Sashe 88
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
.. A kan dinning ɗin da ke sashen Daddy Mommah ta jere duk wani abu da ta girka musu. A nan suka haɗu bayan sun gaisa da Daddy suka soma karyawa. Duk sun yi tsammanin za su ga matayensu a wajen, se dai sam ba ma su ga ɓurɓushinsu ba. Mommah na lura da yanda suke ta jefa idanu da alama wani abun suke nema. Tabbas za ta yi amfani da wannan damar wajen koyawa Areef hankali bayan wahalar da su da ya yi tuntuni. Ta ɓangaren Gwani dai ta lura da wasu abubuwa, se dai duk da haka za ta haɗa duka ta san abin da za ta musu. Shi ya sa baccin Twins ɗin ma ya mata daɗi. Dan ba ta so su bar gidan nan ba tare da kowanne ɓangare yana son ɗaya ɓangaren ba. Ba kuma tare da ta gyarasu ba, dan jinsu take kamar 'ya'yanta.
"Ina 'ya'yan nawa ne?" Daddy ya faɗa yana kallan Mommah.
"Wallahi Yallaɓai bacci suke yi.. Shi ya sa na ce a barsu su yi ɗin duk sanda suka tashi se su yi nasu."
"Toh babu laifi.." Daddy ya faɗi hakan. Se kuma ya ɗora da faɗin
"Se ku shirya, dan kuwa gobe muna da baƙi da yawa cikin gidan nan.. Affan se ka yi haƙuri da mutanen da za su buƙaci ganinka." Murmushi Gwani ya yi be ce komai ba.
"Babu dai wata matsala koh?" Ya tambaya cike da kulawa.
"Daddy idan ma akwai ze faɗa min na faɗa maka.." Bad Man ya faɗa yana gyara zamansa.
"Iyeeee saboda kai ne bakinsa koh?" Daddy ya faɗa yana murmushi. Dukkansu murmushin suka yi. Kafin Daddy ya sake faɗin
"Kar ka ji komai, duk abin da kake buƙata ka sanar da ni ko mahaifiyarka.. Ba na son ka ji kunyar tambayarmu komai Uhmm?"
"In Sha Allah.." Gwani ya amsa da hakan yana murmushi.
... Tun kafin ta gama loda number sunan da ta yi saving number Ammi da shi ya fito. Ta kalla da mamaki tace
"Ikon Allah! Yallaɓai na ɗauka number wadda ta rako waɗancan mutanen ne koh?" Kallanta Daddy ya yi kafin ya amsa da
"Ehh ita ce.." Jin abin da Daddy ya faɗa ne ya sanyata kawai danna number ta kira. Babu daɗewa Ammi ta ɗaga. Suka gaisa kamar yanda suka saba, kafin can Mommah tace
"Wai da ma ke ce kika rako mutane cikin gidan nan jiya?" Murmushi Ammi ta yi dan ta san da ma Mommahn ba ta shaidata ba ne.
"Ƙwarai kuwa ni ce."
"Ikon Allah! Kin ga wallahi ban ganki ba. Hankalina duk ba ya wajen. Ki yi haƙuri."
"Haba babu komai.. Da ma ai ba za ki gane ni ba tun da ba sanin juna muka yi ba." Murmushi Mommah ta yi tana faɗin
"Haka ne.. Da ma na kira ne na miki godiya a kan hakan.. Allah Ya saka da alkhairi.. Amma da ma kin san su ne?" Ba tare da ta amsa addu'ar ba kawai ta share tace
"Eh toh.. Ba zan ce na sansu ba gaskiya.. Amma dai mun haɗu da su ne na je wajen Gwaggota. So a can muka haɗu, ita Maimunan ba ta da lafiya." Daga nan dai ta faɗa mata yanda suka haɗu har zuwansu Kano. Sosai Mommah ta sakewa Ammi godiya, dan ta ga ƙoƙarinta matuƙa. Ta san da wata ce ba za ta zauna ta jira har ta taimaka musu ba. Ba don Allah ya taimake su ya haɗa su da Ammin ba da tuni ba wannan maganar ake yi ba.
"Ki dena min godiya ke kam.." Ammi ta faɗa tana murmushi. Kamar ta katse wayar ba tare da ta tambayi Mommahn yanda ake ciki ba. Se dai tace
"Ya kuwa maganar ɗayan yaron..?" Murmushi Mommah ta yi cike da jin daɗin tambayar Ammin tace
"Cikin ikon Allah an same shi.. Yanzu haka ma yana tare da ɗan uwansa."
