Sashe 96
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kasa juyawa ta yi dan har lokacin ba ta ji ta koma daidai ba. Ganin ta ƙi juyowa ne ya sanya shi zagayawa ya tsaya a gabanta. Ya zuba mata idanunsa kamar wanda ze karanci abin da ke damunta. Sam ta kasa ɗaga ido ballantana ta kalle shi.
"Me ya faru Uhmm?" Ya tambaya cikin kulawa kuma a hankali kamar me raɗa. Hannunta ta kama ta shiga murzawa kaɗan, kamar za tace wani abu, se kuma ta girgiza kai kawai. Ta ɗaga ƙafa tana shirin tafiya ya riƙo hannun nata da sauri yana faɗin
"Ki faɗa min don Allah.." Yanzu kam ɗaga idanunta ta yi ta kalle shi. Se kuma ta janye da sauri. Har ga Allah wata irin kunyarsa take ji. Haka nan kawai take ji idan ta ɗore da sauyawar da ta yi a yanzu haka ze kawo ko dan ta fahimci waye shi ne. Duk da tun kafin sanin waye shi ɗin ta soma chanjawa amma yanzu ita dai haka take ji, ze yi tunanin dalilin chanjawarta kenan. Se da ta ja numfashi kafin ta buɗe baki cikin ƙarfin hali tace
"Don Allah Didi na jirana.." Ta yi maganar muryarta na rawa. Shi dai sam ya kaasa samun nutsuwar zuciya tun da ya ganta a irin wannan halin. Da alama kuma ba sanar da shi abin da ke damunta za ta yi ba. "Me ya sa har yanzun?" Ya tambayi kansa. Se ya sauke ajiyar zuciya yana sakin hannun nata. Ta yi amfani da wannan damar wajen saurin shigewa cikin ɗakin. Binta ya yi da kallo har ta shige ɗakin, kafin ya ɗauke kansa yana ficewa daga sashen.
.. Se da dare sannan Mommah ta samu suka zauna da en biyunta. Bayan ta fito daga ɗakin da baƙin da suka kwana suke ta tabbatar ba sa buƙatar komai, sannan ta dawo sashenta. A palour suka zauna, kamar kowanne lokaci yanzu ma se da ta soma tambayarsu lafiyarsu da kuma tambayar ko akwai wani abun, duka suka amsa mata da babu. Se suka ɗan cigaba da tattaunawa. Mommah so take ta yi shawara da Gwani a kan maganarsu Ummeey, se dai tafi so su yi maganar ne tare da Daddy. Shi kuma yanzu haka hutawa yake yi saboda yau ɗin da ya wuni gaba ɗaya be runtsa ko kaɗan ba.
"Ya asibitin kuwa? Me ke damunta?" Mom ta tambaya tana kallan Gwani. Hannu ya kai ya ɗan shafi gefen ƙeyarsa. Ya ɗan yi murmushi duk da gefe guda kuma hankalinsa na cikin ɗakin dan ganin ta inda za ta ɓullo. Cike kuma da fatan kar ya ganta kamar yanda ya ganta ɗazun.
"Mommah.." Ya faɗa yana dakatawa.
"Na'am." Ta amsa yana karantarsa. Kawai se ya yi ta maza ya maaze yace
"Wai tana ɗauke.. da.. juna biyu ne.."
"Kaiii!! Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!!" Shi ne abin da Mommah ta soma faɗa lokacin da ya kai ƙarshen maganarsa.
"Allah Ubangiji Ya ɗayyiba, Ya kuma inganta.. Kai Alhamdulillah.. Allah Ka ƙarawa Annabi daraja." Mommah ta sake faɗa, farin cikin da take ciki sam ya kaasa ɓoyuwa a kan fuskarta. Yanda ya ga zallar farin ciki a fuskar Mommahn shi ne ya sanya shi sake jin daɗi. Ya kuma sake godewa Allah. Ita kam Mommah ba ta san wacce irin godiya za ta yi wa Allah ba. Ga danginta sun dawo cikin rayuwarta, ga kuma jika tana shirin samu nan kusa. Lallai Allah shi ne abun godiya.
"Congratulations bro.. Ashe na kusa zama uba." Bad Man ya faɗa kyakkyawan murmushi kwance kan kyakkyawar fuskarsa. Jinjina kai Gwani ya yi har lokacin fuskarsa ɗauke da ƙawataccen murmushi.
A ɗaya ɓangaren kuwa tashi Didi ta yi daga kan daddumar ta ninketa, sannan ta ajjeta a ma'ajiyarta kafin ta kalli inda Lulu ke zaune ta yi shiru, ta ƙurawa waje ɗaya ido kamar me tunani.
