miƙe kawai yana sake yin murmushin, dan be ma san abin da ze ce ba. Ya ɗauki flask da cup ɗin ya wuce zuwa ɗakin nasa. Kamar ko da yaushe, yanzu ma haka da sallama a kan laɓɓansa ya shiga cikin ɗakin. Tana zaune a kan gadon ta rafka wani uban tagumi kamar wadda aka yiwa mutuwa. Fuskar nan kamar za ta kaiwa na kusa da ita duka. Ta cika ta yi famm, ƙiris take jira ta fashe. Kai tsaye inda take ɗin ya isa. Ya ajje su a gefenta kana ya sake ɗaukar abun buƙata ya fice daga ɗakin. Har ya gama abin da yake yi ba ta ɗago ta kalle shi ba, saboda yanda zuciyarta ke mata zafi, musamman a yanzun da tafi sarewa da zuwan Mami fiye da ɗazu. Ɗaga ido ta yi ta kalli abin da ya ajje ɗin, ta taɓe baki tana faɗin
"Allah ya kiyaye ni cin abincin gidan nan.. Ko mutuwa zan yi ba zan ci ba har se na koma gidanmu." Ta faɗa tana murguɗa baki kamar da wani a kusa da ita. Cigaba da zama ta yi, ba tare da ta bi ta kan abincin ba. Zuwa can dai da ta gaji se ta miƙe zaune kawai cikin nemarwa kanta mafita. Wayarsa da ta gani ajje ya sanyata ƙarasawa da sauri ta ɗauka ta duba lokaci. Ganin yanda lokaci ya ja ne ya sanyata maida wayar inda take, zuwa yanzu kam ta gama saddaƙarwa Mami ba zuwa za ta yi ba. Dan haka se kawai ta gyara zaman hijab ɗinta ta soma takawa dan barin ɗakin. Kafin ta ƙarasa fitowa daga ɗakin ta tsaya ta kalli gidan, ta sake kallan gidan. Se ta yi gefe da kanta tana faɗin
"Tuff.." ta faɗa kawai irin a iskancen nan ba tare da ta zubda komai daga bakinta ba. Yau ɗin da ta sake ganin gidan nasu se ta ji haushinsa ya ƙaru a cikin ranta. Kenan me yake taƙama da shi da yake ji da kansa, izza kamar wani ɗan gidan sarauta bayan shi ɗin ba kowa ba ne? Se taƙama da kyau da duk en makarantar sun shaida amma banda ita, dan kuwa ita dai ba ta ga kyan da ake faɗa ba. Mutum se Addini kawai, da nuna shi ɗin wani ne. Toh yau dai ga ta a cikin gidansu, ga ta a cikin ɗakinsa, ba ta ga wani abu da ze sa ya dinga ɗaukar kansa daidai da ita ba. Kawai se ta sake taɓe baki tana ƙarasa fitowa daga cikin ɗakin. Daidai lokacin da Ummeey ta kwashe sharar da ta yi a inda ta gama girki, murmushi ya suɓuce mata sanda ta ga Lulun na fitowa daga cikin ɗakin.
"Kin gaji da zaman koh?" Ummeey ta faɗa tana kallanta. Da sauri Lulu ta ɗaga kai ta kalleta, dan ba ta yi tsammanin ganin kowa a wajen ba. Ganin murmushi ne har lokacin a fuskar Ummeey ya sanyata yin yaƙe kawai, wanda kana ganin fuskarta za ka fahimci hakan.
"Mu je ki zauna a ciki kafin ki dawo.." Ummeey ta faɗa. Ji ta yi kamar ta rusa ihu, ko kuma ta zage ta juye kwandon rashin kirkin da ta kwaso, da kuma haushin rashin zuwan Mami da ya ƙara fusatata, take ji za ta iya yiwa duk wani na cikin gidan bore, ta yi musu da yaren da za su fi gane gida take so su maidata, ba za ta taɓa zama cikin gidan nan ba. Se dai yanda matar ta mata kwarjini ya sanyata kasa ƙoƙarin yin komai, se binta a baya da ta yi, duk da har lokacin zuciyarta tafasa take yi. Har ɗaki Ummeey ta kai Lulun, ta nemi waje ta zauna tana sake kallan cikin ɗakin. Ita har mamaki ma abin yake bata, yanda aka yi wanda ya tashi a gida kamar wannan ya kasance Gwani. Wanda a yanayinsa ko wani abun ƙaryarka ka iya fasalta muhallin da ya taso. Ta sake taɓe baki tana jin yanda zuciyarta ta sake yo kusa kusa. Fita Ummeey ta yi zuwa inda tukunyar girkinta take, ta zubowa Lulun dambun masarar da ta gama yinsa yanzun nan. Se da ta ɗebo mata ruwa a randa sannan ta shigo ɗakin ta ajje a gaban Lulun tace
"Ki ci kin ji ɗiyata.." Bin kwanon ta yi da kallo tana ji kamar ta yi fatali da shi, ita sam ba wannan ne a gabanta ba, burinta kawai ta ganta a gida. Ko ma ba a gida ba ne, ta dena ganinta cikin mutanen dake da alaƙa da Gwani.
"Na ƙoshi.." karo na farko kenan da ta yi magana. Murmushi Ummeey ta yi sannan tace
"A'ah fa.. ban yarda ba. Ki ci ko kaɗan ne idan ya so anjima se ki ƙara.."
"Allah na ƙoshi ni." Ta faɗa tana gyara zamanta. Jin Ummeeyn za ta sake cewa wani abu ya sanyata faɗin
"Na ci abinci ɗazu." Ta faɗa dan ba ta so Ummeeyn ta ƙara yi mata wata maganar a kan abincin, dan sake tunzurata take yi.
"Toh madallah.." Ummeey ta faɗa tana miƙewa dan ficewa daga ɗakin, wataƙila idan ta ga ba ta cikin ɗakin ta samu ta ci ko kaɗan ne. Runtse idanunta Lulu ta yi tana sauke numfashi da sauri da sauri. Haka ba dan ta so ba ta cigaba da zama cikin ɗakin kamar za ta rusa ihu.
Ya yi matuƙar mamaki lokacin da ya shiga ɗakin ya ga ba ta ciki. Mamaki ya kama shi, ka da dai a ce guduwa ta yi? Idan guduwa ta yi ina ta je kenan? Dan ya san dai ba za ta tunkari gida ba idan ta aikata wannan ɗanyen aiki. Ya ɗan fesar da iska daga bakinsa yana lumshe idanunsa. Shi kam ya haɗu da wahala, wannan wace irin mata ce? Miƙewa ya yi kuma da ɗan sauri kamar wanda ya tuna wani abu. Kai tsaye ɗakin Ummeey ya wuce.. A tsakar gida ya tarar da Ummeeyn tana kwashe kayan da ta gama wankesu ɗazu da safe. Da sauri ya ƙarasa ya karɓi kayan a hannunta yana faɗin
"Da kanki kuma Ummeey?"
"Babu komai Affan.. Ka dawo?" Ta faɗa da murmushi a kan fuskarta. Jinjina kai ya yi kana ya amsa da
"Ehh.."
"Ka kyauta da ka dawo yanzu ai.. Ka bar er mutane dama ita kaɗai? Ba ta saba ba se fitowa ta yi, yanzu haka tana ɗakina.."