Sashe 89
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Toh za su ji In Sha Allah.. Ku gaida gida." Ta ƙarasa maganar tana kallan Mami, ba kuma ta jira tace wani abu ba ta fice daga ɗakin. Dan kuwa ita yanzu ta dawo daga rakiyar Mamin, tun lokacin da ta ji labarin abin da ya faru na son kashewa Lulu aure. Dalili kenan da ya sa yanzu take kaffa kaffa da ita. Harara Mami ta bi Ammi da ita a kan laɓɓanta tana furta
"Munafuka." Se da Ammin ta fice gaba ɗaya sannan ta maida dubanta kan Abba tace
"Uhmm da ma Yaya wajenka na zo." Gyara zama Abba ya yi yana kallanta yace
"Ikon Allah! Wajena kuma?" Se ta jinjina kai kafin ta cigaba da faɗin
"Ehh.. Da ma a kan Lulu ne.." Tun da ya ji sunan da ta ambata se ya cigaba da kallanta. Ya yin da ita ta ƙi yarda ta kalle shi. Kawai se ta cigaba da faɗin
"Zuwa na yi na sake baka haƙuri don Allah.. Ina so ne na gyara alaƙarmu ta koma kamar ta da.. Na ji abin alkhairin da ya same su, shi ya sa na ce tun da zafi zafi ni ma na je na musu fatan alkhairi kar a ce ko baƙin ciki nake musu." Daga haka ta yi shiru tana ɗan murmushi. Girgiza kai Abba ya yi, shi kam sam ya rasa gane halin Mamin, wato son zuciyarta ya mata yawa.
"Kamar na riga na faɗa miki ka da na sake jin maganaki a kan Lulu ko abin da ya shafi gidanta ba koh?. Sadiya ban san kuma me kike so da ni ba, bayan ƙoƙarin kashe auren Afaaf da kika yi duk da haka kin kuɓuta daga hannun kuliya hakan be ishe ki ba? Ba zan yanke alaƙarmu ba, amma ki sani tabbas dole mu yi nesa da juna saboda samun zaman lafiya. Afaaf kuwa na riga na rabaki da ita ki sake saka wannan a ranki. Kar kuma na ji labarin kin je gidan nan idan ba haka ba har abada zan datse alaƙarmu da ke ne Sadiya.." Ɗaga kai ta yi ta kalli Abban, ba ta taɓa tunanin hakan daga gare shi ba, dan ta san halinsa a wasu lokutan yana da sauƙin kai, shi ya sa ta yi tunanin ze tausaya mata ya barta su cigaba da alaƙa da Lulu, ko dan wannan abin alkhairin da ya same su. Se ga shi yana faɗin ze yanke alaƙarsu.
"Haba Yaya don Allah? An gama maganar komai fa. An kashe komai wallahi. Yanzu babu abin da ze kai ni wajen Lulu da danginta se alkhairi. Don Allah kar ka ce haka."
"Na gama maganata.. Ruwanki ki je gidan Afaaf, ruwanki ki koma gida.. Zaɓi ya rage gare ki.." Daga haka Abba ya miƙe ba tare da ya jira tace komai ba ya fice daga ɗakin.
"Ke ma Mami ƙi haƙura amma kin ƙi.. Idan kuma kin zaɓi Lulu ne a kan Abba shi kenan."
