Sashe 24
A Jini Take Izzata Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
"Ko ina ruwan mutum da ciwona.. Na tsani shishshigi.. Mutum se nuna shi wani ne yake yi bayan ba haka ɗin ba ne.." ta yi maganar duka a lokaci ɗaya .
Harɗe hannayensa Gwani ya yi a ƙirjinsa yana kallan Abbati fuskarsa a haɗe. Se da jikinsa ya yi sanyi a ransa yana tunanin ko ya kama shi ne yana kallan yarinyar can? Kuma ko dai ita ce matar tasa? Se da ya sosa ƙeyarsa sannan ya ƙaraso inda Gwani yake yace
"Afuwa Gwani.. A yi min aikin gafara.. Wallahi na kalleta ne dan tabbatar da wani abu da nake zargi.." Sam be yi niyyar saurarar abin da Abbatin ke faɗa ba, se dai jin abin da ya ambata daga ƙarshe ya sanya shi kallansa har lokacin be saki fuskarsa ba
"Zargi?" Ya faɗa cike da mamaki. Jinjina kai Abbati ya yi yace
"Ƙwarai kuwa.. Amma ka yi min haƙuri don Allah.. maganar a kan matarka ne.." ya faɗa ba dan yana da tabbacin hakan ba, se dan gane gaskiyar hakan. Kamar Gwani ba ze ce komai ba, se dai kuma ya ji yana son jin maganar, amma kuma maganganu irin wannan ɗin ba kasafai suka saba haɗa shi da Abbatin ba. Kallan inda Lulu take Gwani ya yi, kafin ya dawo da dubansa kan Abbati yace
"Me kake so ka ce?" Gyara tsayuwa ya yi, yana tunanin ta inda ze fara. Abubuwa kala kala ke tare da shi, se kuma ya fahimci dalilin tsayar da shi da aka yi aka ba shi wani saƙo, ashe duk dan ya yi amfani da su ne wajen ganar da Gwani gaskiyar al'amari. Be so hakan ta kasance a kan Gwani ɗin ba, mutum me matuƙar kirki da sanin ya kamata. Se dai kuma koma mene ne ba ze iya zuba ido a cuci Gwanin yana kallo ba tare da ya taɓuka wani abun ba..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO36*
___ "Amma na ga kamar sauri kake yi.. Idan babu damuwa zan jiraka ku je ku dawo.." Abbati ya faɗa. Sauke numfashi kaɗan Gwani ya yi kafin yace
"Shi kenan.."
"Dama zamu yi magana da Malam, kafin ka dawo mun gama.." Abbati ya faɗa ba dan ya so hakan ba, se dan ba ya so ya yi maganar kuma a gaban Lulun. Ko babu komai ba ze so ta dinga masa kallan wanda ya tona mata asiri ba. Duk da ma shi be yi hakan da nufin tozar tata ba, kawai dai ze yi hakan ne saboda mutuncin dake tsakaninsa da Gwani. Dan idan ya yi shiru ba tare da ya faɗawa Gwani ba, bayan sanin ainahin wace ce Lulun kamar be kyauta masa ba. Yin gaba ya yi, har ya zo ya wuce su Lulu, ta yi kamar ba ta gan shi ba, se da Little yace mata
"Lulu ya tafi fa.."
"Ina ruwanka toh? Ya daɗe be tafi ɗin ba mana.."
"Kaiii!!" Ya faɗa kamar wani babba yana kallanta. Ɗauke kai ta yi tana harara sannan ta kama hannunsa suka soma tafiya. Wani ƙaramin asibiti dake bakin titinsu suka nufa wanda za a iya kiransa da chemist, se dai saboda faɗaɗashin da mamallakinsa ya yi ne ya sanya ya zama clinic.
"Matarka ce?" Shi ne abin da Likitan ya faɗa yana kallan Gwani sanda ta faɗa masa abin da ke damunta kamar za ta kai masa duka shi ma, saboda yanda take ta ciccin magani. Dama tunda suka taho Gwanin kansa ransa ba ya jinsa da daɗi ballantana har ya biye mata, hakan ne ya sa daga ita har shi ɗin fuskarsu babu annuri. Se dai fuskar Gwani kana kalla za ka gane a haka yanayinsa yake, yayin da oganniyar kuwa haushi da takaici su ne suka sanyata tsuke kyakkyawar fuskarta waje ɗaya.
