Sashe 67
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
... Sanye cikin doguwar rigar atamfa ɗinkin rapper. Se wani hijab madaidaici da ta saka a kai. Ta yi wani shahararren kyau kamar ba ita ba. Kitchen ta nufa ta shiga duba abubuwan da take da su. Se ta fito a nutse ta nemi gefen gadon ta zauna. So take ta yi girki tun da dai ta warke, se dai kuma babu kayan miya. Ga dai kayan abincin da ya siyo mata en daidai kamar na me ƙarfinsa. Ta ɗan tura baki da alama wani abin ta tuna cikin zuciyarta. Kawai se ta miƙe ta fice zuwa tsakar gida. Abeey na zaune a kan dadduma yana saurarar wani shiri daga gidan Radio. Gefe guda kuma Ummeey na zaune tana tsince wake a cikin faranti. Daidai lokacin Lulu ta fito daga cikin ɗakin se ta ƙarasa gefen Ummeeyn ta zauna a nutse tace
"Sannu da hutawa Abeey."
"Yawwah sannu dai ɗiyata. Ki na lafiya?"
"Ehh.." ta amsa da hakan tana maida dubanta kan Ummeey.
"Ummeey Barka da wannan lokacin."
"Barkanki dai.." Ummeey ta amsa da murmushi kan fuskarta. Se ta saka hannu ta karɓi farantin hannun Ummeeyn tana faɗin
"Kawo na tsince."
"Daga fitowarki kuma?" Ummeey ta faɗa. Se kawai ta yi murmushi tana soma tsince waken. Girgiza kai Ummeey ta yi har cikin ranta tana sake jin daɗin chanjawar Lulun. Miƙewa ta yi ta je ta zubawa Abeey da ze fita ruwa a buta. Se da ya miƙe sannan Lulu tace
"A dawo lafiya."
"Allah ya sa." Abeey ya amsa shi ma da murmushin kan fuskarsa. Daga haka ya ƙarasa ya ɗauki butar ya yi alwala kafin ya yi sallama da Ummeey ya fice daga gidan. Komawa Ummeey ta yi ta zauna tana ɗan soma jan Lulun da ta yi shiru da hira ko za ta samu ta sake. A daidai lokacin ne kuma Gwani ya yi sallama cikin gidan. Duka suka amsa masa sallamar, se dai ita Lulu ƙasa ƙasa ta yi tata ta cigaba da abin da take yi. Ƙarasawa ya yi ya nemi waje ya zauna Ummeey na masa sannu da zuwa. Ya amsa yana maida dubansa kan Lulu da tun ɗazun yake jin zuciyarsa na azalzalarsa a kan ya kalleta.
"Sannu da zuwa." Ta faɗa kamar wadda aka tilastawa se dai har lokacin ba ta kalle shi ba.
"Yawwah.." Ya amsa a hankali yana ƙoƙarin nemo ƙwayar idanunta dake kallan ƙasa. Sam ya manta ma Ummeey na wajen. Ita dai Ummeey ba tare da tace komai ba ta miƙe ta shige kitchen. A karon farko ta ɗaga kanta saboda tasirin idanunsa da suka mata nauyi a ka. Se kuwa suka haɗa ido. Ya lumshe ido yana ƙoƙarin basarwa. Se dai ya kasa, be san dalili ba. Yau ɗin se yake ganinta kamar wata ta daban, ta yi kyau. Uwa uba ramar nan da ta yi babu ita, ta koma ainahin Afaaf ɗinta. Duk da ya ga sarai ta gan shi yana kallan nata amma hakan be sanya shi fasawa ba. Allah ma ya gani ba ƙaramin farin ciki yake samun kansa a ciki ba duk lokacin da yake kallanta. Shi kansa har mamakin kansa yake yi idan yana wani abun. Abubuwa da dama kuma suna ɗaure masa kai. Musamman yanda yake ji tabbas a cikin ransa ƙaunar Afaaf ɗin yake. Abin da be taɓa zata ba, be kuma tsammani ba. Ya sauke ajiyar zuciya yana ɗauke kansa daga fuskarta lokacin da ya tabbatarwa kansa da ya gamsu da ganinta. Miƙewa ya yi ya wuce ɗakinsu. Se a lokacin ta iya ɗaga kai ta kalli inda ya tashi. Se kuma ta maida kanta kan waken tana faɗin
"Kawai ya yi ta wani kallan mutane.." Ta faɗa tana sake turo baki.