"Amma dai ba zazzaɓin ba ne koh?" Didi ta faɗa lokacin da ta zauna kusa da Lulu. Se a lokacin Lulu ta ɗaga kai ta kalli Didi, ba tace komai ba se turo baki da ta yi ta shiga ɓata rai kamar wadda aka ɓatawa rai.
"Kaii!! Toh me kuma ya faru?" Didi ta sake faɗa tana kallan nata. Ita Allah ma ya gani ba ta san ta ina za ta fara ba. Da wane idon za ta cigaba da kallan Didi idan tace mata ciki ne da ita? Taɓ ɗi jam. Daidai lokacin Mommah ta shigo cikin ɗakin. Ta ƙarasa ta nemi waje ta zauna tana kallansu su duka. Se da suka sake gaisawa da Mommahn sannan tace
"Afaaf.."
"Na'am.." Lulu ta amsa tana kallan Mommah. Murmushi Mommah ta yi kana ta soma faɗin
"Allah Ya yi miki albarka Afaaf, Ya inganta abin da ke cikinki, Ya kawo shi lafiya.. Ya kike jin jikinki yanzu? Babu abin da ke damunki dai koh?" Shiru ta yi bayan ta ɗauke kanta da sauri. Ba ta taɓa tunanin Mommahn ta sani ba, dan ba ta ɗauka Gwanin ze iya faɗa mata ba. Yanzu shi saboda rashin kunya da rashin ta ido Mommahn ya faɗawa wannan maganar Wannan abun kunya da me ya yi kama.
"Uhmmm?" Mommah ta sake tambaya. Se ta yi saurin jinjina kai har lokacin ba ta ɗaga kai ta kalli Mommahn ba, se hannunta da take murzawa a hankali.
"Toh ki kula sosai.. Idan ki na buƙatar wani abu ki sanar da ni. Afrah ki kula da er uwakki.. Allah Ya yi muku albarka." Ta ƙare yanzun tana kallan Didi. Se a lokacin Didi ta ɗauke kanta daga kallan Lulu da take tun ɗazu, ta yi murmushin yaƙe tana faɗin
"Toh.."
"Akwai abin da zan yi yanzu.. Bari na je."
"Toh Mommah.." Shi ne abin da Didi ta faɗa, da ma ta ƙagu Mommahn ta fita daga ɗakin. Aikuwa kamar ta sani ɗin se ta fice daga ɗakin. Maida fuskarta yanda take Didi ta yi ta ƙurawa Lulu ido. Duk da yanda gefe guda wani farin ciki ke neman danne ɓacin ranta, ta yi fatali da hakan, ta ƙi bari ya yi tasiri a kanta.
"Ciki ne dake Lulu shi ne ba ki faɗa min ba?" Didi ta faɗa har cikin muryarta ɓacin rai na bayyana. Da sauri Lulu ta ɗaga kai ta kalleta jin muryarta da ke ɗauke da fushi. Se ta yi saurin girgiza kai tace
"Ba haka ba ne Didi.. Ba ƙin faɗa miki na yi ba."
"Ya ishe ni.. Ni babu abin da za ki faɗa min." Didi ta faɗa bayan ta ɗaga mata hannu. Ta miƙe, dan idan ba ta yi wasa ba farin cikin na dab da danne ɓacin ran gaba ɗaya. Riƙo hannunta Lulu ta yi tace
"Don Allah ki yi haƙuri Didina.. Wallahi ba haka ba ne.. Kin ga ni fa Allah.." Se kuma ta yi shiru. Harara Didin ta jefa mata kafin tace
"Allah me..?"
"Toh ni kunya nake ji, na rasa ta ina zan fara faɗa miki.. Haka kurum.." Ta ƙare tana turo baki. Yanzu kam haƙura ta yi ta sheƙe da dariya sosai har da toshe baki. Daidai lokacin da aka turo ƙofar ɗakin. Duka suka ɗaga kai suka kalli wadda ta turo ƙofar ɗakin. Sanye take cikin wata haɗaɗɗiyar doguwar riga, ta yafa yalolon mayafinta da ta yi amfani da shi wajen rufe gashin kanta. Hannunta ɗauke da tsadaddiyar wayarta da take dannawa. Idanunta ta kai cikin ɗakin daidai lokacin da suma suka kalleta.
"Oh.. yi haƙuri fa.." Ta faɗa a ɗan yatsine tana sakin ƙofar bayan ta watsar da su. Ba ta jira sun ce komai ba ta yi gaba tana taɓe baki. Kallan juna Lulu da Didi suka yi. Haka nan kawai se su ka ga abun wani iri. Kamar irin da gangan ta yi hakan.