"Dallah can tashi mu tafi.. Er banza me baƙin hali. Maimakon ki ƙarfafa min gwuiwa, a'ah ke kullum ba ki san wannan ba." Mami ta faɗa tana jan hannun Jadwa suka fice daga ɗakin kamar za su tashi sama. Haka ta din ga sirbiɗiɗin masifa ita kaɗai kai ka ce za ta ari baki ne..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO72*
___ A ɗaya ɓangaren kuwa babu daɗewa Ammi ta isa gidan Alhaji Matawallen. A palourn Mommah ta sauka, inda nan Ummeey ta dawo bayan gama gaisawa da matan abokan Daddy. Didi, Lulu, Little har ma da Baba Atine duka suna zaune cikin ɗakin. Baba Atine da Ummeey suna ɗan hira jefi jefi. Ammi ta yi sallama cikin ɗakin. Kamar a mafarki suka ji sallamar Ammin, gaba ɗaya suka ɗaga kai suka kalleta, dan tabbatar da ita ɗin ce ba kunnensu ke jiyo musu ba daidai ba. Gaba ɗaya manta a inda suke suka yi, suka tafi da gudu suka rungumeta lokaci ɗaya suna furta
"Ammi.." Ita ma rungumesun ta yi cike da kewarsu. Ummeey da ke zaune ta yi murmushi tana kallansu. Da ƙyar suka iya sakin Ammin kafin suka tako zuwa cikin ɗakin. Se dai duk da haka sun kaasa sakin hannun Ammin. Shi kam Little da ma tuni ya riƙo mayafin Ammin saboda ma kar ta tafi ta bar shi. Neman waje suka yi suka zauna. Ammi suka gaisa da Ummeey sosai kasancewar sun shaida juna. Tuni har Little ya fara yi wa Ammi hira, en biyunta na zagaye da ita kamar za su haɗiyeta. Daidai lokacin Mommah ta shigo cikin ɗakin, ta yi matuƙar kyau cikin wani tsadadden lace, ta yi ɗaurin da ya dace da shigarta, wanda ya zauna ya mata kyau sosai. Shi kansa mayafin da ta ɗora a kan kayan ya yi mugun kyau, ya kuma hau da lace ɗin. A taƙaice dai duk abin da Mommahn ta saka sun mata kyau, sun kuma karɓi jikinta sosai. Kai idan ka ganta ba za ka ce ta ajje 'ya'ya kamarsu Gwani ba. Ƙarasawa ta yi ta nemi waje ta zauna a kan kujera, tana kallan Ammi da murmushi kan fuskarta tace
"Barka da ƙarasowa."
"Yawwah.. barka dai.. Ya jama'a?"
"Alhamdulillah.."
"Madallah.." Sake yi mata jajen abin da ya faru Ammi ta yi. Mommah ta sake mata godiya tana kuma amsa addu'ar da Anmin ta yi a kan 'ya'yan nata.
Sosai Ammi ta yi mamaki lokacin da ta ji cewar Gwani Affan shi ne ɗan Mommahn. Wato dai kenan mazajen da Lulu da Didi suka aura en biyu ne. Se ga shi Allah Ya haɗa su sun auri juna ba tare da sanin da akwai babbar alaƙa a tsakaninsu ba. Haka ta cigaba da jajanta al'amarin kafin daga bisani ta cigaba da biyewa en biyunta da ke ta kawo mata hira. Se ta biye musu musamman da Mommah da Ummeey suka fita daga ɗakin, se ya kasance saura su kaɗai. Dan haka sosai suka yi hirar da suka daɗe ba su yita ba. A nan ne kuma cikin hikima ta din ga fahimtar wasu abubuwan. Sosai ta ji daɗi yanda duk cikinsu babu wanda ya yi ƙorafi a kan auransa, hakan ba ƙaramin faranta mata rai ya yi ba musamman idan aka yi duba da farkon auren. Kamar ko yaushe haka cikin dabara ta cigaba da yi musu faɗa, da ba su shawarwari, gami da sake ji daga bakinsu ko suna da wata matsalar. Haka dai yammacin ya kasance musu cikin farin ciki. Se bayan magribh sannan Ammi ta fara shirin tafiya saboda Abba da ya zo ɗaukarta, da kuma ta ya su Daddy farin cikin abin da ya faru.
"Ammi tare za mu tafi koh?" Little ya faɗa yana kallanta.
"Aou har ka gaji da nan ɗin?" Ta tambaya tana murmushi, duk da da ma ita ma da niyyar tafiya da autanta ta zo. Se ya matso kusa da ita ya rungume hannunta yana cuno baki yace
"Ni dai ke zan bi."
"Iyee.. Lallai ma Little.. Za ka ƙara nemana ne." Didi ta faɗa tana karkaɗa kai.
"Bare kuma ni." Lulu ta faɗa tana harararsa. Shi dai be ce komai ba se sake rungume Ammin da ya yi. Ta yi murmushi dan ta san kwana biyun da ya yi ba ya ganinta ne ya sanya shi kewarta, har ya ƙi zama duk da ga en uwansa cikin gidan.
"Ni ma da ma da kai zan tafi Autana.." Ammi ta faɗa tana sake rungumo shi.
"Kai Ammi.." Suka haɗa baki wajen faɗin hakan. Har compound suka raka Ammi cike da kewa. Ba su san da zuwan Abba ba se da suka raka Ammi har inda motarsa take.
"Laaa Abba.." Suka kusan faɗa a tare cike da tsananin farin ciki.
