← Book details A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 49 OF 122

Sashe 49

A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Kee!!" Ya yi maganar lokacin da ya aza mata shu'umar ƙwayar idanunsa. Yanayin yanda ya riƙetan ne ya sanya ita ma kallan fuskarsa take yi. Hakan ne ya sa cikin ƙanƙanin lokaci idanunsu suka shige cikin na juna. Kusan a lokaci ɗaya kowannensu ya ji wani bugun zuciya. Be taɓa tsayawa ya kalli yanda idanunta suke ba se a yau. Dan kuwa se ya ji tamkar kar ya janye idanun nasa saboda yanda idanun nata suka ƙawata shi. Wannan brown ɗin ƙwayar idanun nata su yake kalla. Idanuntan da suka fi kama da na mage. Be taɓa ganin irin idon ba, be sani ba kuma ko akwai masu irinsa. Shi dai amma be taɓa gani ba se a yanzu. Yanda ta ga ya shagala kamar me tunani ya sanyata sake ƙoƙarin tashi. Sarai yana sane da ita, hakan ne ya sanya shi sake riƙo hannunta ta sake yin kusa da shi.

"Keee!! Ki nutsu ki faɗa min me ya zaunar da ke cikin ɗakin?" Shiru ta yi tana ɗan janye hannunta ko za ta samu ya saketa.

"Taurin kai koh? Ba na miki gargaɗi ba?" Ya dakata a nan yana cigaba da kallanta kamar ba shi ba. Nan ma ba tace komai ba se kawar da kanta take yi tana cigaba da ƙiƙƙifta narkakkun idanunta da ke cike da ƙwalla. Gaba ɗaya ta rasa yanda za ta yi. So take ya saketa amma ya ƙi, so take ta bar ɗakin amma ya ƙi barinta.

"Ki ka sake ki ka min kuka za ki ga abin da zan miki." Ya faɗa yana damƙe hannunta da ɗan ƙarfi saboda yanda ya ga yanayin fitar numfashinta ya ƙara gudu alamar kuka za ta yi. Ƙaramar ƙara ta saki saboda yanda ta ji zafi. A hankali ta buɗe baki cikin rashin sanin mafita idan ba wannan ba tace

"Don Allah ka yi haƙuri.. Ba ma zan sake shigowa cikin ɗakin ba. Ka yi haƙuri don Allah.."

"Better.." ya ƙare maganar yana sakar mata hannu. Cikin matuƙar sauri ta sauka daga kan gadon a gaggauce ta fice daga ɗakin tana sauke wasu taggwan ajiyar zuciya.

... Ta kai fiye da mintuna 20 tana daga cikin ɗakin tana kallansa. Se dai ta kasa fitowa dan ko magana ma ba ta son yi masa ballantana a kai ga ta karɓi wani abun a wajensa. Minti 1 ta ƙara zuwa lokacin ta haƙura, kawai ta soma takawa dan fitowa daga cikin ɗakin saboda kar ta je ya tashi ya bar ɗakin kuma a yi biyu babu. A ɗan nesa kaɗan da shi ta tsaya, se dai inda ta tabbatar ze jita. Nan ma cigaba ta yi da tsayuwar ba tare da tace komai ba. Se cuno baki da ta soma yi kamar wadda aka tilastawa yin maganar. Duk da rubutu yake yi cikin wata farar fullscap amma sarai ya san da wanzuwarta a wajen. Se dai be nuna alamun hakan ba. Ya cigaba da rubutunsa a nutse. Se da ta wula sannan dan kanta ta buɗe baki da ƙyar tace

"Ka ara min wayarka zan kira Didi.." ta ƙare har lokacin tana tura baki tana kuma kallan gefe. A kaikaice ya ɗaga ido ya saci kallanta. Sosai ta yi kyau da yanda take yin maganar. Se ya sauke kansa yana cigaba da rubutunsa, ya nuna kamar be ji ba. Ba ƙaramin haushi ta ji ba jin shirun da ta yi. Ta ɗauka ko yana jinta ne amma ya yi mata shiru. Se da ta ɗago kanta ta kalli inda yake zaunen yana rubutunsa cikin kwanciyar hankali sannan ta fahimci be jita ba. Ta gyara tsayuwarta tana fatan yanzu idan ta yi maganar ya jita.

"Ka ba ni wayarka in kira Didi.." ta sake faɗa se dai yanzun tana kallansa.

"Wai da ni kike magana?" Gwani ya faɗa cikin basarwa bayan ya ɗaga kai shi ma ya kalleta. Shiru kawai ta yi tana ji kamar ta rusa ihu dan takaici. Musamman da ta fahimci kamar yana sane ya yi maganar nan. Kamar ba za tace komai ba, se dai kuma da yake ita take nema ya sanyata maimaita abin da ta faɗa a karo na biyu. Yamutsa fuska ya yi bayan ya ɗago da kansa daga kan rubutun da yake kafin yace

"Ohh.. ban ji ba.. me ne..?" Ya ƙare yana karkatar da kansa, shi wai a lallai da gaske so yake ya ji abin da ta faɗa ɗin. Se dai yau ɗin burinsa ta ƙara cewa wani abun ya saurara a yanda ta yi maganar tun farko, dan idan ba dan ya san halinta ba se yace shagwaɓa take yi ba tsiwa ba. Zuwa lokacin fa Lulu ta gama shaƙa da yawa. Se dai ta fahimci da gasken yana sane yake yi mata wulaƙanci dan ya ga ta zo neman abu a wajensa...