"Cikinta ke ciwo, saboda abincin da ba ta son ci. Ya ɗan kumbura kuma.. Ina fatan yanzu ka fahimci abin da ke damunta?" Gwani ya faɗa dan ya ga yana nema ya yi wa ciwon nata wata fassara, saboda yanda ta yi bayanin a cunkushe. Sake haɗe face ta yi ita a lallai dole wata boss ce, wadda ba ta son raini. Ta saci kallansa ta maka wasa wata harara cike da haushinsa, da takaicin yanda ya kallan mata ciki saboda iskanci. Murmushi Likitan ya yi yana faɗin
"Ohk.." Basu daɗe cikin asibitin ba suka baro shi, bayan ya siya magangunan da aka rubuta mata, sannan suka dawo gida. Ita dai kawai daurewa take yi, ji take kamar ta tari adaidaita ta koma gidansu. Se dai idan ta koma ɗin bata san me za tace musu ba, hakan ne ya sa ta ɗan runtse idanunta ta buɗe daidai lokacin da ta shige cikin gidan hannunta na riƙe da na Little dake ɗauke da ledar magangunan.
A ƙofar gidan ya samu Abbati, zuwa lokacin har sun gama magana da Abeey, jiran Gwani kawai yake yi. Da mamaki Gwani ya ƙarasa wajen nasa yana faɗin
"Ashe kana nan?"
"Wallahi kuwa.. Kun dawo kenan? Sannunku da dawowa.." ya yi maganar duka a lokaci ɗaya.
"Yawwah.." Gwani ya faɗa. Gyara tsayuwarsa Abbati ya yi kafin ya soma faɗin
"Ban san ta yaya zan fara maka magana ba Gwani.. Ba munafunci zan maka ba, ba kuma so nake na tozarta wani ba. A'ah na ga hakan yana da kyau ka sani ne, saboda takanas aka zo aka faɗa min wata magana da ta hana ni sukuni a kan matar da ka aura." Cikin matuƙar mamaki Gwani yace
"Matata?" Ya tambaya a makakance.
"Ehh.." Cikin ƙankanin lokaci ya shiga zayyane masa yanda suka yi da mutanen nan ɗazu, sannan ya ƙare da fito da madaidaiciyar wayarsa ya shiga kamo hoton lokaci ɗaya yana faɗin
"Idan kuma har ban yi kuskure ba, toh wallahi yarinyar nan ita na gani ranar nan za ta shiga gidan nan da mutane ke kuka da shi, har na maka ƙorafi a kan yara ƙanana dake shiga gidan, toh ashe ma wannan ɗin ce. Na shaida na kuma tabbatar da hakan ne saboda a ranar ma tana tare da yaron nan.. Sannan kuma na sake gasgata hakan ne sanadiyyar wannan hoton da aka nuna min.." ya ƙare yana miƙawa Gwani wayar. Tunda ya soma maganar Gwani ke rarrabe kowacce kalma da ya faɗa yana haɗata da ma'anarta, saboda ya fi fahimtar abin da ya faɗa ɗin. Se dai zuwa lokacin da ya gama maganarsa ya kuma miƙo masa wayar hannunsa, se kawai ya ji wani bugun zuciya. Haka kawai ya ji kamar tsoro na shigarsa, har ya ji tamkar ma ka da ya duba wayar. Se dai kawai ya karɓa ɗin ya ɗora idanunsa da suka ɗan sauya tun lokacin da Abbati ya fara faɗa masa wace ce Lulu kamar yanda aka faɗa masa. A take, a kuma lokaci ƙanƙanci idanunsa suka sauka a kan hoton, kamar yanda aka faɗa ɗin hakan ne kuwa, Lulun ce tsaye wani ya rungumeta, wani wanda ba a iya ganin fuskarsa se tata, saboda daga ɓangarenta aka ɗauki hoton. Ɗan runtse idanunsa ya yi cikin rashin sanin abin yi. Bayan wajen second 30 ya buɗe idanun nasa lokacin da suka yi ja kamar ba na shi ba, se dai ba a kan hoton ba, dan ba ya tunanin ze iya cigaba da kallan hoton, ko da kuwa ba maganar wadda take a matsayin matarsa ake yi ba, ballantana kuma wadda ke a matsayin matar tasa. Cikin matuƙar dakiya yace
"Ban da kai se wa ya ga hoton?" Ya tambaya a sautin muryarsa kaɗai za ka fahimci yanda abin ya yi masa ɗaci.
