← Book details A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 41 OF 122

Sashe 41

A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Taurin kai koh?" Yanda ya riƙe mata hannun ba ƙaramin zafi ta ji ba. Ta kuma fahimci ba ta da wata mafita illah ta yi abin da ya faɗa ɗin, dan haka se kawai ta ɗaga idanunta ta sanya a kan fuskarsa. Gaba ɗaya idanunsa ya ɗauka ya ɗora a kan tata fuskar. Se ma ya shigar da idanunsa cikin nata dan saƙon da ze faɗa mata ya fi shigarta. Karo na farko kenan da irin wannan kallon ya taɓa haɗa su. Har ta numfashinsu se ya shiga haɗewa da na juna. Ruwan da har yanzu ke jikin gargasar dake ƙirjinsa har sakkowa yake a kan hijab ɗin jikinta. Duk wani sauka da ruwan ze yi ji take kamar da zuciyarta yake sauka, saboda yanda yake sauka tare da bugun zuciyarta. So take ta ɗauke idanun nata amma ya ƙi ba ta ko da ƙaramar dama ce.

"Tsoronki wannan jinin da ke ta zuba koh? Toh yanzu babu shi.. Saboda haka ki buɗe kunnanki da kyau ki ji ni.. Idan kika sake na ji wata magana a kan abin da kika gani, ko a wajen waye.. ko ke ce kika faɗa ko ba ke ba ce ba damuwata ba ce..hukuncin da zan yi a kan ki ne.. Kin ji koh?" Ya yi maganar yana jan kunnensa guda ɗaya. Jinjina kai ta yi dan har ga Allah ta gaji da kallan cikin ƙwayar idanunsa haka nan. Cigaba ya yi da kallanta ba kamar kallan ɗazu ba, haka nan kawai ta fahimci abin da yake nufi, dan haka ta buɗe baki da ƙyar tace

"Ehh.." Da ƙarfi ya sake ta yana miƙewa ya bar wajen. Ta saki ajiyar zuciya har lokacin bugun zuciyarta be saitu ba ta miƙe da ƙyar ta fice daga ɗakin hannunta riƙe da ƙafarta me ciwon.

Ajiyar zuciya ta sake saukewa a karo na barkatai lokacin da ta ganta a cikin ɗakinta. Da ƙyar ta ja ƙafafunta ta nemi waje ta zauna. Duk da yanda ƙafarta ke zugi amma farin cikinta ɗaya da ta fito daga ɗakin. Ta kai wajen minti 10 a haka tana cigaba da kokawa da saita numfashinta kafin ya dawo daidai.

.... "Kin shigo kenan?" Daddy ya faɗa lokacin da yake neman waje ze zauna kan kujera.

"Ehh 'Yallaɓai na dawo."

"Toh Madallah.. ya batun duba lafiyarki kuwa?"

"Yana nan.."

"Amma dai ba ki manta lokacin ba koh? Anya ma kuwa kina lissafi.." Murmushi Mom ta yi tace

"Haba dai Daddyn Areef ta ya ya za a yi na manta? Ina sane fa." Shi ma murmushin Daddy ya yi yana girgiza kai sannan yace

"Yanda na faɗa kuwa haka ne. Domin da ki na sane da lokacin zuwanki da tuni yanzu haka kin fara shirye shirye."

"Haba 'Yallaɓai se ka ce me yin tafiya cikin satin nan?"

"Toh kin gani ba? Cikin satin nan ne tafiyar taki, na ga ba ki fara shiri ba shi ya sa na tambaya." Cike da mamaki tace

"Wannan satin kuma? Ya aka yi na ɓace a lissafi.."

"Tsufa mana.." Ya ba ta amsa cikin barkwanci. Yaƙe kawai ta yi dan ita tuni hankalinta ya tafi wani wajen. Se ta miƙe a sanyaye tace

"Bari na je toh 'Yallaɓai. Godiya da tunasarwa." Ba ta jira amsarsa ba ta fice daga cikin ɗakin. Binta ya yi da kallo yana mamakin yanda yanayinta ya chanja kamar ba maganar neman lafiyarta ake yi ba. Ya girgiza kai kawai.