"Kai Alhamdulillah.. Allah abun godiya.. Alhamdulillah.." Ammi ta faɗa har cikin ranta tana jin daɗin hakan.
"In Sha Allah zuwa gobe zan shigo.."
"Allah Ya kai mu.." Mommah ta faɗa. Daga haka dai suka yi sallama.
"Se ka ce kun san juna." Murmushi Mommah ta yi tana ajje wayarta a gefe tace
"Mahaifiyarsu Afrah ce fa ashe.."
"Ahh haba?" Daddy ya faɗa yana kallanta.
"Wallahi kuwa.. Shi ya sa ka ga na yi mamaki da ka ce ita ce number."
"Ikon Allah.. Toh Allah Ya saka mata da alkhairi."
"Ameen.." Mommah ta amsa da hakan. A daren shi kansa Daddy ya shiga kiran duk wanda ya kamata ya sanar da shi wannan abun alkhairin da ya faru.
... Washe gari sosai gidan ya tashi da baƙi, kaama daga en uwa ne, abokan arziƙi da maƙota. Abokan Daddy kuwa ba a magana, dan kuwa ƙwansu da kwarkwatarsu har da waɗanda ba a garin suke ba duk sun zo. Masu uzuri ne kawai da waɗanda ba sa ƙasar su kaɗai ne ba su zo ba. Sosai gidan ya cigaba da karɓar baƙuncin mutane, hakan ne ya sa gidan ya zama kamar wanda ake biki. Kafin rana kuwa zance ya baza gari ya baza ko ina. Cewar bayan tsayin shekaru Allah Ya bayyana ɗan gidan Alhaji Matawalle da aka sace ranar da aka haife shi. Se dai a dukka abin da ake ta wallafawa har yanzu babu wanda ya san ga wanda ya aikata laifin. Dan kuwa Daddy ya bar abun ne be sanarwa da kowa cewa Mom ce ta aikata hakan ba. Tun da dai za a hukuntata ba se an tona mata asiri ba. Ragowar abin da ya rage ta je su haɗu da Ubangiji. Wajen azahar Ummeey da Abeey suka iso gidan. Tarba ta musamman aka musu, ba daga wajen abokan Daddy, en uwansa ba, har ma da matayen abokansa da su ma suke cikin gidan. A ranar dai Ummeey da Abeey sun ga karamci, kyaututtuka kuwa sun karɓesu babu adadi. Dan kuwa kowa ya tashi da abin da yake gwangwajesu da shi. Ita dai Ummeey har kuka ta yi saboda irin karamcin da aka nuna musu.
.. Daga inda yake zaune ya ɗan sauke ajiyar zuciya yana maida dubansa kan Bad Man yace
"Ka ce me?"
"Ba abin da na faɗa." Ya faɗa cikin basarwa. Murmushi Gwani ya yi dan ya fahimce shi, ya ɗauka yana sane ya share shi. Se dai sam ba haka ba ne, be ji shi ba ne, saboda tunanin da ya faɗa. Miƙewa ya yi, har ya soma takawa sannan ya kalli Bad yace
"Ba za ka je ba ne?"
"Ina?" Ya faɗa yana kallansa a kaikaice.
"Masallaci.."
"Eh zan yi a gida." Ya faɗa yana maida dubansa kan waya.
"Ba ka isa ba kuma.. Malam ka tashi mu wuce."
"Ban san hanya ba ne?" Ya faɗa yana watsa masa harara. Fahimtar dalilin Bad Man ɗin na fusata ya sanya shi faɗin
"Yi haƙuri ɗan uwa.. Tashi mu je." Ƙwafa Bad Man ya ja yana Murmushi lokaci ɗaya yana furta
"Hmmm.." Daga haka ya sauko daga kan gadon. Binsa da kallo Gwani ya yi, shi dai burinsa a yi masa laifi a ba shi haƙuri. Ya girgiza kai lokacin da suka fara tafiya dan ficewa daga ɗakin. Tare suka jera suna tafiya, cikin shigar da za a iya cewa kusan iri ɗaya. Se ya kasance sun fito sakk a en biyunsu. Tun daga nesa ya hango Kaseem ɗin da ganinsu ya sanya shi nufowa inda suke. Ya tamke fuskar nan tuna abin da ya faru. Ya ɗauke kai kamar be gan shi ba. Dab da za su wuce shi Kaseem yace
"Hello brothers.." Dakatawa Gwani ya yi, kamar Bad Man ba ze dakata ba se kuma ya tsaya. Hannu Kaseem ya soma miƙawa Bad Man. Se da ya ɗaga ido ya kalli Kaseem ɗin kamar me son gano wani abu kafin a hankali ya miƙa masa hannun suka gaisa. Kaseem ya sakar masa murmushi kamar babu wani abu da ya taɓa faruwa tsakaninsu yace
"Congratulations bro.."
