Sashe 2
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"A'ah Son pls ka koma ka kwanta.. kana buƙatar hutu plssss.." ta faɗa cikin rarrashi har lokacin tana riƙe da hannunsa. Haka kawai tunda ya farka yake jinsa a fusace, gaba ɗaya jikinsa ya masa wani irin nauyi, komai na jikinsa jinsa yake kamar ba na shi ba. Hakan ne ya sanya a yanzu burinsa kawai ya fita yaje ya sha wani abun ko ze samu ya dawo daidai. Dan gaba ɗaya ya kasa gane me ke damunsa. Se a lokacin ma ya lura da inda yake, ya lura da ba a cikin gidansu yake ba. Hakan ne ya sa ya sake kallan Mom ɗin yace
"Ina ne nan?" Ya faɗa yana sake kallan ɗakin sosai. Kafin tace komai ya sake faɗin
"What brought me here? Asibiti?" Ya faɗa a mamakance.. Da sauri Mom ta girgiza kai tace
"I don't even know my Son.. But bari na kira Daddynka shi ya san dalilin kawoka nan ɗin.." Ta yi maganar tana ɗakko wayarta, ta shiga kiran Daddy. Se dai cikin rashin sa'a ake faɗa mata wayar ba zata shiga a lokacin ba.
... Gaba ɗaya se da Daddy ya miƙa musu hannu suka gaisa. Daga Abeey har Abba suna sake mamakin hali irin na Alhaji Matawallen.
"Barkanku da wannan lokaci.." Daddy ya faɗa..
"Barka dai.." Abeey da Abba suka haɗa baki wajen faɗar hakan. Bayan sun sake gaisawa sosai Daddy ya soma faɗin
"Toh wannan dai aure an yi shi ne ba tare da sanin kowanne ɓangare ba. Saboda haka na san iyaye mata kan iya yin taro duk ranar da yaran nan zasu tare. Saboda haka ina ganin mu saka ranar da ya kamata a ɗauki yaran nan a kaisu gidajensu. Ina ganin hakan shi ne mafita.." Jinjina kai dukansu suka yi cikin na'am da zancen Daddyn. Abeey ya ɗan yi gyaran murya sannan yace
"Toh se dai wani hanzari ba gudu ba.. Akwai abubuwa da ake irin na al'ada, wanda idan akace a cikin kwanaki kaɗan za a yi su Yallaɓai kamar ya yi kusa. Dan haka nake neman alfarmar bamu lokaci ko da kaɗan ne a fara kai kayan sannan a bamu matar.." Murmushi Abba ya yi yana kallan Abeey yace
"Ayyah.. Malam.. in dai dan wannan ne babu matsala.. Kowannensu ka iya yi wa matarsa duk abin da ya ga dama bayan zuwanta gidansa. Wannan ɗin tunda ba addini bane ina ganin kawai mu bar shi.."
"A'ah barinsu kam be taso ba. Gwara dai da kace idan sun je can ɗin se a musu.." Abeey ya katse Abba da faɗin hakan. Dukansu se suka yi murmushi daidai lokacin da Daddy yace
"Hakan ma ya yi.. Muma kuma ta ɓangaren mu bama buƙatar komai.. yarinya kawai muke buƙata.."
"A yi min wannan alfarmar Yallaɓai. Ko daga baya ne zan yi wa yarinyar nan kaya a aiko mata dasu.." Abba ya faɗa yana murmushi.
"Shi kenan.. Malam ka amince da hakan?" Daddy ya faɗa yana kallan Abeey
"Shi kenan.. Allah ya sanya alkhairi, ya haɗa kan yaran nan. Ya kuma kaɗe fitina.." Abeey ya amsa da hakan. Gyara zama Daddy ya yi kafin yace
"Toh Alhamdulillah.. Tunda dai an gama da kowacce matsala. Ina ganin kawai nan da sati ɗaya idan Allah ya kai mu kowaccensu ta tare a ɗakinta. Allah ya bada zaman lafiya.."