Tun kafin ta ƙarasa cikin ɗakinta ta soma kiran number ƙanwarta Makiyya. Babu daɗewa kuwa ta ɗaga.

"Hajiya Yaya ikon Allah.. kafin Allah ba na mutum ba."

"Kin ga riƙe kirarinki na san dalilinki na hakan."

"Haka za mu yi da ke?" Aunt Makiyy ta faɗa.

"Kin ga ba wannan ba.. Ashe wai cikin satin nan ne zan koma ganin likita.."

"Toh fa! Har lokacin ya yi?"

"Wallahi kuwa.. yanzun nan Daddyn Areef ke tuna min." Mom ta bata amsa.

"Toh yanzu me ye abin yi?" Aunt Makiyy ta tambaya. Shiru Mom ta yi na en wasu mintuna kafin ta sauke ajiyar zuciya tace

"So nake na kora yarinyar nan gida kafin na bar ƙasar nan. Dan matuƙar ban yi hakan ba hankalina ba ze taɓa kwanciya ba."

"Ehh toh da gaskiyarki Yaya.. se dai ni a ganina ba haka ya kamata ki yi ba. Me ze hana shi kansa Areef ɗin ki tura shi wata ƙasar ya yi adadin kwanakin da za ki yi a can? Idan ya so se ku dawo tare. Kin ga ku na dawowa se a san abin da za a yi dan zuwa lokacin ni ma na dawo." Shiru Mom ta yi na en wasu sakanni. Se kuma can ta shiga jinjina kai cike da gamsuwa da abin da Aunt Makiyyn ta faɗa.

"Hakan ya yi. Zan jarraba na gani. Duk yanda ake ciki zan kira ki ki ji.." Murmushi Aunt Makiyy ta yi tace

"Yawwah.. Allah ya taimaka.."

"Ameen." Mom ta amsa da hakan sannan suka yi sallama.

... Ƙarasawa Baba Atine ta yi cikin ɗakin hango Didi da ta yi zaune a kan gado riƙe da ƙafarta da ke nannaɗe da bandage tana kalla.

"Subhanallahi me ya same ki Afrah?" Ta yi maganar lokacin da ta isa inda Didin take. Da sauri ta sauke ƙafarta dan ko jin shigowar Baba Atinen ba ta yi ba.

"Me ya same ki 'yata?" Baba Atine ta sake faɗa a karo na biyu. Idanunta da suka yi rau rau ta ɗan lumshe kafin ta buɗe, ba dan ta so ba tace

"Bigewa na yi.."

"Bigewa kuma? A ina?" Baba Atine ta faɗa cike da kulawa, dan har ga Allah ta tsorata da ganin bandage ɗin a ƙafar Didin. Shiru Didin ta yi tana tunanin me za tace wa Baba Atinen, dan ba ta so ta faɗa mata a inda ta taka saboda tuna gargaɗin da Bad Man ya mata. Gefe guda kuma ba ta so ta yi ƙarya. Kafin ta gama tsara abin da za ta faɗa ɗin Baba Atine ta miƙe ta fice daga ɗakin. Wata ƙatuwar ajiyar zuciya Didi ta sauke ganin Baba Atinen ta fita daga ɗakin. Ko babu komai kafin su sake haɗuwa ta san me za ta ce mata. Lumshe idanunta ta yi tana jinginar da bayanta a jikin gadon da take kai har lokacin hannunta na kan ƙafarta da take ji tana mata zugi.

Tana nan zaune bayan wajen minti 10 har baccin wahala ya fara ɗaukarta ta ji an turo ƙofar ɗakin. Da yake baccin be yi nisa ba ya sa ta buɗe manyan brown eyes ɗinta da suka ɗan yi ja saboda baccin da ya fara ɗaukarta. Baba Atine na baya yayin da Mommah ke gaba kamar kodayaushe sanye cikin hamshaƙiyar shiga da kodayaushe take matuƙar karɓar madaidaicin jikinta. Da sallama suka shiga ɗakin kamar yanda Mommah ke gaba, yanzun ma ita ce ta fara isa inda Didin take. Ganin Mommahn da ta yi ba tare da ta tsammata ba ya sanyata miƙewa zaune da sauri ta zauna a kan gadon. Gefen gadon Mommah ta samu ta zauna cikin kulawa tace

"Daughter me ya same ki?" Ta yi maganar tana sanya hannunta ta ɗago ƙafar da idanunta suka sauka a kai.