"Thanks." Ya faɗa a gajarce. Se ya maida dubansa kan Gwani, shi ma murmushin ya sakar masa kafin ya miƙa masa hannu suka gaisa yace
"Ina maka barka da dawowa gida."
"Ina godiya." Gwani ya faɗa yana maida masa da martanin murmushin. Se ya saki hannun Gwani sannan ya koma inda Bad yake yace
"Pls ka manta da abin da ya faru.. In Sha Allah komai ya wuce.. Ka yi haƙuri da halayena a lokacin." Shiru Bad Man ya yi na tsawon sakanni kafin ya sauke numfashi yace
"Ba damuwa.."
"Na gode.." Daga haka suka jera zuwa masallacin tare.
... Sanye cikin wata atamfa me kyau da wadataccen mayafi Ammi ta fito daga ɗakin. Abba da ke zaune a kan kujera da wani littafi a hannunsa yana dubawa ya ɗaga kai ya kalleta.
"Ma Sha Allah! Sosai kika fito kika yi kyau abinki.." Ya ƙare yana murmushi. Dariya Ammi ta yi jin a yanda Abban ya yi maganar, tace tana neman waje ta zauna
"Toh ina godiya sosai Abbansu."
"Madallah. Kin ida shirin ne?" Se ta jinjina kai tana amsawa da "Ehh." Kafin Abba yace komai aka yi sallama cikin ɗakin. Dukkansu suka amsa sallamar suna kallan masu yinta. Ƙarasowa Mami da Jadwa suka yi, Mami ta nemi waje ta zauna kan kujera, lura da Jadwa da ke neman zama a kan kujera ya sanyata taɓota tana watsa mata harara. Ta haɗe fuska tana ji kamar ta maaze ta yi zamanta. Se dai ta nemi waje ta zauna a ƙasan.
"Barka da wannan lokacin Abban Twins."
"Barka dai Sadiya.. Ke ce a gidan?"
"Ehh wallahi.." Ta faɗa tana murmushi. Se ta maida dubanta kan Ammi suka gaisa sama sama.
"Abba ina wuni?" Jadwa ta faɗa.
"Lafiya ƙalau Jadwa, kuna lafiya?"
"Ehh.." ta amsa da hakan. Shiru wajen ya ɗauka na tsawon lokaci ba wanda ya sake cewa komai. Zuwa can dai Ammi ta miƙe tace
"Bari na wuce Abbansu.. Kar dare ya min."
"Toh madallah.. Allah Ya tsare. Kya musu fatan alkhairi kafin na zo."
"Ina 'ya'yan nawa ne?" Daddy ya faɗa yana kallan Mommah.
"Wallahi Yallaɓai bacci suke yi.. Shi ya sa na ce a barsu su yi ɗin duk sanda suka tashi se su yi nasu."
"Toh babu laifi.." Daddy ya faɗi hakan. Se kuma ya ɗora da faɗin
"Se ku shirya, dan kuwa gobe muna da baƙi da yawa cikin gidan nan.. Affan se ka yi haƙuri da mutanen da za su buƙaci ganinka." Murmushi Gwani ya yi be ce komai ba.
"Babu dai wata matsala koh?" Ya tambaya cike da kulawa.
"Daddy idan ma akwai ze faɗa min na faɗa maka.." Bad Man ya faɗa yana gyara zamansa.
"Iyeeee saboda kai ne bakinsa koh?" Daddy ya faɗa yana murmushi. Dukkansu murmushin suka yi. Kafin Daddy ya sake faɗin
"Kar ka ji komai, duk abin da kake buƙata ka sanar da ni ko mahaifiyarka.. Ba na son ka ji kunyar tambayarmu komai Uhmm?"
"In Sha Allah.." Gwani ya amsa da hakan yana murmushi.
... Tun kafin ta gama loda number sunan da ta yi saving number Ammi da shi ya fito. Ta kalla da mamaki tace
"Ikon Allah! Yallaɓai na ɗauka number wadda ta rako waɗancan mutanen ne koh?" Kallanta Daddy ya yi kafin ya amsa da
"Ehh ita ce.." Jin abin da Daddy ya faɗa ne ya sanyata kawai danna number ta kira. Babu daɗewa Ammi ta ɗaga. Suka gaisa kamar yanda suka saba, kafin can Mommah tace
"Wai da ma ke ce kika rako mutane cikin gidan nan jiya?" Murmushi Ammi ta yi dan ta san da ma Mommahn ba ta shaidata ba ne.