.. Se da ta tabbatar hankalinsa na kan wasan da yake yi. Wanda yana yi yana karatu hankalinsa kwance kuma yana wasansa. Se ta ƙarasa ta shimfiɗa dadduma ta tayar da sallah. Ba ta ankara ba kuwa ya faki idanunta ya fice daga ɗakin a guje.
"Wannan yaro." Ta faɗa tana dafe goshinta lokacin da ta idar da Sallah ta kuma fahimci ya fice daga ɗakin. Ba ta takurawa kanta ba dan ta san wajen waye ze tafi, wato Areef. Mutumin da cikin lokaci ƙanƙani ya shiga ran Little ɗin. Ita har mamaki abin yake bata musamman ita da ta san halin Little. Ga shi ma kuma Bad ɗin dake da bauɗaɗɗen hali. Se ga shi kuma tasu ta zo ɗaya. Cigaba da zama ta yi a kan daddumar dan kuwa ta saka a ranta ko kwana Little ze yi a wajensa ba za ta je ɗaukarsa ba. Se da ta yi karatun Qur'an me yawa sannan ta miƙe daga kan daddumar. Har zuwa dare Little na tare da Bad Man da yau be fita ko ina ba musamman saboda saɓanin da suka samu da Kaseem. Kowa fushi yake da kowa, hakan ne ya sanya shi ba shi space kafin ya waiwaye shi.
Fitowarta daga wanka kenan ta gama shiryawa. Se ta ƙarasa ta nemi wata doguwar riga mara nauyi, wadda iyakacin tsayinta gwuiwarta. Se da ta ɗauki ƙaramin mayafi ma tukunna kafin ta koma gaban mudubin. Saka rigar ta yi, hakan ne ya sanya ta janye towel ɗin jikinta ta ƙasa ta maida shi inda ya kamata. Kafin ta dawo ta ɗauki mayafi da niyyar ɗaure kanta ta samu ta kwanta. Daidai lokacin ya turo ɗakin ba tare da ya nemi izini ba. Da sauri ta ɗaga kai dan ganin ko waye? Se dai tun kafin ya shigo ɗin tuni ƙamshin turarensa me daɗi ya riga shi shigowa cikin ɗakin. Se kuma daga baya ya shigo hannunsa ɗauke da Little. Kai tsaye yanzun ma kan gadon ya nufa ya sauke shi, ya ja masa blanket ya lulluɓe shi kafin ya miƙe. A hankali ya saci kallan inda take hannunta ɗauke da hijab ɗin da ta yi nasarar ɗaukar shi. Duk da ba ta kallansa amma ta san ita yake kalla. Ba ta ɗago ba se ta soma ƙoƙarin kare ƙafafunta dake a buɗe da hannunta. Duk da ba ta so ya fahimci abin da take yi. Tun daga ƙasa ya maida dubansa kanta ya shiga kallanta har saman kanta. Ya ɗan ciji laɓɓansa kafin ya soma takawa. Ta ɗauka fita ze yi daga cikin ɗakin, har tana shirin sauke ajiyar zuciya se tsintar mutum ta yi a gabanta.
"Wai kare jikinki ki ke dan kar na kalla?" Ta tsinci maganarsa, wadda ta sanyata saurin ɗaga idanunta ta kalle shi. Ya ɗaga kansa alamar "Uhmm.." Ya ƙare lokacin da ya zamana tazarar dake tsakaninsu ba ta da yawa ko kaɗan. Gaba ɗaya ta ruɗe. Kunya duk ta baibayeta. Har ga Allah ba ta san ya fahimci abin da take yi ba. Fahimtar yana cigaba da kallanta ne ya sanyata ƙoƙarin zamewa ko da ta ƙasa ne. Se ya sanya hannunsa ya riƙota ta kusa haɗewa da jikinsa.
"Kare jikinki kike dan kar na kalla?" Ya sake tambaya da niyyar ta ba shi amsa. Idan ma kallan ɗan iska take masa, ya gwada mata da gasken haka yake. Ya san hakan ne kaɗai ze sa ta dena masa haka. Se ta yi saurin girgiza kai tana runtse idanunta. Ba ta ankara ba se ta soma jin hucin numfashinsa a kan fuskarta, dalili kenan da ya sanyata buɗe idanunta ta yi saurin jan laɓɓanta ta taune cikin bakinta. So take ta yi magana amma tana tsoro kar ta buɗe bakin a sake maimaita abin da ya faru a karo na biyu. Hakan ne ya sanyata kama bakinta a tsorace. Daidai lokacin da wayar Bad Man ta yi ƙara kenan. Se ya saketa da sauri yana jin wani ɓacin rai na taso masa. Juyawa ya yi kawai ya fice daga ɗakin ba tare da ya sake kallan inda take ba.