Toh Alhamdulillah. Bayan hutun en kwanaki da na ɗauka, yau ga ni na dawo. In Sha Allah zamu cigaba da fafatawa babu kama hannun yaro. 😍💃
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO24*
___"Toh madallah, Allah ya kaimu ya kuma sa ayi komai a sa'a, ya kaɗe fitina." Abeey ya faɗa. Abba da Daddy suka amsa da "Ameen."
... "Barka da wannan lokaci Abeey.." Gwani ya faɗa yana neman waje ya zauna. Murmushi Abeey ya yi kana ya amsa da
"Barka dai Affan.. Zauna sosai magana zamu yi.." Abeey ya yi maganar lokaci ɗaya yana kallansa. Gyara zaman ya yi shima yana murmushin. Abeey ya ɗan sauke ajiyar zuciya sannan yace
"Wato Affan kamar yanda na sanar da kai, zan ɗaura maka aure.. toh na cika. Na ɗaura maka aure kuma In Sha Allah ina fatan zaka karɓi matar hannu bibbiyu.." Shiru Gwani ya yi yana ɗan so ya tunano abin da ya sa Abeeyn ya ɗaura auren nasa haka kamar a gaggauce. Se dai kome ya yi hakan ba laifi bane. Dan haka ya yi shiru yana cigaba da saurarar abin da yake faɗa ɗin.
"Babban abin da ya min daɗi shi ne yadda mahaifin yarinyar da kansa ya nemi yana so ka auri ɗiyarsa. Kuma abin da ya sake min daɗi shi ne yanda yarinyar tasa ta kasance ɗalibarka." Tunda Abeeyn ya fara magana be ɗago ba se yanzun. Be san sanda ya furta
"Ɗalibata..?" Cike da tabbatarwa Abeey ya jinjina kai
"Ƙwarai kuwa ɗalibarka.. Er gidan Muhammadu Aji ce fa.." Ɗan shiru Gwani ya yi, se ya ji kamar yau ne ya fara jin sunan. Zuwa can kuma se ya tuna wane ne Muhammad Aji, su waye kuma 'ya'yansa. Kenan Afrah Abban nasu ya nemi ya aura? Har ma an ɗaura auren?
"Kaa ji sunan nata.. ɗan tuna min ya ɗan kwanta min.."
"Afrah...?" Ya faɗa cikin sigar tambaya da sauri yana kallan Abeey. Girgiza kai Abeey ya yi yace
"A'ah.. ina tunanin sunan er uwar tagwaitakarta ne wannan.." Cikin son sake tabbatar da abin da Abeeyn ke nufi. Da kuma son ya ƙaryata abin da yake hasashe yace
"Afaaf..?" Murmushi Abeey ya yi yace
"Ƙwarai kuwa Afaaf.." Runtse idanunsa Gwani ya yi yana jin yanda kansa ya ɗan juya masa. Be san ta yadda Abeey ze yi wani abu yace be masa ba. Amma wannan karon abin ya shammace shi. Afaaf fa? Ta yaya wannan yarinyar dake ganin tafi ƙarfin kowa zata zauna a matsayin matarsa? Bama wannan ba, ta yaya shi kansa ze iya zama da ita a matsayin matarsa? Wane alfahari ze yi idan an kira wannan da matarsa? Mutuniyar da bata ragawa kowa ba? Kallan kowa take a ƙasanta. Kallan kowa take a tafi ƙarfinsa. Yarinyar da tun zuwansa ajin basu taɓa shiri ba daidai da rana ɗaya kuwa? Yau ita ake kira da matarsa?
"Ya Salam.." ya faɗa cikin zuciyarsa yana dafe kansa, zuciyarsa na masa wani irin zafi.
"Affan.." Abeey ya faɗa yana kallansa. Da sauri ya ɗaga kai, yana ɗan wanzar da murmushi a kan fuskarsa yace
"Na'am Abeey.."
"Lafiya dai koh?"