"Wace wannan ɗin? Me ye hakan ta yi? Ni fa ba ba na son rashin mutunci." Lulu ta faɗa fuskarta a haɗe. Sanin hali ya sanya Didi faɗin
"Ke babu fa komai. Ƙila akwai wadda take nema ne, ta yi kuskuren zuwa ɗakin nan.." Didi ta ƙare tana murmushi duk da ita ma ta fahimci wani abun..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO75*
... Kusan a tare Mommah da su Lulu suka fito daga ɗaki. Dukkansu shirye cikin shiga me kyau, wadda ta yi matuƙar dacewa da su. Kaya iri ɗaya Lulu da Didi suka saka, sun sake fitowa a en biyunsu sakk. Se dai Lulu sosai take sake murjewa, ta ƙara wani shahararren kyau. A palour suka tarar da Iftihal da ke zaune kan kujera, t.v na ta aikinta ya yin da idanunta ke kan wayarta tana dannawa. Murmushi ta yi lokacin da ta ɗaga kanta ta kalli Mommah tace
"Barka da wannan lokaci.."
"Barka dai.. Ki na lafiya?" Mommah ta faɗa tana murmushi.
"Alhamdulillah." Ta amsa tana maida dubanta kan waya. Kamar yanda ba ta kallesu ba haka su ma babu wanda ya kalleta. Takaici ya kamata, su ba su san ita ɗin tana da bambanci da su ba ne? Ba su san ita ɗin wace ce ba? A hankali ta ɗaga kai ta watsa musu wani banzan kallo, daidai lokacin da Lulu ta ɗaga kai. Se kuwa kallan ya sauka a kan fuskarta, da ta jefa mata wani kallo da ya fi nata muni da manyan idanunta masu kyau kafin ta watsar da ita. Haushi takaici suka sake rufe Iftihal. Lallai dole ne ta koyawa yarinyar nan hankali.
"Ifti ko za ki bi mu ne..?" Mommah ta faɗa tana murmushi. Se da ta sake watsawa Lulu harara sannan ta girgiza kai kafin tace
"A'ah.. zan zauna a nan.. Se kun dawo." Ta ƙarasa maganar tana soma danna wayarta.
"Babu damuwa?" Mommah ta sake faɗa cikin kulawa.
"Eh babu.." Se a lokacin sannan Mommah ta kalli su Didi tace
"Me ya faru Uhmm?" Ya tambaya cikin kulawa kuma a hankali kamar me raɗa. Hannunta ta kama ta shiga murzawa kaɗan, kamar za tace wani abu, se kuma ta girgiza kai kawai. Ta ɗaga ƙafa tana shirin tafiya ya riƙo hannun nata da sauri yana faɗin
"Ki faɗa min don Allah.." Yanzu kam ɗaga idanunta ta yi ta kalle shi. Se kuma ta janye da sauri. Har ga Allah wata irin kunyarsa take ji. Haka nan kawai take ji idan ta ɗore da sauyawar da ta yi a yanzu haka ze kawo ko dan ta fahimci waye shi ne. Duk da tun kafin sanin waye shi ɗin ta soma chanjawa amma yanzu ita dai haka take ji, ze yi tunanin dalilin chanjawarta kenan. Se da ta ja numfashi kafin ta buɗe baki cikin ƙarfin hali tace
"Don Allah Didi na jirana.." Ta yi maganar muryarta na rawa. Shi dai sam ya kaasa samun nutsuwar zuciya tun da ya ganta a irin wannan halin. Da alama kuma ba sanar da shi abin da ke damunta za ta yi ba. "Me ya sa har yanzun?" Ya tambayi kansa. Se ya sauke ajiyar zuciya yana sakin hannun nata. Ta yi amfani da wannan damar wajen saurin shigewa cikin ɗakin. Binta ya yi da kallo har ta shige ɗakin, kafin ya ɗauke kansa yana ficewa daga sashen.
.. Se da dare sannan Mommah ta samu suka zauna da en biyunta. Bayan ta fito daga ɗakin da baƙin da suka kwana suke ta tabbatar ba sa buƙatar komai, sannan ta dawo sashenta. A palour suka zauna, kamar kowanne lokaci yanzu ma se da ta soma tambayarsu lafiyarsu da kuma tambayar ko akwai wani abun, duka suka amsa mata da babu. Se suka ɗan cigaba da tattaunawa. Mommah so take ta yi shawara da Gwani a kan maganarsu Ummeey, se dai tafi so su yi maganar ne tare da Daddy. Shi kuma yanzu haka hutawa yake yi saboda yau ɗin da ya wuni gaba ɗaya be runtsa ko kaɗan ba.