"Bro ina son magana da kai." Kaseem ya faɗa muryarsa a cushe. Kamar ba ze ce komai ba dan se da ya ɗauki sakanni masu yawa, hannunsa na cikin tulin sumar kansa yana hautsinawa.
"Ina ji."
"Ka faɗa min ya aka yi ka auri Afrah?" Shiru Bad ɗin ya yi dan so yake ya fahimci maganar sosai kafin yace wani abu. Zuwa can ransa ya soma ɓaci. Wani irin ɓacin rai da ya haɗu da na yanzu.
"Kaseem.. ka kama kanka. Ka na nema fa ka wuce gona da iri. Na barka ranar nan ba tare da na illataka ba, hakan be isheka ba? So daga rana irin ta yau kar ka sake magana a kan matata, idan ba haka ba zan illataka.." Daga haka be jira Kaseem ɗin yace komai ba ya kashe wayar. Ya nemi waje ya zauna, har lokacin hannunsa na cikin sumar kansa.
"Wane irin mutum ne Kaseem?" Ya tambayi kansa. Be taɓa tunanin haka yake ba. Ya kuma saka a ransa duk ranar da ya sake yi masa magana a kan yarinyar nan ze ga abin da ze masa. Se kuma can ya yi shiru yana nazarin abubuwan da ya faɗawa Kaseem ɗin da kuma abubuwan da shi kansa yake yi. Me ya shiga kansa ne? Me yake damunsa? Ya ja tsaki yana miƙewa ya faɗa toilet dan watsa ruwa a jikinsa.
.. Washegari su Ammi suka ɗaga zuwa Kano. Saboda gidan Alhaji Matawallen ba ɓoyayye ba ne kai tsaye nan suka tari mota, Ammi ta masa bayanin inda ze kai su. Se aka yi sa'a me napep ɗin irin wayayyen nan ne, ya ɗauke su, se gidan Alhaji Matawalle. A can baya ya yi parking na motarsa yace
"Toh mu nan ne bodarmu fa Hajiya. Se dai ku sauka ku ƙarasa."
"Toh mun gode." Ammi ce ta fara sauka, ta haɗa keken Maimuna kafin ita da Talatuwa suka ɗora Maimunan a kai. Ammi ta saita duk wani abu da ya kamata jikin keken sannan ta kalli mutumin dake nuna mata gidan.
"Sannu da hutawa Abeey."
"Yawwah sannu dai ɗiyata. Ki na lafiya?"
"Ehh.." ta amsa da hakan tana maida dubanta kan Ummeey.
"Ummeey Barka da wannan lokacin."
"Barkanki dai.." Ummeey ta amsa da murmushi kan fuskarta. Se ta saka hannu ta karɓi farantin hannun Ummeeyn tana faɗin
"Kawo na tsince."
"Daga fitowarki kuma?" Ummeey ta faɗa. Se kawai ta yi murmushi tana soma tsince waken. Girgiza kai Ummeey ta yi har cikin ranta tana sake jin daɗin chanjawar Lulun. Miƙewa ta yi ta je ta zubawa Abeey da ze fita ruwa a buta. Se da ya miƙe sannan Lulu tace
"A dawo lafiya."
"Allah ya sa." Abeey ya amsa shi ma da murmushin kan fuskarsa. Daga haka ya ƙarasa ya ɗauki butar ya yi alwala kafin ya yi sallama da Ummeey ya fice daga gidan. Komawa Ummeey ta yi ta zauna tana ɗan soma jan Lulun da ta yi shiru da hira ko za ta samu ta sake. A daidai lokacin ne kuma Gwani ya yi sallama cikin gidan. Duka suka amsa masa sallamar, se dai ita Lulu ƙasa ƙasa ta yi tata ta cigaba da abin da take yi. Ƙarasawa ya yi ya nemi waje ya zauna Ummeey na masa sannu da zuwa. Ya amsa yana maida dubansa kan Lulu da tun ɗazun yake jin zuciyarsa na azalzalarsa a kan ya kalleta.