"Ehh.. kaina ke ɗan sara min.." ya faɗa a nutse.
"Dama ba tun yanzu bane?" Abeey ya tambaya cike da kulawa.
"Yanzu ne. Amma babu damuwa Abeey, na ji wadda ka aura min.. Allah ya saka da alkhairi.."
"Ameen Ameen.. Ka daure ka sha magani, sannan ka kama kan naka. Allah ya ba da lafiya.. ya kuma saka albarka a rayuwar aurenku.. zuwa gobe se mu ƙarasa maganar kafin nan kan ya yi sauƙi."
"Ameen.." Gwani ya amsa da hakan yana ficewa daga ɗakin. Gaba ɗaya kansa ya kulle, ya ma rasa tunanin da ze yi. Ji yake kamar wani shirin film ne yake kalla, ko kuma wani abu da yafi kama da almara. Jin kansa na cigaba da sarawa lokaci ɗaya ransa na cigaba da ɓaci idan ya tuna wace ce Afaaf se ya nemi waje kawai ya kwanta, cike da fatan ya manta da komai a yanzun, ko ze samu bacci ya ɗauke shi. Ko kuma ma dai kawai ya ga ya farka daga wani baccin ya ga ashe duk mafarki yake yi. Idan kuwa gaske ne lallai ikon Allah ya wuce gaban wasa. Ko me kuma ya tsara ze faru, toh fa babu makawa se ya faru ɗin. A nutse ya ɗan lumshe kyawawan idanunsa har lokacin hannunsa na riƙe da kansa.
... Cikin matuƙar farin ciki yake driving, murmushi yaƙi barin fuskarsa. Tunda Abba ya kira shi a kan yana son ganinsa ya kasa sukuni, gaba ɗaya hankalinsa ya tafi can wajen Abban. Burinsa kawai ya isa ya ji dalilin kiran Abban. Duk da dai ya san kiran na da nasaba ne da maganar aurensa da Didi. Har ya isa gidan ya kasa dena zumuɗi. Aka yi masa jagora zuwa ɗakin baƙi, ya nemi waje ya zauna yana jiran zuwan Abban. Babu daɗewa kuwa se ga Abba ya shigo ɗakin da sallama. Yana ganinsa ya miƙe cike da girmamawa, se da Abban ya zauna sannan shima ya zauna bayan ya gaishe da shi cikin girmamawa.
"Amm Kaseem na san zaka yi mamakin kiran nan da na maka da gaggawa haka.." Se ya yi murmushi sannan yace
"Babu damuwa Abba.." Gyara zama Abba ya yi kafin ya ɗan sauke ajiyar zuciya ya soma faɗin
"Wato kiranka na yi na sanar da kai wata magana, wadda na san ba lallai ne ta maka daɗi ba. Sannan kuma na nemi afuwarka, na baka haƙuri duka dai a kan wannan maganar. Se dai ka san dama ance kana naka ne Allah na nasa. Duk kuma abin da ze faru dama can rubutacce ne. Wani kuma ba ya taɓa aurar matar da ba tasa ba." Abba ya ɗan dakata anan. Har ga Allah tunda Abba ya soma maganar nan ya ji jikinsa ya yi mugun sanyi, tsoro ya shige shi, fatansa da burinsa Abba ya ida faɗar abin da ya soma faɗa. Kamar ya san abin da Kaseem ɗin ke tunani se ya cigaba da faɗin
"Ka yi haƙuri Kaseem.. Na aurar da Afrah ga wani daban ba kai ba. Na aurar da ita saboda wani dalili me ƙarfi. Na kuma ji daɗi da maganarka da ita ba ta yi nisa ba, ma'ana ba ta kai wajen iyaye ba har wannan abu ya faru. Dan da ban san da wane ido zan kalleku ba. Se dai duk da haka kai kanka ina me daɗa baka haƙuri a kan abin da ya faru.. Ina fatan Allah ya musanya maka ita da wadda ta fita. Amma ka sani, na yaba da hankalinka sosai, na kuma so haɗa zuri'a da kai, se dai hakan be yi ba. Da kuma ina da wata yarinyar bayan Afrah da Afaaf, da wallahi zan baka aurenta ne. Dan kuwa itama Afaaf na aurar da ita.. Se dai bani da ita, hakan ne yasa nake maka fatan alkhairi da kuma fatan samun wadda ta fita.