"Ni kaɗai aka nunawa, ni ma ɗin wai dan ya je wajenka ne.." Fito da wayarsa Gwani ya yi, ya yi danne_danne a ciki. Bayan wajen minti 1 ya miƙawa Abbati wayar sannan yace
"Ba na son sake jin maganar a wani wajen. Zan yi maka magana duk lokacin da na gama bincike.." Daga haka kawai ya wuce cikin gidan saboda yanda yake jin wani irin zafi cikin ransa, ba kuma ya tunanin ze sake tsayawa su yi wata maganar bayan wannan. Binsa da kallo Abbati ya yi cike da tausayawa, se kuma ya girgiza kai yana faɗin
Harɗe hannayensa Gwani ya yi a ƙirjinsa yana kallan Abbati fuskarsa a haɗe. Se da jikinsa ya yi sanyi a ransa yana tunanin ko ya kama shi ne yana kallan yarinyar can? Kuma ko dai ita ce matar tasa? Se da ya sosa ƙeyarsa sannan ya ƙaraso inda Gwani yake yace
"Afuwa Gwani.. A yi min aikin gafara.. Wallahi na kalleta ne dan tabbatar da wani abu da nake zargi.." Sam be yi niyyar saurarar abin da Abbatin ke faɗa ba, se dai jin abin da ya ambata daga ƙarshe ya sanya shi kallansa har lokacin be saki fuskarsa ba
"Zargi?" Ya faɗa cike da mamaki. Jinjina kai Abbati ya yi yace
"Ƙwarai kuwa.. Amma ka yi min haƙuri don Allah.. maganar a kan matarka ne.." ya faɗa ba dan yana da tabbacin hakan ba, se dan gane gaskiyar hakan. Kamar Gwani ba ze ce komai ba, se dai kuma ya ji yana son jin maganar, amma kuma maganganu irin wannan ɗin ba kasafai suka saba haɗa shi da Abbatin ba. Kallan inda Lulu take Gwani ya yi, kafin ya dawo da dubansa kan Abbati yace
"Me kake so ka ce?" Gyara tsayuwa ya yi, yana tunanin ta inda ze fara. Abubuwa kala kala ke tare da shi, se kuma ya fahimci dalilin tsayar da shi da aka yi aka ba shi wani saƙo, ashe duk dan ya yi amfani da su ne wajen ganar da Gwani gaskiyar al'amari. Be so hakan ta kasance a kan Gwani ɗin ba, mutum me matuƙar kirki da sanin ya kamata. Se dai kuma koma mene ne ba ze iya zuba ido a cuci Gwanin yana kallo ba tare da ya taɓuka wani abun ba..
✨MHIZ INNOCENT✨
*AJTICHAPTERTWO36*
___ "Amma na ga kamar sauri kake yi.. Idan babu damuwa zan jiraka ku je ku dawo.." Abbati ya faɗa. Sauke numfashi kaɗan Gwani ya yi kafin yace
"Shi kenan.."
"Dama zamu yi magana da Malam, kafin ka dawo mun gama.." Abbati ya faɗa ba dan ya so hakan ba, se dan ba ya so ya yi maganar kuma a gaban Lulun. Ko babu komai ba ze so ta dinga masa kallan wanda ya tona mata asiri ba. Duk da ma shi be yi hakan da nufin tozar tata ba, kawai dai ze yi hakan ne saboda mutuncin dake tsakaninsa da Gwani. Dan idan ya yi shiru ba tare da ya faɗawa Gwani ba, bayan sanin ainahin wace ce Lulun kamar be kyauta masa ba. Yin gaba ya yi, har ya zo ya wuce su Lulu, ta yi kamar ba ta gan shi ba, se da Little yace mata
"Lulu ya tafi fa.."
"Ina ruwanka toh? Ya daɗe be tafi ɗin ba mana.."
"Kaiii!!" Ya faɗa kamar wani babba yana kallanta. Ɗauke kai ta yi tana harara sannan ta kama hannunsa suka soma tafiya. Wani ƙaramin asibiti dake bakin titinsu suka nufa wanda za a iya kiransa da chemist, se dai saboda faɗaɗashin da mamallakinsa ya yi ne ya sanya ya zama clinic.
"Matarka ce?" Shi ne abin da Likitan ya faɗa yana kallan Gwani sanda ta faɗa masa abin da ke damunta kamar za ta kai masa duka shi ma, saboda yanda take ta ciccin magani. Dama tunda suka taho Gwanin kansa ransa ba ya jinsa da daɗi ballantana har ya biye mata, hakan ne ya sa daga ita har shi ɗin fuskarsu babu annuri. Se dai fuskar Gwani kana kalla za ka gane a haka yanayinsa yake, yayin da oganniyar kuwa haushi da takaici su ne suka sanyata tsuke kyakkyawar fuskarta waje ɗaya.