"Sannu da zuwa." Ta faɗa kamar wadda aka tilastawa se dai har lokacin ba ta kalle shi ba.
"Yawwah.." Ya amsa a hankali yana ƙoƙarin nemo ƙwayar idanunta dake kallan ƙasa. Sam ya manta ma Ummeey na wajen. Ita dai Ummeey ba tare da tace komai ba ta miƙe ta shige kitchen. A karon farko ta ɗaga kanta saboda tasirin idanunsa da suka mata nauyi a ka. Se kuwa suka haɗa ido. Ya lumshe ido yana ƙoƙarin basarwa. Se dai ya kasa, be san dalili ba. Yau ɗin se yake ganinta kamar wata ta daban, ta yi kyau. Uwa uba ramar nan da ta yi babu ita, ta koma ainahin Afaaf ɗinta. Duk da ya ga sarai ta gan shi yana kallan nata amma hakan be sanya shi fasawa ba. Allah ma ya gani ba ƙaramin farin ciki yake samun kansa a ciki ba duk lokacin da yake kallanta. Shi kansa har mamakin kansa yake yi idan yana wani abun. Abubuwa da dama kuma suna ɗaure masa kai. Musamman yanda yake ji tabbas a cikin ransa ƙaunar Afaaf ɗin yake. Abin da be taɓa zata ba, be kuma tsammani ba. Ya sauke ajiyar zuciya yana ɗauke kansa daga fuskarta lokacin da ya tabbatarwa kansa da ya gamsu da ganinta. Miƙewa ya yi ya wuce ɗakinsu. Se a lokacin ta iya ɗaga kai ta kalli inda ya tashi. Se kuma ta maida kanta kan waken tana faɗin
"Kawai ya yi ta wani kallan mutane.." Ta faɗa tana sake turo baki.
.. Se da ta tabbatar hankalinsa na kan wasan da yake yi. Wanda yana yi yana karatu hankalinsa kwance kuma yana wasansa. Se ta ƙarasa ta shimfiɗa dadduma ta tayar da sallah. Ba ta ankara ba kuwa ya faki idanunta ya fice daga ɗakin a guje.
"Wannan yaro." Ta faɗa tana dafe goshinta lokacin da ta idar da Sallah ta kuma fahimci ya fice daga ɗakin. Ba ta takurawa kanta ba dan ta san wajen waye ze tafi, wato Areef. Mutumin da cikin lokaci ƙanƙani ya shiga ran Little ɗin. Ita har mamaki abin yake bata musamman ita da ta san halin Little. Ga shi ma kuma Bad ɗin dake da bauɗaɗɗen hali. Se ga shi kuma tasu ta zo ɗaya. Cigaba da zama ta yi a kan daddumar dan kuwa ta saka a ranta ko kwana Little ze yi a wajensa ba za ta je ɗaukarsa ba. Se da ta yi karatun Qur'an me yawa sannan ta miƙe daga kan daddumar. Har zuwa dare Little na tare da Bad Man da yau be fita ko ina ba musamman saboda saɓanin da suka samu da Kaseem. Kowa fushi yake da kowa, hakan ne ya sanya shi ba shi space kafin ya waiwaye shi.
Fitowarta daga wanka kenan ta gama shiryawa. Se ta ƙarasa ta nemi wata doguwar riga mara nauyi, wadda iyakacin tsayinta gwuiwarta. Se da ta ɗauki ƙaramin mayafi ma tukunna kafin ta koma gaban mudubin. Saka rigar ta yi, hakan ne ya sanya ta janye towel ɗin jikinta ta ƙasa ta maida shi inda ya kamata. Kafin ta dawo ta ɗauki mayafi da niyyar ɗaure kanta ta samu ta kwanta. Daidai lokacin ya turo ɗakin ba tare da ya nemi izini ba. Da sauri ta ɗaga kai dan ganin ko waye? Se dai tun kafin ya shigo ɗin tuni ƙamshin turarensa me daɗi ya riga shi shigowa cikin ɗakin. Se kuma daga baya ya shigo hannunsa ɗauke da Little. Kai tsaye yanzun ma kan gadon ya nufa ya sauke shi, ya ja masa blanket ya lulluɓe shi kafin ya miƙe. A hankali ya saci kallan inda take hannunta ɗauke da hijab ɗin da ta yi nasarar ɗaukar shi. Duk da ba ta kallansa amma ta san ita yake kalla. Ba ta ɗago ba se ta soma ƙoƙarin kare ƙafafunta dake a buɗe da hannunta. Duk da ba ta so ya fahimci abin da take yi. Tun daga ƙasa ya maida dubansa kanta ya shiga kallanta har saman kanta. Ya ɗan ciji laɓɓansa kafin ya soma takawa. Ta ɗauka fita ze yi daga cikin ɗakin, har tana shirin sauke ajiyar zuciya se tsintar mutum ta yi a gabanta.