"Na'am Afaaf.. Afrah.." Abba ya faɗa yana murmushi shi ma cike da farin cikin ganin 'ya'yan nasa. Gaisawa suka yi sosai. Abba dan farin ciki ji ya yi kamar ya yi me. Ya san halin Didi, da ma ba shi da matsala da ita. Se dai a yanda ya ga Lulun babu damuwa ko kaɗan a tare da ita ya sa ya fahimci sun yi nasara. Da alama kuma ta karɓi auren, ta haƙura. Sosai hakan ya faranta masa rai. Ya yi musu faɗa sosai da kuma nasiha sannan suka yi sallama suka tafi ya yin da su kuma suka koma cikin gidan. Duk se suka ji zaman gidan babu daɗi, yau ɗin se ta zama ta tuna musu da rayuwarsu ta gida. Ba su wani zauna hira ba tun kafin dare ya yi sosai duk suka kwanta bacci.
... "Wai me ke damunki ne Lulu? Ba za ki faɗa min ba kin gwammace ki zauna da yunwa?" Girgiza kai Lulu ta yi kafin tace tana yamutsa fuska
"Zuciyata tashi take Didi.. Ba na son ƙamshin wallahi." Ta ƙarasa maganar tana sake yamutse fuska. Sauke numfashi Didi ta yi kafin tace
"Toh ki gwada ci ko yaya ne Uhmm?" Ta yi maganar cikin rarrashi tana matsar da plate ɗin kusa da Lulu. Da sauri ta saka hannu ta janye plate ɗin ta maida shi inda Didi ta ɗakko tace duk ranta babu daɗi
"Wallahi ba zan iya ci ba Didi."
"Yau na ga ikon Allah ni er nan.. Toh me ye za ki ci?"
"Ba komai.." Ta faɗa tana turo baki. Daidai lokacin Mommah ta shigo cikin ɗakin. Ta dubi abincin da ke gabansu tace
"Wai har yanzu ba ku ci ba?" Ta tambaya da mamaki tana kallansu su duka.
"Mommah cewa ta yi wai ba za ta ci ba." In ji Didi. Se ta maida dubanta kan Lulu tace
"Me ya faru? Me ya sa ba za ki ci ba?" Gyara zamanta Lulu ta yi kamar me shirin yin doguwar magana, tace a hankali
"Ba zan iya ci ba Mommah.." Neman waje Mommah ta yi ta zauna a kusa da ita. Ta dafata sannan tace
"Me ya sa Uhmm?" Ɗaga kai ta yi ta kalleta kafin ta maida ƙasa tace
"Ba komai.. Ƙamshin ne ba na so." Kallanta Mommah ta cigaba da yi kamin can tace
"Toh shi kenan.. A dafa miki wani abun?" Girgiza kai Lulu ta yi. Mommah ta sake faɗin
"Munafuka." Se da Ammin ta fice gaba ɗaya sannan ta maida dubanta kan Abba tace
"Uhmm da ma Yaya wajenka na zo." Gyara zama Abba ya yi yana kallanta yace
"Ikon Allah! Wajena kuma?" Se ta jinjina kai kafin ta cigaba da faɗin
"Ehh.. Da ma a kan Lulu ne.." Tun da ya ji sunan da ta ambata se ya cigaba da kallanta. Ya yin da ita ta ƙi yarda ta kalle shi. Kawai se ta cigaba da faɗin
"Zuwa na yi na sake baka haƙuri don Allah.. Ina so ne na gyara alaƙarmu ta koma kamar ta da.. Na ji abin alkhairin da ya same su, shi ya sa na ce tun da zafi zafi ni ma na je na musu fatan alkhairi kar a ce ko baƙin ciki nake musu." Daga haka ta yi shiru tana ɗan murmushi. Girgiza kai Abba ya yi, shi kam sam ya rasa gane halin Mamin, wato son zuciyarta ya mata yawa.
"Kamar na riga na faɗa miki ka da na sake jin maganaki a kan Lulu ko abin da ya shafi gidanta ba koh?. Sadiya ban san kuma me kike so da ni ba, bayan ƙoƙarin kashe auren Afaaf da kika yi duk da haka kin kuɓuta daga hannun kuliya hakan be ishe ki ba? Ba zan yanke alaƙarmu ba, amma ki sani tabbas dole mu yi nesa da juna saboda samun zaman lafiya. Afaaf kuwa na riga na rabaki da ita ki sake saka wannan a ranki. Kar kuma na ji labarin kin je gidan nan idan ba haka ba har abada zan datse alaƙarmu da ke ne Sadiya.." Ɗaga kai ta yi ta kalli Abban, ba ta taɓa tunanin hakan daga gare shi ba, dan ta san halinsa a wasu lokutan yana da sauƙin kai, shi ya sa ta yi tunanin ze tausaya mata ya barta su cigaba da alaƙa da Lulu, ko dan wannan abin alkhairin da ya same su. Se ga shi yana faɗin ze yanke alaƙarsu.