"Ƙwarai kuwa ni ce."
"Ikon Allah! Kin ga wallahi ban ganki ba. Hankalina duk ba ya wajen. Ki yi haƙuri."
"Haba babu komai.. Da ma ai ba za ki gane ni ba tun da ba sanin juna muka yi ba." Murmushi Mommah ta yi tana faɗin
"Haka ne.. Da ma na kira ne na miki godiya a kan hakan.. Allah Ya saka da alkhairi.. Amma da ma kin san su ne?" Ba tare da ta amsa addu'ar ba kawai ta share tace
"Eh toh.. Ba zan ce na sansu ba gaskiya.. Amma dai mun haɗu da su ne na je wajen Gwaggota. So a can muka haɗu, ita Maimunan ba ta da lafiya." Daga nan dai ta faɗa mata yanda suka haɗu har zuwansu Kano. Sosai Mommah ta sakewa Ammi godiya, dan ta ga ƙoƙarinta matuƙa. Ta san da wata ce ba za ta zauna ta jira har ta taimaka musu ba. Ba don Allah ya taimake su ya haɗa su da Ammin ba da tuni ba wannan maganar ake yi ba.
"Ki dena min godiya ke kam.." Ammi ta faɗa tana murmushi. Kamar ta katse wayar ba tare da ta tambayi Mommahn yanda ake ciki ba. Se dai tace
"Ya kuwa maganar ɗayan yaron..?" Murmushi Mommah ta yi cike da jin daɗin tambayar Ammin tace
"Cikin ikon Allah an same shi.. Yanzu haka ma yana tare da ɗan uwansa."
"Kai Alhamdulillah.. Allah abun godiya.. Alhamdulillah.." Ammi ta faɗa har cikin ranta tana jin daɗin hakan.
"In Sha Allah zuwa gobe zan shigo.."
"Allah Ya kai mu.." Mommah ta faɗa. Daga haka dai suka yi sallama.
"Se ka ce kun san juna." Murmushi Mommah ta yi tana ajje wayarta a gefe tace
"Mahaifiyarsu Afrah ce fa ashe.."
"Ahh haba?" Daddy ya faɗa yana kallanta.
"Wallahi kuwa.. Shi ya sa ka ga na yi mamaki da ka ce ita ce number."
"Ikon Allah.. Toh Allah Ya saka mata da alkhairi."
"Ameen.." Mommah ta amsa da hakan. A daren shi kansa Daddy ya shiga kiran duk wanda ya kamata ya sanar da shi wannan abun alkhairin da ya faru.
... Washe gari sosai gidan ya tashi da baƙi, kaama daga en uwa ne, abokan arziƙi da maƙota. Abokan Daddy kuwa ba a magana, dan kuwa ƙwansu da kwarkwatarsu har da waɗanda ba a garin suke ba duk sun zo. Masu uzuri ne kawai da waɗanda ba sa ƙasar su kaɗai ne ba su zo ba. Sosai gidan ya cigaba da karɓar baƙuncin mutane, hakan ne ya sa gidan ya zama kamar wanda ake biki. Kafin rana kuwa zance ya baza gari ya baza ko ina. Cewar bayan tsayin shekaru Allah Ya bayyana ɗan gidan Alhaji Matawalle da aka sace ranar da aka haife shi. Se dai a dukka abin da ake ta wallafawa har yanzu babu wanda ya san ga wanda ya aikata laifin. Dan kuwa Daddy ya bar abun ne be sanarwa da kowa cewa Mom ce ta aikata hakan ba. Tun da dai za a hukuntata ba se an tona mata asiri ba. Ragowar abin da ya rage ta je su haɗu da Ubangiji. Wajen azahar Ummeey da Abeey suka iso gidan. Tarba ta musamman aka musu, ba daga wajen abokan Daddy, en uwansa ba, har ma da matayen abokansa da su ma suke cikin gidan. A ranar dai Ummeey da Abeey sun ga karamci, kyaututtuka kuwa sun karɓesu babu adadi. Dan kuwa kowa ya tashi da abin da yake gwangwajesu da shi. Ita dai Ummeey har kuka ta yi saboda irin karamcin da aka nuna musu.
.. Daga inda yake zaune ya ɗan sauke ajiyar zuciya yana maida dubansa kan Bad Man yace
"Ka ce me?"