"Ina ne nan?" Ya faɗa yana sake kallan ɗakin sosai. Kafin tace komai ya sake faɗin
"What brought me here? Asibiti?" Ya faɗa a mamakance.. Da sauri Mom ta girgiza kai tace
"I don't even know my Son.. But bari na kira Daddynka shi ya san dalilin kawoka nan ɗin.." Ta yi maganar tana ɗakko wayarta, ta shiga kiran Daddy. Se dai cikin rashin sa'a ake faɗa mata wayar ba zata shiga a lokacin ba.
... Gaba ɗaya se da Daddy ya miƙa musu hannu suka gaisa. Daga Abeey har Abba suna sake mamakin hali irin na Alhaji Matawallen.
"Barkanku da wannan lokaci.." Daddy ya faɗa..
"Barka dai.." Abeey da Abba suka haɗa baki wajen faɗar hakan. Bayan sun sake gaisawa sosai Daddy ya soma faɗin
"Toh wannan dai aure an yi shi ne ba tare da sanin kowanne ɓangare ba. Saboda haka na san iyaye mata kan iya yin taro duk ranar da yaran nan zasu tare. Saboda haka ina ganin mu saka ranar da ya kamata a ɗauki yaran nan a kaisu gidajensu. Ina ganin hakan shi ne mafita.." Jinjina kai dukansu suka yi cikin na'am da zancen Daddyn. Abeey ya ɗan yi gyaran murya sannan yace
"Toh se dai wani hanzari ba gudu ba.. Akwai abubuwa da ake irin na al'ada, wanda idan akace a cikin kwanaki kaɗan za a yi su Yallaɓai kamar ya yi kusa. Dan haka nake neman alfarmar bamu lokaci ko da kaɗan ne a fara kai kayan sannan a bamu matar.." Murmushi Abba ya yi yana kallan Abeey yace
"Ayyah.. Malam.. in dai dan wannan ne babu matsala.. Kowannensu ka iya yi wa matarsa duk abin da ya ga dama bayan zuwanta gidansa. Wannan ɗin tunda ba addini bane ina ganin kawai mu bar shi.."
"A'ah barinsu kam be taso ba. Gwara dai da kace idan sun je can ɗin se a musu.." Abeey ya katse Abba da faɗin hakan. Dukansu se suka yi murmushi daidai lokacin da Daddy yace
"Hakan ma ya yi.. Muma kuma ta ɓangaren mu bama buƙatar komai.. yarinya kawai muke buƙata.."
"A yi min wannan alfarmar Yallaɓai. Ko daga baya ne zan yi wa yarinyar nan kaya a aiko mata dasu.." Abba ya faɗa yana murmushi.
"Shi kenan.. Malam ka amince da hakan?" Daddy ya faɗa yana kallan Abeey
"Shi kenan.. Allah ya sanya alkhairi, ya haɗa kan yaran nan. Ya kuma kaɗe fitina.." Abeey ya amsa da hakan. Gyara zama Daddy ya yi kafin yace
"Toh Alhamdulillah.. Tunda dai an gama da kowacce matsala. Ina ganin kawai nan da sati ɗaya idan Allah ya kai mu kowaccensu ta tare a ɗakinta. Allah ya bada zaman lafiya.."
Toh Alhamdulillah. Bayan hutun en kwanaki da na ɗauka, yau ga ni na dawo. In Sha Allah zamu cigaba da fafatawa babu kama hannun yaro. 😍💃
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO24*
___"Toh madallah, Allah ya kaimu ya kuma sa ayi komai a sa'a, ya kaɗe fitina." Abeey ya faɗa. Abba da Daddy suka amsa da "Ameen."