"Haba Yaya don Allah? An gama maganar komai fa. An kashe komai wallahi. Yanzu babu abin da ze kai ni wajen Lulu da danginta se alkhairi. Don Allah kar ka ce haka."
"Na gama maganata.. Ruwanki ki je gidan Afaaf, ruwanki ki koma gida.. Zaɓi ya rage gare ki.." Daga haka Abba ya miƙe ba tare da ya jira tace komai ba ya fice daga ɗakin.
"Ke ma Mami ƙi haƙura amma kin ƙi.. Idan kuma kin zaɓi Lulu ne a kan Abba shi kenan."
"Dallah can tashi mu tafi.. Er banza me baƙin hali. Maimakon ki ƙarfafa min gwuiwa, a'ah ke kullum ba ki san wannan ba." Mami ta faɗa tana jan hannun Jadwa suka fice daga ɗakin kamar za su tashi sama. Haka ta din ga sirbiɗiɗin masifa ita kaɗai kai ka ce za ta ari baki ne..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO72*
___ A ɗaya ɓangaren kuwa babu daɗewa Ammi ta isa gidan Alhaji Matawallen. A palourn Mommah ta sauka, inda nan Ummeey ta dawo bayan gama gaisawa da matan abokan Daddy. Didi, Lulu, Little har ma da Baba Atine duka suna zaune cikin ɗakin. Baba Atine da Ummeey suna ɗan hira jefi jefi. Ammi ta yi sallama cikin ɗakin. Kamar a mafarki suka ji sallamar Ammin, gaba ɗaya suka ɗaga kai suka kalleta, dan tabbatar da ita ɗin ce ba kunnensu ke jiyo musu ba daidai ba. Gaba ɗaya manta a inda suke suka yi, suka tafi da gudu suka rungumeta lokaci ɗaya suna furta
"Ammi.." Ita ma rungumesun ta yi cike da kewarsu. Ummeey da ke zaune ta yi murmushi tana kallansu. Da ƙyar suka iya sakin Ammin kafin suka tako zuwa cikin ɗakin. Se dai duk da haka sun kaasa sakin hannun Ammin. Shi kam Little da ma tuni ya riƙo mayafin Ammin saboda ma kar ta tafi ta bar shi. Neman waje suka yi suka zauna. Ammi suka gaisa da Ummeey sosai kasancewar sun shaida juna. Tuni har Little ya fara yi wa Ammi hira, en biyunta na zagaye da ita kamar za su haɗiyeta. Daidai lokacin Mommah ta shigo cikin ɗakin, ta yi matuƙar kyau cikin wani tsadadden lace, ta yi ɗaurin da ya dace da shigarta, wanda ya zauna ya mata kyau sosai. Shi kansa mayafin da ta ɗora a kan kayan ya yi mugun kyau, ya kuma hau da lace ɗin. A taƙaice dai duk abin da Mommahn ta saka sun mata kyau, sun kuma karɓi jikinta sosai. Kai idan ka ganta ba za ka ce ta ajje 'ya'ya kamarsu Gwani ba. Ƙarasawa ta yi ta nemi waje ta zauna a kan kujera, tana kallan Ammi da murmushi kan fuskarta tace
"Barka da ƙarasowa."
"Yawwah.. barka dai.. Ya jama'a?"
"Alhamdulillah.."
"Madallah.." Sake yi mata jajen abin da ya faru Ammi ta yi. Mommah ta sake mata godiya tana kuma amsa addu'ar da Anmin ta yi a kan 'ya'yan nata.
Sosai Ammi ta yi mamaki lokacin da ta ji cewar Gwani Affan shi ne ɗan Mommahn. Wato dai kenan mazajen da Lulu da Didi suka aura en biyu ne. Se ga shi Allah Ya haɗa su sun auri juna ba tare da sanin da akwai babbar alaƙa a tsakaninsu ba. Haka ta cigaba da jajanta al'amarin kafin daga bisani ta cigaba da biyewa en biyunta da ke ta kawo mata hira. Se ta biye musu musamman da Mommah da Ummeey suka fita daga ɗakin, se ya kasance saura su kaɗai. Dan haka sosai suka yi hirar da suka daɗe ba su yita ba. A nan ne kuma cikin hikima ta din ga fahimtar wasu abubuwan. Sosai ta ji daɗi yanda duk cikinsu babu wanda ya yi ƙorafi a kan auransa, hakan ba ƙaramin faranta mata rai ya yi ba musamman idan aka yi duba da farkon auren. Kamar ko yaushe haka cikin dabara ta cigaba da yi musu faɗa, da ba su shawarwari, gami da sake ji daga bakinsu ko suna da wata matsalar. Haka dai yammacin ya kasance musu cikin farin ciki. Se bayan magribh sannan Ammi ta fara shirin tafiya saboda Abba da ya zo ɗaukarta, da kuma ta ya su Daddy farin cikin abin da ya faru.