"Ya salaam garin yaya haka ta faru? Me ya samu ƙafarki?" Mommah ta faɗa yanayin fuskarta na nuna yanda tashin hankalin da ta shiga lokacin da ta yi tozali da ƙafar Didin. Lumshe idanunta Didi ta yi tana jin lokacin faɗin gaskiyar ya yi, dan Mommahn ta fi ƙarfin ta yi mata ƙarya. Dan haka cikin sanyi tace

"Kwalba na taka.."

"Subhanallahi kwalba kuma?" Mommah ta faɗa tana kallan Didin cike da mamaki. Jinjina kai ta yi kafin tace komai Mommahn ta sake faɗin

"A ina kika taka? Kwalbar me ye ne?" Ta tambaya cikin tsare Didin da idanunta. A yanzu kam ba ta ji za ta iya faɗa mata kwalbar giyar Bad Man ta taka cikin ɗakinsa. Komai lalacewarsa komai kuma rashin kirkinsa a gareta mijinta ne, idan ya zamana ta faɗa gaskiyar abin da ta taka hakan na nufin ta tona masa asiri kenan? Bayan ta san illar hakan.

"Kwalbar turare ce.." Ba tare da ta kammala harhaɗa zancen ba ta yi ƙarfin halin faɗa.

"Ya ilahy.. shi ne ba ki faɗa min ba Daughter? Kin kyauta kenan? Wannan bandage ɗin kuma a ina kika samo shi?" Dukka Mommah ta haɗa tambayar ta yi ta lokaci ɗaya. Ba ta san lokacin da murmushi ya ƙwace mata ba duk da jin jerin gwanon tambayoyin da Mommahn ta jero mata. A kullum a kodayaushe mutuncin Mommahn ƙaruwa yake yi a wajenta, ƙaunarta kuma daɗuwa take yi a cikin ranta.

"Ki yi haƙuri Mommah.." Ta faɗa a sanyaye.

"Naa ji.. shi ne kuma har da ɗaura bandage a ƙafarki. Wato ba dan Atine ta gani ba da shi kenan se dai ki yi shiru ba tare da sanin illar hakan ba? Kwalba fa kika taka Daughter."

"Ki yi haƙuri Mommah.. ba ni na saka bandage ɗin ba.. shi ne ya saka min." Ta faɗa lokacin da muryarta ta raunana saboda fahimtar da ta yi Mommahn ba ta ji daɗin ɓoye matan da ta yi ba.

"Waye?" Mommah ta tambaya dan kwata kwata ba ta kawo Bad Man ba saboda sanin hali. Rasa sunan da za ta faɗa ta yi, se ta shiga kame kame kawai.

"Wai Areef kike nufi?" Baba Atine ta faɗa lokacin da ta ƙaraso kusa da su. Se ta jinjina kai kafin a hankali ta buɗe bakinta da ƙyar tace

"Ehh.." Wani ƙayataccen murmushi Mommah ta yi tana jin wani irin sanyi har cikin ranta.

"Ma Sha Allah, Alhamdulillah.. Allah ya ƙara ƙara haɗa kan ku." Baba Atine ta faɗa.

"Ameen Ameen.." Mommah ta faɗa da murmushi a kan fuskarta.

"Toh Alhamdulillah.. Amma duk da haka tashi mu je asibiti.."

"Mommah ba.."

"Tashi na ce.." Mommah ta katse Didi da faɗin haka. Ba ta sake cewa komai ba se miƙewar da ta yi da ƙyar, dan ta kasa taka ƙafarta. Cike da tausayawa Mommah ke binta da kallo a ranta tana sake addu'ar Allah ya daidaita tsakanin Didin da Areef.

Da taimakon Baba Atine suka fita daga ɗakin tana riƙe da Didi. dauriya kawai take yi dan ita kaɗai ta san yanda take ji a ƙafar tata.
Chapter 41 · 0% Book details