... "Barka da wannan lokaci Abeey.." Gwani ya faɗa yana neman waje ya zauna. Murmushi Abeey ya yi kana ya amsa da
"Barka dai Affan.. Zauna sosai magana zamu yi.." Abeey ya yi maganar lokaci ɗaya yana kallansa. Gyara zaman ya yi shima yana murmushin. Abeey ya ɗan sauke ajiyar zuciya sannan yace
"Wato Affan kamar yanda na sanar da kai, zan ɗaura maka aure.. toh na cika. Na ɗaura maka aure kuma In Sha Allah ina fatan zaka karɓi matar hannu bibbiyu.." Shiru Gwani ya yi yana ɗan so ya tunano abin da ya sa Abeeyn ya ɗaura auren nasa haka kamar a gaggauce. Se dai kome ya yi hakan ba laifi bane. Dan haka ya yi shiru yana cigaba da saurarar abin da yake faɗa ɗin.
"Babban abin da ya min daɗi shi ne yadda mahaifin yarinyar da kansa ya nemi yana so ka auri ɗiyarsa. Kuma abin da ya sake min daɗi shi ne yanda yarinyar tasa ta kasance ɗalibarka." Tunda Abeeyn ya fara magana be ɗago ba se yanzun. Be san sanda ya furta
"Ɗalibata..?" Cike da tabbatarwa Abeey ya jinjina kai
"Ƙwarai kuwa ɗalibarka.. Er gidan Muhammadu Aji ce fa.." Ɗan shiru Gwani ya yi, se ya ji kamar yau ne ya fara jin sunan. Zuwa can kuma se ya tuna wane ne Muhammad Aji, su waye kuma 'ya'yansa. Kenan Afrah Abban nasu ya nemi ya aura? Har ma an ɗaura auren?
"Kaa ji sunan nata.. ɗan tuna min ya ɗan kwanta min.."
"Afrah...?" Ya faɗa cikin sigar tambaya da sauri yana kallan Abeey. Girgiza kai Abeey ya yi yace
"A'ah.. ina tunanin sunan er uwar tagwaitakarta ne wannan.." Cikin son sake tabbatar da abin da Abeeyn ke nufi. Da kuma son ya ƙaryata abin da yake hasashe yace
"Afaaf..?" Murmushi Abeey ya yi yace
"Ƙwarai kuwa Afaaf.." Runtse idanunsa Gwani ya yi yana jin yanda kansa ya ɗan juya masa. Be san ta yadda Abeey ze yi wani abu yace be masa ba. Amma wannan karon abin ya shammace shi. Afaaf fa? Ta yaya wannan yarinyar dake ganin tafi ƙarfin kowa zata zauna a matsayin matarsa? Bama wannan ba, ta yaya shi kansa ze iya zama da ita a matsayin matarsa? Wane alfahari ze yi idan an kira wannan da matarsa? Mutuniyar da bata ragawa kowa ba? Kallan kowa take a ƙasanta. Kallan kowa take a tafi ƙarfinsa. Yarinyar da tun zuwansa ajin basu taɓa shiri ba daidai da rana ɗaya kuwa? Yau ita ake kira da matarsa?
"Ya Salam.." ya faɗa cikin zuciyarsa yana dafe kansa, zuciyarsa na masa wani irin zafi.
"Affan.." Abeey ya faɗa yana kallansa. Da sauri ya ɗaga kai, yana ɗan wanzar da murmushi a kan fuskarsa yace
"Na'am Abeey.."
"Lafiya dai koh?"
"Ehh.. kaina ke ɗan sara min.." ya faɗa a nutse.
"Dama ba tun yanzu bane?" Abeey ya tambaya cike da kulawa.
"Yanzu ne. Amma babu damuwa Abeey, na ji wadda ka aura min.. Allah ya saka da alkhairi.."