"Ammi tare za mu tafi koh?" Little ya faɗa yana kallanta.
"Aou har ka gaji da nan ɗin?" Ta tambaya tana murmushi, duk da da ma ita ma da niyyar tafiya da autanta ta zo. Se ya matso kusa da ita ya rungume hannunta yana cuno baki yace
"Ni dai ke zan bi."
"Iyee.. Lallai ma Little.. Za ka ƙara nemana ne." Didi ta faɗa tana karkaɗa kai.
"Bare kuma ni." Lulu ta faɗa tana harararsa. Shi dai be ce komai ba se sake rungume Ammin da ya yi. Ta yi murmushi dan ta san kwana biyun da ya yi ba ya ganinta ne ya sanya shi kewarta, har ya ƙi zama duk da ga en uwansa cikin gidan.
"Ni ma da ma da kai zan tafi Autana.." Ammi ta faɗa tana sake rungumo shi.
"Kai Ammi.." Suka haɗa baki wajen faɗin hakan. Har compound suka raka Ammi cike da kewa. Ba su san da zuwan Abba ba se da suka raka Ammi har inda motarsa take.
"Laaa Abba.." Suka kusan faɗa a tare cike da tsananin farin ciki.
"Na'am Afaaf.. Afrah.." Abba ya faɗa yana murmushi shi ma cike da farin cikin ganin 'ya'yan nasa. Gaisawa suka yi sosai. Abba dan farin ciki ji ya yi kamar ya yi me. Ya san halin Didi, da ma ba shi da matsala da ita. Se dai a yanda ya ga Lulun babu damuwa ko kaɗan a tare da ita ya sa ya fahimci sun yi nasara. Da alama kuma ta karɓi auren, ta haƙura. Sosai hakan ya faranta masa rai. Ya yi musu faɗa sosai da kuma nasiha sannan suka yi sallama suka tafi ya yin da su kuma suka koma cikin gidan. Duk se suka ji zaman gidan babu daɗi, yau ɗin se ta zama ta tuna musu da rayuwarsu ta gida. Ba su wani zauna hira ba tun kafin dare ya yi sosai duk suka kwanta bacci.
... "Wai me ke damunki ne Lulu? Ba za ki faɗa min ba kin gwammace ki zauna da yunwa?" Girgiza kai Lulu ta yi kafin tace tana yamutsa fuska
"Zuciyata tashi take Didi.. Ba na son ƙamshin wallahi." Ta ƙarasa maganar tana sake yamutse fuska. Sauke numfashi Didi ta yi kafin tace
"Toh ki gwada ci ko yaya ne Uhmm?" Ta yi maganar cikin rarrashi tana matsar da plate ɗin kusa da Lulu. Da sauri ta saka hannu ta janye plate ɗin ta maida shi inda Didi ta ɗakko tace duk ranta babu daɗi
"Wallahi ba zan iya ci ba Didi."
"Yau na ga ikon Allah ni er nan.. Toh me ye za ki ci?"
"Ba komai.." Ta faɗa tana turo baki. Daidai lokacin Mommah ta shigo cikin ɗakin. Ta dubi abincin da ke gabansu tace
"Wai har yanzu ba ku ci ba?" Ta tambaya da mamaki tana kallansu su duka.
"Mommah cewa ta yi wai ba za ta ci ba." In ji Didi. Se ta maida dubanta kan Lulu tace
"Me ya faru? Me ya sa ba za ki ci ba?" Gyara zamanta Lulu ta yi kamar me shirin yin doguwar magana, tace a hankali
"Ba zan iya ci ba Mommah.." Neman waje Mommah ta yi ta zauna a kusa da ita. Ta dafata sannan tace
"Me ya sa Uhmm?" Ɗaga kai ta yi ta kalleta kafin ta maida ƙasa tace
"Ba komai.. Ƙamshin ne ba na so." Kallanta Mommah ta cigaba da yi kamin can tace
"Toh shi kenan.. A dafa miki wani abun?" Girgiza kai Lulu ta yi. Mommah ta sake faɗin