"Wai kare jikinki ki ke dan kar na kalla?" Ta tsinci maganarsa, wadda ta sanyata saurin ɗaga idanunta ta kalle shi. Ya ɗaga kansa alamar "Uhmm.." Ya ƙare lokacin da ya zamana tazarar dake tsakaninsu ba ta da yawa ko kaɗan. Gaba ɗaya ta ruɗe. Kunya duk ta baibayeta. Har ga Allah ba ta san ya fahimci abin da take yi ba. Fahimtar yana cigaba da kallanta ne ya sanyata ƙoƙarin zamewa ko da ta ƙasa ne. Se ya sanya hannunsa ya riƙota ta kusa haɗewa da jikinsa.
"Kare jikinki kike dan kar na kalla?" Ya sake tambaya da niyyar ta ba shi amsa. Idan ma kallan ɗan iska take masa, ya gwada mata da gasken haka yake. Ya san hakan ne kaɗai ze sa ta dena masa haka. Se ta yi saurin girgiza kai tana runtse idanunta. Ba ta ankara ba se ta soma jin hucin numfashinsa a kan fuskarta, dalili kenan da ya sanyata buɗe idanunta ta yi saurin jan laɓɓanta ta taune cikin bakinta. So take ta yi magana amma tana tsoro kar ta buɗe bakin a sake maimaita abin da ya faru a karo na biyu. Hakan ne ya sanyata kama bakinta a tsorace. Daidai lokacin da wayar Bad Man ta yi ƙara kenan. Se ya saketa da sauri yana jin wani ɓacin rai na taso masa. Juyawa ya yi kawai ya fice daga ɗakin ba tare da ya sake kallan inda take ba.
"Bro ina son magana da kai." Kaseem ya faɗa muryarsa a cushe. Kamar ba ze ce komai ba dan se da ya ɗauki sakanni masu yawa, hannunsa na cikin tulin sumar kansa yana hautsinawa.
"Ina ji."
"Ka faɗa min ya aka yi ka auri Afrah?" Shiru Bad ɗin ya yi dan so yake ya fahimci maganar sosai kafin yace wani abu. Zuwa can ransa ya soma ɓaci. Wani irin ɓacin rai da ya haɗu da na yanzu.
"Kaseem.. ka kama kanka. Ka na nema fa ka wuce gona da iri. Na barka ranar nan ba tare da na illataka ba, hakan be isheka ba? So daga rana irin ta yau kar ka sake magana a kan matata, idan ba haka ba zan illataka.." Daga haka be jira Kaseem ɗin yace komai ba ya kashe wayar. Ya nemi waje ya zauna, har lokacin hannunsa na cikin sumar kansa.
"Wane irin mutum ne Kaseem?" Ya tambayi kansa. Be taɓa tunanin haka yake ba. Ya kuma saka a ransa duk ranar da ya sake yi masa magana a kan yarinyar nan ze ga abin da ze masa. Se kuma can ya yi shiru yana nazarin abubuwan da ya faɗawa Kaseem ɗin da kuma abubuwan da shi kansa yake yi. Me ya shiga kansa ne? Me yake damunsa? Ya ja tsaki yana miƙewa ya faɗa toilet dan watsa ruwa a jikinsa.
.. Washegari su Ammi suka ɗaga zuwa Kano. Saboda gidan Alhaji Matawallen ba ɓoyayye ba ne kai tsaye nan suka tari mota, Ammi ta masa bayanin inda ze kai su. Se aka yi sa'a me napep ɗin irin wayayyen nan ne, ya ɗauke su, se gidan Alhaji Matawalle. A can baya ya yi parking na motarsa yace
"Toh mu nan ne bodarmu fa Hajiya. Se dai ku sauka ku ƙarasa."
"Toh mun gode." Ammi ce ta fara sauka, ta haɗa keken Maimuna kafin ita da Talatuwa suka ɗora Maimunan a kai. Ammi ta saita duk wani abu da ya kamata jikin keken sannan ta kalli mutumin dake nuna mata gidan.