"Ameen Ameen.. Ka daure ka sha magani, sannan ka kama kan naka. Allah ya ba da lafiya.. ya kuma saka albarka a rayuwar aurenku.. zuwa gobe se mu ƙarasa maganar kafin nan kan ya yi sauƙi."
"Ameen.." Gwani ya amsa da hakan yana ficewa daga ɗakin. Gaba ɗaya kansa ya kulle, ya ma rasa tunanin da ze yi. Ji yake kamar wani shirin film ne yake kalla, ko kuma wani abu da yafi kama da almara. Jin kansa na cigaba da sarawa lokaci ɗaya ransa na cigaba da ɓaci idan ya tuna wace ce Afaaf se ya nemi waje kawai ya kwanta, cike da fatan ya manta da komai a yanzun, ko ze samu bacci ya ɗauke shi. Ko kuma ma dai kawai ya ga ya farka daga wani baccin ya ga ashe duk mafarki yake yi. Idan kuwa gaske ne lallai ikon Allah ya wuce gaban wasa. Ko me kuma ya tsara ze faru, toh fa babu makawa se ya faru ɗin. A nutse ya ɗan lumshe kyawawan idanunsa har lokacin hannunsa na riƙe da kansa.
... Cikin matuƙar farin ciki yake driving, murmushi yaƙi barin fuskarsa. Tunda Abba ya kira shi a kan yana son ganinsa ya kasa sukuni, gaba ɗaya hankalinsa ya tafi can wajen Abban. Burinsa kawai ya isa ya ji dalilin kiran Abban. Duk da dai ya san kiran na da nasaba ne da maganar aurensa da Didi. Har ya isa gidan ya kasa dena zumuɗi. Aka yi masa jagora zuwa ɗakin baƙi, ya nemi waje ya zauna yana jiran zuwan Abban. Babu daɗewa kuwa se ga Abba ya shigo ɗakin da sallama. Yana ganinsa ya miƙe cike da girmamawa, se da Abban ya zauna sannan shima ya zauna bayan ya gaishe da shi cikin girmamawa.
"Amm Kaseem na san zaka yi mamakin kiran nan da na maka da gaggawa haka.." Se ya yi murmushi sannan yace
"Babu damuwa Abba.." Gyara zama Abba ya yi kafin ya ɗan sauke ajiyar zuciya ya soma faɗin
"Wato kiranka na yi na sanar da kai wata magana, wadda na san ba lallai ne ta maka daɗi ba. Sannan kuma na nemi afuwarka, na baka haƙuri duka dai a kan wannan maganar. Se dai ka san dama ance kana naka ne Allah na nasa. Duk kuma abin da ze faru dama can rubutacce ne. Wani kuma ba ya taɓa aurar matar da ba tasa ba." Abba ya ɗan dakata anan. Har ga Allah tunda Abba ya soma maganar nan ya ji jikinsa ya yi mugun sanyi, tsoro ya shige shi, fatansa da burinsa Abba ya ida faɗar abin da ya soma faɗa. Kamar ya san abin da Kaseem ɗin ke tunani se ya cigaba da faɗin
"Ka yi haƙuri Kaseem.. Na aurar da Afrah ga wani daban ba kai ba. Na aurar da ita saboda wani dalili me ƙarfi. Na kuma ji daɗi da maganarka da ita ba ta yi nisa ba, ma'ana ba ta kai wajen iyaye ba har wannan abu ya faru. Dan da ban san da wane ido zan kalleku ba. Se dai duk da haka kai kanka ina me daɗa baka haƙuri a kan abin da ya faru.. Ina fatan Allah ya musanya maka ita da wadda ta fita. Amma ka sani, na yaba da hankalinka sosai, na kuma so haɗa zuri'a da kai, se dai hakan be yi ba. Da kuma ina da wata yarinyar bayan Afrah da Afaaf, da wallahi zan baka aurenta ne. Dan kuwa itama Afaaf na aurar da ita.. Se dai bani da ita, hakan ne yasa nake maka fatan alkhairi da kuma fatan samun wadda ta fita.