A yi manage da wannan. Za mu haɗe gobe idan Allah ya kai mu.

MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO51*

___Ba ta ƙara ko minti 1 a wajen ba ta juya dan barin wajen. A ranta tana sake mamakin yanda ya ƙi chanja hali har yanzun bayan ta san waye shi. Ita ta ɗauka waɗanda ba su san shi ba yake nunawa izza kamar yanda yake musu kafin su san shi. Se dai ta fahimci sam ba haka ba ne. Abin da ta kasa fahimta kenan har yanzun.
Fahimtar abin da za ta yi ya sanya shi yin murmushin da ya ƙawata kyakkyawar fuskarsa. Se ya samu kansa da binta da kallo kamar wanda ake ja. Se da ta ɓacewa ganinsa sannan ya dawo da dubansa kan abin da yake yi. Ɗan lumshe idanunsa ya yi yana maida kansa ya jingina da bangon da ke bayansa. Be san dalilin da ya sa a kwanakin nan yake yawan son kallanta ba. Yake kuma yawan son ya ji ta yi magana ba, ko da kuwa tsiwar nan tata za ta yi. Yanzun ma abin da ya sa ya ƙi nuna ya fahimci abin da take faɗa ne dan ta cigaba da tsayawa ko ya samu ya dinga kallanta ko da a fuzge ne. Se dai da alama ta fusata. A hankali ya ɗan buɗe idanunsa daidai lokacin da ya furzar da iska daga bakinsa ya sake bin ɗakin da ta shiga da kallo. Ɗakin da duk da kasancewar kayan kitchen a cikinsa hakan be hanata zama a cikinsa ba duk lokacin da yake nan. Se kace wanda ze yi mata wani abu. Abin da zuciyarsa ta raya masa ne ya sanya shi yin murmushi lokacin da ya tuna da abin da ya faru. Wanda shi ne kusan sanadiyyar da ya sa ta dena haɗa ɗaki ɗaya da shi. Kawai se ya girgiza kai lokacin da yake miƙewa ya fice daga ɗakin.

... A hankali ta cigaba da takawa zuwa cikin ɗakin tana bin ko ina da kallo a wani yatsine kamar wadda ta ga mutum a wajen. A haka har ta ƙarasa ɗakin Bad Man. Kai tsaye ta tura ƙofar ɗakin ta shige. Yana zaune kan gadon sanye cikin wasu ƙananan kaya masu shegen kyau. Waɗanda suka mugun amsar shi, kamar da ma dan shi a ka yi su. Sake kallan agogon dake ɗaure a kan tsintsiyar hannunsa ya yi, har lokacin ya kaasa dena mamakin tsawon awannin da ya ɗauka cikin ɗakin nan yarinyar nan na ciki. Be taɓa zaton har gari ya waye ba. Ya ɗauka dai dukka cikin dare ne. Se bayan da ta fita daga ɗakin ya duba lokaci sannan ya fahimta. A daidai lokacin Mom ta shigo cikin ɗakin. Ya ɗaga kai ya kalleta da sauri dan ya ɗauka Didi ce ta sake dawowa.

"Mom.." ya faɗa da ɗan mamaki, saboda daɗewa da ya yi be ga ƙafar Mom ɗin cikin ɗakin nan ba. Ba ta amsa ba se da ta gama ƙarewa cikin ɗakin kallo sannan ta nemi waje gefensa ta zauna.

"Good morning my dear.." ta faɗa lokacin da ta gama gyara zamanta a kan gadon.

"Morning Mom.. How you dey?" Maimakon ta amsa shi se ta jefa masa tambayar da ta sanya shi ɗaga kai ya kalleta.

"Ka fara shiri ne?" A mamakance ya kalleta ɗin dan shi har ga Allah gaba ɗaya ya manta sun yi wata magana makamancin wannan.

"Shirin me fa?" Ya tambaya yana kallanta.

"Ban gane ba Areef.. me kake nufi da ni ne? Ba mun yi maganar duk ranar da zan bar ƙasar nan za mu bari tare ba? Ko ka manta ne?" Ta ƙare a raunane dan ta soma shanshano abin da yake nufi. Sauke numfashi ya yi, se kuma ya shiga girgiza kai sannan yace

"Sorry Mom.. Na manta ɗin da gaske.. But In Sha Allah zan biyo ki bayan tafiyarki." Hannu Mom ta kai ta dafe goshinta da shi. Ita kam wannan yaro, wannan yaro na neman saka mata ciwon kai. Jin ba tace komai ba ya sanya shi ɗorawa da faɗin

"Ban shiryawa zuwa ko ina ba. So dole se na shirya kin sani Mom. Ba ze yiwu yau kawai na tafi wata ƙasar ba. Na san dole za ki ce se kin fara zuwa Abuja ki kwana biyu kafin ki wuce.. toh idan dai na gama shirye shiryen da zan yi may be mu sauka tare." Ba dan wannan maganar da ya yi ba ba za ta yarda da barin nasa ba. Amma jin abin da ya faɗa ya sanyata yin amanna. Se ta sauke ajiyar zuciya sannan tace

"Shi kenan.. Zuwa anjima zan wuce Abuja.. And kai nake so ka kai ni." Daidai lokacin da ya miƙe tsaye yace

"Babu damuwa.." Daga haka se ita ma Mom ɗin ta miƙe dan ficewa daga ɗakin da tun lokacin da Aunt Makiyy tace ta dena shiga ba ta sake shiga ba. Se yau ɗin da ta manta da ita kawai ta shige.

"Za ka fita ne?"
Chapter 49 · 0% Book details