"Ba abin da na faɗa." Ya faɗa cikin basarwa. Murmushi Gwani ya yi dan ya fahimce shi, ya ɗauka yana sane ya share shi. Se dai sam ba haka ba ne, be ji shi ba ne, saboda tunanin da ya faɗa. Miƙewa ya yi, har ya soma takawa sannan ya kalli Bad yace
"Ba za ka je ba ne?"
"Ina?" Ya faɗa yana kallansa a kaikaice.
"Masallaci.."
"Eh zan yi a gida." Ya faɗa yana maida dubansa kan waya.
"Ba ka isa ba kuma.. Malam ka tashi mu wuce."
"Ban san hanya ba ne?" Ya faɗa yana watsa masa harara. Fahimtar dalilin Bad Man ɗin na fusata ya sanya shi faɗin
"Yi haƙuri ɗan uwa.. Tashi mu je." Ƙwafa Bad Man ya ja yana Murmushi lokaci ɗaya yana furta
"Hmmm.." Daga haka ya sauko daga kan gadon. Binsa da kallo Gwani ya yi, shi dai burinsa a yi masa laifi a ba shi haƙuri. Ya girgiza kai lokacin da suka fara tafiya dan ficewa daga ɗakin. Tare suka jera suna tafiya, cikin shigar da za a iya cewa kusan iri ɗaya. Se ya kasance sun fito sakk a en biyunsu. Tun daga nesa ya hango Kaseem ɗin da ganinsu ya sanya shi nufowa inda suke. Ya tamke fuskar nan tuna abin da ya faru. Ya ɗauke kai kamar be gan shi ba. Dab da za su wuce shi Kaseem yace
"Hello brothers.." Dakatawa Gwani ya yi, kamar Bad Man ba ze dakata ba se kuma ya tsaya. Hannu Kaseem ya soma miƙawa Bad Man. Se da ya ɗaga ido ya kalli Kaseem ɗin kamar me son gano wani abu kafin a hankali ya miƙa masa hannun suka gaisa. Kaseem ya sakar masa murmushi kamar babu wani abu da ya taɓa faruwa tsakaninsu yace
"Congratulations bro.."
"Thanks." Ya faɗa a gajarce. Se ya maida dubansa kan Gwani, shi ma murmushin ya sakar masa kafin ya miƙa masa hannu suka gaisa yace
"Ina maka barka da dawowa gida."
"Ina godiya." Gwani ya faɗa yana maida masa da martanin murmushin. Se ya saki hannun Gwani sannan ya koma inda Bad yake yace
"Pls ka manta da abin da ya faru.. In Sha Allah komai ya wuce.. Ka yi haƙuri da halayena a lokacin." Shiru Bad Man ya yi na tsawon sakanni kafin ya sauke numfashi yace
"Ba damuwa.."
"Na gode.." Daga haka suka jera zuwa masallacin tare.
... Sanye cikin wata atamfa me kyau da wadataccen mayafi Ammi ta fito daga ɗakin. Abba da ke zaune a kan kujera da wani littafi a hannunsa yana dubawa ya ɗaga kai ya kalleta.
"Ma Sha Allah! Sosai kika fito kika yi kyau abinki.." Ya ƙare yana murmushi. Dariya Ammi ta yi jin a yanda Abban ya yi maganar, tace tana neman waje ta zauna
"Toh ina godiya sosai Abbansu."
"Madallah. Kin ida shirin ne?" Se ta jinjina kai tana amsawa da "Ehh." Kafin Abba yace komai aka yi sallama cikin ɗakin. Dukkansu suka amsa sallamar suna kallan masu yinta. Ƙarasowa Mami da Jadwa suka yi, Mami ta nemi waje ta zauna kan kujera, lura da Jadwa da ke neman zama a kan kujera ya sanyata taɓota tana watsa mata harara. Ta haɗe fuska tana ji kamar ta maaze ta yi zamanta. Se dai ta nemi waje ta zauna a ƙasan.
"Barka da wannan lokacin Abban Twins."
"Barka dai Sadiya.. Ke ce a gidan?"
"Ehh wallahi.." Ta faɗa tana murmushi. Se ta maida dubanta kan Ammi suka gaisa sama sama.
"Abba ina wuni?" Jadwa ta faɗa.
"Lafiya ƙalau Jadwa, kuna lafiya?"
"Ehh.." ta amsa da hakan. Shiru wajen ya ɗauka na tsawon lokaci ba wanda ya sake cewa komai. Zuwa can dai Ammi ta miƙe tace
"Bari na wuce Abbansu.. Kar dare ya min."
"Toh madallah.. Allah Ya tsare. Kya musu fatan alkhairi kafin na zo."