"Ya asibitin kuwa? Me ke damunta?" Mom ta tambaya tana kallan Gwani. Hannu ya kai ya ɗan shafi gefen ƙeyarsa. Ya ɗan yi murmushi duk da gefe guda kuma hankalinsa na cikin ɗakin dan ganin ta inda za ta ɓullo. Cike kuma da fatan kar ya ganta kamar yanda ya ganta ɗazun.
"Mommah.." Ya faɗa yana dakatawa.
"Na'am." Ta amsa yana karantarsa. Kawai se ya yi ta maza ya maaze yace
"Wai tana ɗauke.. da.. juna biyu ne.."
"Kaiii!! Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!!" Shi ne abin da Mommah ta soma faɗa lokacin da ya kai ƙarshen maganarsa.
"Allah Ubangiji Ya ɗayyiba, Ya kuma inganta.. Kai Alhamdulillah.. Allah Ka ƙarawa Annabi daraja." Mommah ta sake faɗa, farin cikin da take ciki sam ya kaasa ɓoyuwa a kan fuskarta. Yanda ya ga zallar farin ciki a fuskar Mommahn shi ne ya sanya shi sake jin daɗi. Ya kuma sake godewa Allah. Ita kam Mommah ba ta san wacce irin godiya za ta yi wa Allah ba. Ga danginta sun dawo cikin rayuwarta, ga kuma jika tana shirin samu nan kusa. Lallai Allah shi ne abun godiya.
"Congratulations bro.. Ashe na kusa zama uba." Bad Man ya faɗa kyakkyawan murmushi kwance kan kyakkyawar fuskarsa. Jinjina kai Gwani ya yi har lokacin fuskarsa ɗauke da ƙawataccen murmushi.
A ɗaya ɓangaren kuwa tashi Didi ta yi daga kan daddumar ta ninketa, sannan ta ajjeta a ma'ajiyarta kafin ta kalli inda Lulu ke zaune ta yi shiru, ta ƙurawa waje ɗaya ido kamar me tunani.
"Amma dai ba zazzaɓin ba ne koh?" Didi ta faɗa lokacin da ta zauna kusa da Lulu. Se a lokacin Lulu ta ɗaga kai ta kalli Didi, ba tace komai ba se turo baki da ta yi ta shiga ɓata rai kamar wadda aka ɓatawa rai.
"Kaii!! Toh me kuma ya faru?" Didi ta sake faɗa tana kallan nata. Ita Allah ma ya gani ba ta san ta ina za ta fara ba. Da wane idon za ta cigaba da kallan Didi idan tace mata ciki ne da ita? Taɓ ɗi jam. Daidai lokacin Mommah ta shigo cikin ɗakin. Ta ƙarasa ta nemi waje ta zauna tana kallansu su duka. Se da suka sake gaisawa da Mommahn sannan tace
"Afaaf.."
"Na'am.." Lulu ta amsa tana kallan Mommah. Murmushi Mommah ta yi kana ta soma faɗin
"Allah Ya yi miki albarka Afaaf, Ya inganta abin da ke cikinki, Ya kawo shi lafiya.. Ya kike jin jikinki yanzu? Babu abin da ke damunki dai koh?" Shiru ta yi bayan ta ɗauke kanta da sauri. Ba ta taɓa tunanin Mommahn ta sani ba, dan ba ta ɗauka Gwanin ze iya faɗa mata ba. Yanzu shi saboda rashin kunya da rashin ta ido Mommahn ya faɗawa wannan maganar Wannan abun kunya da me ya yi kama.
"Uhmmm?" Mommah ta sake tambaya. Se ta yi saurin jinjina kai har lokacin ba ta ɗaga kai ta kalli Mommahn ba, se hannunta da take murzawa a hankali.
"Toh ki kula sosai.. Idan ki na buƙatar wani abu ki sanar da ni. Afrah ki kula da er uwakki.. Allah Ya yi muku albarka." Ta ƙare yanzun tana kallan Didi. Se a lokacin Didi ta ɗauke kanta daga kallan Lulu da take tun ɗazu, ta yi murmushin yaƙe tana faɗin
"Toh.."
"Akwai abin da zan yi yanzu.. Bari na je."