"Cikinta ke ciwo, saboda abincin da ba ta son ci. Ya ɗan kumbura kuma.. Ina fatan yanzu ka fahimci abin da ke damunta?" Gwani ya faɗa dan ya ga yana nema ya yi wa ciwon nata wata fassara, saboda yanda ta yi bayanin a cunkushe. Sake haɗe face ta yi ita a lallai dole wata boss ce, wadda ba ta son raini. Ta saci kallansa ta maka wasa wata harara cike da haushinsa, da takaicin yanda ya kallan mata ciki saboda iskanci. Murmushi Likitan ya yi yana faɗin
"Ohk.." Basu daɗe cikin asibitin ba suka baro shi, bayan ya siya magangunan da aka rubuta mata, sannan suka dawo gida. Ita dai kawai daurewa take yi, ji take kamar ta tari adaidaita ta koma gidansu. Se dai idan ta koma ɗin bata san me za tace musu ba, hakan ne ya sa ta ɗan runtse idanunta ta buɗe daidai lokacin da ta shige cikin gidan hannunta na riƙe da na Little dake ɗauke da ledar magangunan.
A ƙofar gidan ya samu Abbati, zuwa lokacin har sun gama magana da Abeey, jiran Gwani kawai yake yi. Da mamaki Gwani ya ƙarasa wajen nasa yana faɗin
"Ashe kana nan?"
"Wallahi kuwa.. Kun dawo kenan? Sannunku da dawowa.." ya yi maganar duka a lokaci ɗaya.
"Yawwah.." Gwani ya faɗa. Gyara tsayuwarsa Abbati ya yi kafin ya soma faɗin
"Ban san ta yaya zan fara maka magana ba Gwani.. Ba munafunci zan maka ba, ba kuma so nake na tozarta wani ba. A'ah na ga hakan yana da kyau ka sani ne, saboda takanas aka zo aka faɗa min wata magana da ta hana ni sukuni a kan matar da ka aura." Cikin matuƙar mamaki Gwani yace
"Matata?" Ya tambaya a makakance.
"Ehh.." Cikin ƙankanin lokaci ya shiga zayyane masa yanda suka yi da mutanen nan ɗazu, sannan ya ƙare da fito da madaidaiciyar wayarsa ya shiga kamo hoton lokaci ɗaya yana faɗin
"Idan kuma har ban yi kuskure ba, toh wallahi yarinyar nan ita na gani ranar nan za ta shiga gidan nan da mutane ke kuka da shi, har na maka ƙorafi a kan yara ƙanana dake shiga gidan, toh ashe ma wannan ɗin ce. Na shaida na kuma tabbatar da hakan ne saboda a ranar ma tana tare da yaron nan.. Sannan kuma na sake gasgata hakan ne sanadiyyar wannan hoton da aka nuna min.." ya ƙare yana miƙawa Gwani wayar. Tunda ya soma maganar Gwani ke rarrabe kowacce kalma da ya faɗa yana haɗata da ma'anarta, saboda ya fi fahimtar abin da ya faɗa ɗin. Se dai zuwa lokacin da ya gama maganarsa ya kuma miƙo masa wayar hannunsa, se kawai ya ji wani bugun zuciya. Haka kawai ya ji kamar tsoro na shigarsa, har ya ji tamkar ma ka da ya duba wayar. Se dai kawai ya karɓa ɗin ya ɗora idanunsa da suka ɗan sauya tun lokacin da Abbati ya fara faɗa masa wace ce Lulu kamar yanda aka faɗa masa. A take, a kuma lokaci ƙanƙanci idanunsa suka sauka a kan hoton, kamar yanda aka faɗa ɗin hakan ne kuwa, Lulun ce tsaye wani ya rungumeta, wani wanda ba a iya ganin fuskarsa se tata, saboda daga ɓangarenta aka ɗauki hoton. Ɗan runtse idanunsa ya yi cikin rashin sanin abin yi. Bayan wajen second 30 ya buɗe idanun nasa lokacin da suka yi ja kamar ba na shi ba, se dai ba a kan hoton ba, dan ba ya tunanin ze iya cigaba da kallan hoton, ko da kuwa ba maganar wadda take a matsayin matarsa ake yi ba, ballantana kuma wadda ke a matsayin matar tasa. Cikin matuƙar dakiya yace
"Ban da kai se wa ya ga hoton?" Ya tambaya a sautin muryarsa kaɗai za ka fahimci yanda abin ya yi masa ɗaci.
"Ni kaɗai aka nunawa, ni ma ɗin wai dan ya je wajenka ne.." Fito da wayarsa Gwani ya yi, ya yi danne_danne a ciki. Bayan wajen minti 1 ya miƙawa Abbati wayar sannan yace
"Ba na son sake jin maganar a wani wajen. Zan yi maka magana duk lokacin da na gama bincike.." Daga haka kawai ya wuce cikin gidan saboda yanda yake jin wani irin zafi cikin ransa, ba kuma ya tunanin ze sake tsayawa su yi wata maganar bayan wannan. Binsa da kallo Abbati ya yi cike da tausayawa, se kuma ya girgiza kai yana faɗin