"Toh Mommah.." Shi ne abin da Didi ta faɗa, da ma ta ƙagu Mommahn ta fita daga ɗakin. Aikuwa kamar ta sani ɗin se ta fice daga ɗakin. Maida fuskarta yanda take Didi ta yi ta ƙurawa Lulu ido. Duk da yanda gefe guda wani farin ciki ke neman danne ɓacin ranta, ta yi fatali da hakan, ta ƙi bari ya yi tasiri a kanta.
"Ciki ne dake Lulu shi ne ba ki faɗa min ba?" Didi ta faɗa har cikin muryarta ɓacin rai na bayyana. Da sauri Lulu ta ɗaga kai ta kalleta jin muryarta da ke ɗauke da fushi. Se ta yi saurin girgiza kai tace
"Ba haka ba ne Didi.. Ba ƙin faɗa miki na yi ba."
"Ya ishe ni.. Ni babu abin da za ki faɗa min." Didi ta faɗa bayan ta ɗaga mata hannu. Ta miƙe, dan idan ba ta yi wasa ba farin cikin na dab da danne ɓacin ran gaba ɗaya. Riƙo hannunta Lulu ta yi tace
"Don Allah ki yi haƙuri Didina.. Wallahi ba haka ba ne.. Kin ga ni fa Allah.." Se kuma ta yi shiru. Harara Didin ta jefa mata kafin tace
"Allah me..?"
"Toh ni kunya nake ji, na rasa ta ina zan fara faɗa miki.. Haka kurum.." Ta ƙare tana turo baki. Yanzu kam haƙura ta yi ta sheƙe da dariya sosai har da toshe baki. Daidai lokacin da aka turo ƙofar ɗakin. Duka suka ɗaga kai suka kalli wadda ta turo ƙofar ɗakin. Sanye take cikin wata haɗaɗɗiyar doguwar riga, ta yafa yalolon mayafinta da ta yi amfani da shi wajen rufe gashin kanta. Hannunta ɗauke da tsadaddiyar wayarta da take dannawa. Idanunta ta kai cikin ɗakin daidai lokacin da suma suka kalleta.
"Oh.. yi haƙuri fa.." Ta faɗa a ɗan yatsine tana sakin ƙofar bayan ta watsar da su. Ba ta jira sun ce komai ba ta yi gaba tana taɓe baki. Kallan juna Lulu da Didi suka yi. Haka nan kawai se su ka ga abun wani iri. Kamar irin da gangan ta yi hakan.
"Wace wannan ɗin? Me ye hakan ta yi? Ni fa ba ba na son rashin mutunci." Lulu ta faɗa fuskarta a haɗe. Sanin hali ya sanya Didi faɗin
"Ke babu fa komai. Ƙila akwai wadda take nema ne, ta yi kuskuren zuwa ɗakin nan.." Didi ta ƙare tana murmushi duk da ita ma ta fahimci wani abun..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO75*
... Kusan a tare Mommah da su Lulu suka fito daga ɗaki. Dukkansu shirye cikin shiga me kyau, wadda ta yi matuƙar dacewa da su. Kaya iri ɗaya Lulu da Didi suka saka, sun sake fitowa a en biyunsu sakk. Se dai Lulu sosai take sake murjewa, ta ƙara wani shahararren kyau. A palour suka tarar da Iftihal da ke zaune kan kujera, t.v na ta aikinta ya yin da idanunta ke kan wayarta tana dannawa. Murmushi ta yi lokacin da ta ɗaga kanta ta kalli Mommah tace
"Barka da wannan lokaci.."
"Barka dai.. Ki na lafiya?" Mommah ta faɗa tana murmushi.
"Alhamdulillah." Ta amsa tana maida dubanta kan waya. Kamar yanda ba ta kallesu ba haka su ma babu wanda ya kalleta. Takaici ya kamata, su ba su san ita ɗin tana da bambanci da su ba ne? Ba su san ita ɗin wace ce ba? A hankali ta ɗaga kai ta watsa musu wani banzan kallo, daidai lokacin da Lulu ta ɗaga kai. Se kuwa kallan ya sauka a kan fuskarta, da ta jefa mata wani kallo da ya fi nata muni da manyan idanunta masu kyau kafin ta watsar da ita. Haushi takaici suka sake rufe Iftihal. Lallai dole ne ta koyawa yarinyar nan hankali.
"Ifti ko za ki bi mu ne..?" Mommah ta faɗa tana murmushi. Se da ta sake watsawa Lulu harara sannan ta girgiza kai kafin tace
"A'ah.. zan zauna a nan.. Se kun dawo." Ta ƙarasa maganar tana soma danna wayarta.
"Babu damuwa?" Mommah ta sake faɗa cikin kulawa.
"Eh babu.." Se a lokacin sannan Mommah ta kalli su Didi tace